Showing 147001 words to 150000 words out of 232912 words

Chapter 50 - Matar Haidar Hausa Novels By Maryam S Indabawa.txt

29 Oct 2025

1293

kyau."

Ya zuba mata ido ita kuwa kan ta a kasa ta kasa duban shi, numfashi ya ja sannan yace
"Maryam!"
Wani iri taji dan sai da tsigar jikin ta ta tashi, ta dago ta kalle shi da sauri ta dauke kanta, dan bata iya jurar kallon idon sa, wani abu take gani yana fitowa yana shiga nata wanda hakan ke haifar mata da mutuwar jiki, shiru yai kamar ba zai magana ba sai kuma yace
"Bayan tafiya ta kin shiga wani mawuyacin hali wanda ni kaina da bana nan na shiga makamancin sa, a dalilin rashin daukar shawara ta abin yaso ya taba miki rayuwar ki, in nine ke ba ruwa na da wani samari karatu na zan rika a gaba zaki samu masu son ki wanda kema a lokacin kin kama kasa amman a yanzu karatun shine ya dace da ki sa a gaba, kina zaune wani yazo zai tarwarsa miki rayuwa akan me? Me sonki na gaskiya ba zai taba barin ki ba ko tuhumar wani abu akan ki, yana da kyau ki nutsu ki gane mai sonki, da wanda kike so."

Hannun ta ya kamo wani iri taji waninshock wand ashima sai da yaji tsargawar sa, dan murazawa yayi sannan ya saki yace
"Dan Allah ba danni ba ki bar harkar wasu samari ki riki karatun ki, ki taimakawa Haidar, a gaba zaki samu mai son ki wanda baki taba tsammani ba amman ba yanzu ba kinji."

Mamakin Aliyu take saboda me yake hadata da Allah bayan rayuwar tace, shi bai aure ba itama kada tayi kenan anya ba aljanu ne dashi ba wanda basa son aure to aljanu mana. Hannun ta ya dago yace
"Yes nasan zaki ce ina ruwana da rayuwar ki amman ki sani rayuwar ki na da mahimmanci ga mutane da yawa ingantata zai bawa mutane da yawa farin ciki ki tsaya ki nutsu ki duba kinji little sister dita."

Baki ta turo yai murmushi yace
"Wato bakiji ba ko?"
Hannu ta daura akan bakin ta, yace
"Kin fiso ki ta tara maza suna zuwa su taso miki da son sanin wacece ke ko?"

Ji tayi zuciyar ta ta karye dan tabbas duk wanda ya ganta zai so ya mallake ta kuma tana yawan samun masoya amman ta ina zata fara sam bata fatan abun da ya faru akan ta da Muhammad ya kara faruwa bata fatan tarihin ta yai ta yawo ana mata wani kallo wanda bata san dai dalilin komai ba amman kuma tabbas duk abinda Aliyu yake ada gaskiya ne, amman tayaya zata na gujewa samarin dake kawo mata hari, tana lura da wanda suke tare da Fauwaz yadda yake ta shishige mata bata san ya akai ba sai kawai jin hawaye tayi na bin kumatunta tabbas tasani rayuwar ta abin tausayi ce shin ko ta auri Muhammad wane hali zata shiga a gidan sa, kada wata rana ai mata gori da ya zataji anya kuwa batai gangancin amsar soyayyar Muhammad ba, Aliyu ganin hawaye a idon ta ya hau lallashi amman ina kana dada tunzurata yayi, wannan yasa ya janyo ta jikin sa ya rumgume ta hadi da runtsa idon sa, dan abinda yaji a tare da shi, tana jin ta a jikin sa taji wani nutsuwa wanda bata san lokacin da ta sauke ajiyar zuciya ba, take kukan nata ya dauke, so take ta bar jikin nasa amman kuma ya matse ta a jikin sa.

