Showing 51001 words to 54000 words out of 232912 words

Chapter 18 - Matar Haidar Hausa Novels By Maryam S Indabawa.txt

29 Oct 2025

1241

kawai"

"Wallahi da kansa yake karyewa."
Fuska ta rufe da hannu tace
"Ba kyau fa."

Yai dariyar sa mai kyau yana shafa sajen sa hadi da bin ta da wani kallo yace
"Naga Matata ce menene ba kyaun?"
"Nidai mu tafi dan Allah!"

Gyara zama yayi ya kunna motar suka karasa gidan su