Ido ta lumshe muryar sa mai taushi taji yana fadin
"Kiyi hakuri banyi niyyar na saki kuka ba amman gaskiya na fada miki, damuwa ki tawa ce zan fiki shiga damuwa da gaske nake, ina jin ki tamkar su Najwa a tare dani dan haka dole na damu da damuwar ki, ki daure ki cika min buri na akan ki Maryam."
Ido ta runtse ya dago kanta daga jikinshi yasa hannunshi ya rike fuskata yana duban idota hawaye na zuba, idonshi cikin nata yake kallonta, da sauri ta runtse idonta dan ba zata iya jure kallonshi ba ya sakar mata fuska sannan ya dauko handkerchief ya fara goge mata hawayen fuskar ta sai da ya gama sannan ya amshi jakar ta yace
"Kwalliyar duk ta baci duk da daman ba so nake a gani ba amman dan shafa hoda kadan ba da yawa ba kar maza su kara rikice miki."

Kallon sa take dan a wani lokacin in yai abu mamaki yake bata ta kasa gane ina ya dosa, shima gane yasaki layi yace
"Saboda tsaro fa kar azo a saka miki damuwa."

Kai kawai ta dauke, ya bude jakar ya mika mata hoda ta amsa ta fara shafawa kura mata ido, har ta gama ta juya ta kalle shi, ya saki murmushin sa mai kyau ya juya ta kalli agogo har tara saura, tace
"Yaya lokaci na kurewa fa."

Bai Kalle ta ba duk da yaji dan in ta shine ba wata dinner ganin bai juyowa ba tace
"Yaya."
Ya dago yana kure ta da idon sa yace
"Menene?"

"Yaya dare nayi fa."
"Agogo ya kalla yace
"ko mu koma gida?"
Yadda ya hade rai yasa ta dauke kai kawai, ya gyara zaman sa ya tada motar suka bar wajen. Ko da suka je har ango da amarya sun shiga ana ta biki.



*Allah ya jikan musulmai ya kyautata namu zuwan yasa mu cika da kyau da imani. Amin*


*Antty*
[11/27, 14:18] Maryam S IndabawaπŸ₯°: ο»ΏπŸ’—πŸ’— *MATAR HAIDAR* πŸ’—πŸ’—
Page 60

By
*MARYAM S INDABAWA*

*HAKURI DA JURIYA ONLINE WRITERS*
HAJOW
✍🏻✍🏻✍🏻
🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
(United we stand, our aim is to educate, entertain and enlighten our readers in a adventurous manner.)

Facebook @Maryam Sulaiman
Instagram @Maryam S Indabawa
Wattpad @MSindabawa

*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*


Suna parking ta fara kokarin bude kofar da sauri ya dannan lock ta juyo zatai magana, ganin ba fuska yasa ta koma ta jingina a jikin kujera, sai da ya gama danne dannen sa sannan ya dago yana kallon ta hannu ya saka a aljihu ya zaro yan 500 bandir biyu ya mika mata, amsa tayi tace
"Nagode."

Unlock yayi ya fita itama ta bude ta fita, gaba yai yana tafe tana bin sa a baya, a bakin hall din suka hadu da Tasleem wacce akai mata wata heavy makeup ga shi ta saka wani material mai kyalli an mata gown ta kamata sosai ba mayafi sai yar jaka da waya a hannun ta da hill shoe, tana ganin sa ta taho tana fadin
"Yaya ina ta jiran ka fa."

Kamar ba dashi take ba haka yazo zai shige ta kamo hannun sa ya dago a zafafe da sauri ta saki hannun nasa ya bita da wani bazan kallo, Maryam dai shigewa tayi ta barsu a wajen, tana shiga taga Muhammad zai fito, hanya ta bashi amman sai yaki yabi ya tsaya kallon ta, dagowa tai tana kallon sa tare da kallon bayan ta ko Yaa Aliyu ya shigo, a hankali tace
"Ina zaka?"

"Nemo ki mana. Ina ta kira bakya dauka."
Wayar ta kalla tace
"Tana silent ne."

"Wa ya kawo ki to?"
"Yaya ne."

"Oh ya dawo ne?"
Kai kawai ta gyada ta fara tafiya yabi ta yana fadin
"Amman kinyi kyau my love."

"Ka fini yin kyau in Jawahir ne?"
"Naganta tare da dayan Yayan nan naki."

"Oh Yaa Farouk, kace sun hadu."
Ta karasa wajen Najwa da ta dauke kai tace
"Haba Amatya ya da bata rai."

"Wai sai yanzu zaki zo "
"To kema yaushe kika zo din."

"Au haka ma zaki ce ko?"
"To ya zanyi Yaya ne ya tsaya harkar gaban sa."

"Meyasa kika zauna ya kawo ki ai kinsan halin sa."
"Kinga mu bar maganar nan, amman fa kinyi kyau."

Ta kalli Abdul tace
"Ango kunsha kyau fa."
"Yace ai fushi muke. Ta hade hannaye tace
Tuba nake, sannan ta bar wajen tana murmushi, wajen su Jawahir taje suka gaisa sannan taje ta samu Momy da Ummi daga nan ta samu waje ta zauna tana mai daukar wayar ta, ta fara danne danne akai akai tana dagowa tana kallon yadda ake gudanar da abubuwa
"Amarya ta."

Ya fada cikin cool voice din sa ya zauna tai murmushi kawai yace
"Wallahi Baby kinyi kyau kamar na hadiye ki."
Murmushi ta saki, tana yin kasa da kan ta ya daga hannu ya kira MC ya karaso yace
"Ina son fili amare dani da tawa amaryar."

"An gama ranka ya dade."
Ya fada yana barin wajen, yan 1k ya dire mata a gaban ta har guda uku Maryam ta dago tana fadin
"Na menene?"
"Liki."

"Yaya ya bani fa."
"Wannan na mijin ki ne ba yaya ba."
Zatai magana ya daura hannunsa akan lips din sa yace
"Ba kyau mai da hannun kyauta baya."

"Amman ai sunyi...."
"Dauki kawai."
Dai dai lokacin da MC ya fara kiran suna Muhammad Auwal akan ya fito ango da amarya na jiran sa, kirari ya farai masa Muhammad ya mike ya juyo ya kalli Maryam da bata da alamar mikewa, yace
"Dear!"

Dagowa tai ya kafe ta da idanun sa yace
"Taso mana."
Ba yadda zatai ta mike yai gaba tabi bayan sa, ganin yai mata nisa yasa ya tsaya har ta karaso suka jera in kagansu sai sun baka sha'awa dan kuwa sun dace da juna, amarya a tsaye da ango suka hau stage din dai dai shigowar Aliyu ya hange ta a saman stage tana liki wani abu yaji ya tsaya masa a makoshi bai kara shiga damuwa ba sai da yaga Muhammad a gefen ta ji yai kamar ya bar hall din amman ya samu waje ya zauna tare da zaro wayar sa yana danne danne, hakika bai so zuwa dinner ba dan shi bai fiya zuwa biki ba in ba daurin aure ba amman dan ya kula da ita yasa yazo sai dai zuwan na neman ya sa masa hawan jini, in ya dago yaga yadda Muhammad yake mata magana kasa kasa yana mata liki ji yake kamar ya tashi yaje ya janye ta, sun jima Muhammad na barin kudi sai kirari MC yake masa sai da Maryam ta bar wajen sannan yabi bayan ta, zuciyar Aliyu kamar ta buga bayan sun zauna aka kai musu lemo ya bude mata ya mika mata ta dago ta kalle shi ta amsa tana murmushi ya kufala duk a kan idon Aliyu da ya kasa daina kallon su, kiran yaye da kannen amarya akai wannan yasa su Anty Asiya duk suka fita, Farouk ma ya fita ganin ba Aliyu da Maryam ya je ya kamo hannun Aliyu da kyar ya kai shi kan stage ai kuwa kannen sa duk suka hau zuba masa kudi, Maryam ya hango yaje ya kamo ta suka hau stage din, rafers din yan 1k Aliyu ya balle ya dinga zubawa kannen sa, suma suna masa liki, sauran suna rawa, Maryam dake gefe a tsaye ba abinda take ya juya yana zubawa kudi take camera man da mc suka hau kirari tare da fadin
"Yayan ango da tashi amaryar Allah ya kara dankon soyayya."

Aliyu kuwa sam idon sa ya rufe sai da ya juye mata su tas sannan ya bar wajen, juyawa tai zata bar wajen Najwa ta kamo hannun ta tana dan jujjuga ta Maryam bata iya rawa ba hasalima kunya take ji, a haka ta koma wajen zaman ta duk bata da nutsuwa akai akai tana dagowa tana kallon Aliyu da ya hade rai kamar bai dariya.

Iyayen amarya da aka kira shi yasa Maryam fita ta hau yiwa su Ummi liki suma suna mata, a haka kai musu picture gaba dagan su. Har karfe sha dayan dare shagali ake sha, Maryam na zaune ita da Muhammad da sai hira yake bata tana dariya dan Muhammad ya iya daukewa mutum kewa da sasu nishadi, Aliyu dake hangen su yazo wuya, a fusace ya mike ya karaso inda suke tana ganin sa ta dauke kai yace
"Tashi muje."

"Yaya ba fa a tashi ba."
Wata tsawa ya daka mata wannan yasa ta mike da sauri tayi waje ya bi bayan ta har bakin hall din ya kalle ta yace
"Shige muje."

"Yaya ni zan taho da su Ummi wallahi ba zan iya zama ni kadai a gida ba."
Bai kula ta ba ya nufi wajen da yai parking tabi bayan sa kamar zatai kuka ya bude mota ya nuna mata, ta shiga ya rufe ya juya ya bar wajen da kallo ta bishi a tunanin ta lokacin zai fito amman me tin tana jiran fitowar sa har ta fara jin tsoro, wayar ta ta dauka ta fara kiran layin Basma tana dauka tace
"Ina Yaya?"

"Gashi can."
"Me yake?"

"Danne danne ke kina ina?"
"Shikenan."
Ta kashe wayar ta fara neman layin sa ko ya manta da ya barta a mota ne amman har ta gama ringing yana gani bai dauka ba sai da ta kira sau uku amman bai dauka ba kashe wayar tayi dan haushi shi yana can yazo ya kulle ta anan wai dan me yake mata haka ne yayiwa su Basma mana sai ita da ya raina. Kuka ta saki a haka wanda ta kudundune waje daya, bata san lokacin da bacci ya dauke ta ba. Sha biyu saura su Ummi suka tafi wanda sha biyu nayi Aliyu ya hau kada kan kannen sa duk sai da ya ga tafiyar su har amarya sannan yayo wajen motar sa, lokacin sha biyu da rabi tuni Maryam tai nisa a baccin ta, mota ya bude wanda yasa Maryam ta bude ido da sauri tana ganin ta a inda take ta saki ihu, da sauri ya rufe mata baki yana fadin
"Menene haka kiyi addu'a sai ihu ko?"

Ajiyar ta sauke ya kunna wutar motar duk da ta ganshi amman jikin ta sai rawa yake.

Ganin a tsorace take yasa ya kamo hannun ta yana murzawa a hankali yace
"Is ok am sorry kinji."
Idon ta lumshe ya saki hannun ta yace
"Me dazu nace miki?"

Yadda ya daure fuska sai da ya bata tsoro tai saurin yin kasa da kan ta yace
"Wato ke bakya jin magana ko?"
Shiru tayi ya girgiza kai zai magana wayar ta, ta soma ringing shi ya dauki wayar yana duban sunan ganin Ummi ce yasa ya kai kunnen sa yace
"Ummi."

Tace
"Kuna tare?"
"Eh Ummi yanzu zamu taho na tsaya naga kowa ya tafi ne shiyasa."

"To shikenan sai kun karaso."
Ta kashe wayar ya mika mata yace
"Ummi taga dare yayi."
Ya fara yana duba agogo daya saura kwata ya tada mota suka har wajen a hankali yake tafiya kamar wanda bai son tukin bai damu da ganin dare yayi ba ita dai Maryam tana jikin kujera tana ganin ikon Allah kamar ba zasu ba a haka suka karasa gida.


A compound din Ummi yai parking zata bude taji a rufe take ta juyo ta kalle shi kamar bai san me take nufi ba ya dage mata gira, ta kalli kofar tace
"Yaya bacci nake ji."

"Shine bana so kiyi kamar yadda nima ba zan ba."
Ya fada yaba danne-dannen waya, dagowa tai ta kalle shi tace
"To saboda me?"
Leben sa ya cije tace
"Dan Allah ka buden wallahi bacci nake ji."

Kamar ba zai bude ba sai ya bude da sauri ta fice a motar tai ciki, kan ya fito ya rufe har ta haye sama, wanka tayi tana fitowa ta fada saman gado bacci take ji amman sai sam ta kasa da ta rufe sai taga fuskar Aliyu wanda a haka ta dinga juyi har wajen biyu da wani abu, can wajen biyu da rabi kirshirwa ta ishe ta, ta mike ta bude firij din dakin ta sam ba ruwa, sauka tayi kasa ta shiga kitchen dan dauko ruwa, fitilar falon a kashe sai hasken fitilin waje da ya leko, tana shiga ta dauka ta samu ta zauna tana sha, sai da ta sha sannan ta mike rike da guda daya, a bakin kofa taci karo da mutum tayi baya kamar zata fadi, da sauri ya taro ta, baki ta bude da nufin yin ihu da sauri ya daura hannun sa akan bakin ta, ido ta zaro jin ta rumgume jikin mutum, a hankali ya raba jikin su yana kallon ta, ganin Yaa Aliyu ne yasa ta saki kuka dan sosai ta tsorata bata taba tsammanin ganin mutum a lokacin ba, kirjin ta in ban da bugawa ba abinda yake.

Hannun ta ya kamo ya dan murza alamar rarrashi, yace
"Ya isa to menene na kukan meyasa da kika sauko baki kunna fitilar ba, me ma ya fito dake da daren nan, me ya hanaki bacci?"
Hannun ta, ta janye tayi hanyar bene da sauri ya kamo ta wanda hakan yasa ta fado jikin sa, matse ta yai a jikin sa yana kallon fuskar ta.

Hawaye ne ke bin kuncin nata, hannu yasa yana goge hawayen dake bin kumatun ta, a hankali cikin muryar sa mai dadi yace
"Ya isa to kinji am sorry daina kukan kinji."
Haka yai ta lallashin ta har tai shiru sannan ya sake ta ta hau sama tana shiga ta fada saman gado tare da lulluba addu'a tayi sannan ta hau tunanin abun da ya faru bata jima ba bacci ya dauke ta.


*
Washe gari da wuri ta tafi gidan Sitti dan kar Aliyu ya hanata fita, ranar lunching akai a wani event centre, tare Maryam da Najwa suka tafi makeup akai musu, karfe biyar aka gamai musu, ana gamawa Abdul da Muhammad suka daukesu, Maryam na gaba, ita da Muhammad, Abdul da Najwa ba baya, a haka suka tafi wajen lunching din ranar sakayau taji ta saboda babu Aliyu amman ita kuma taji kewar sa.

Yana zaune a falo yana danne danne a waya Ummi suka sauko da Yaya zasu tafi wajen Lunching din dagowa yai yana fadin
"Lafiya zakuyi?"

"Eh."
Kallon saman yayi yace
"Ina Maryam din?"

"Ai su sun jima da tafiya."
Da sauri ya mike yana fadin
"Bari na shirya sai na ajiye ku."
Da kallo suka bishi, ya shige daki bai jima ba ya fito sanye da dogon wando na jean da orange kalar riga, yace
"Muje."
Sukabi bayan sa, ya shiga suka bar wajen. Karfe shida saura sukaje wajen suka sauka ya shige, Maryam na ciki, cikin kawayen ta ana ta shagali wayar ta ta fara ringing tana dubawa taga sunan Aliyu, gabanta ne yai wata mummunan faduwa ta dauka tana sallama amsawa yayi yace
"ina jiranki a waje."
Yana fada ya kashe wayar sa, shiru tayi tana nazari Jawahir ta dafa ta tace
"Menene?"

"Yaya ne wai yana waje."
"To kije kiji mana."

Mikewa tayi ta nufi barin wajen fita tayi tana dube duben ta ina zata hango shi, tana tsaye taji ana mata horn, juyawa tayi ta karasa wajen motar, kofar motar ya bude ta shiga ta zauna yace
"Rufe kofar."

Tana rufewa yaja motar ya bar wajen, wayar ta ce ta fara kuka tana dubawa taga Muhammad ne dauka tayi takai kunnen ta yace
"Ina kika je naga fitar ki

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login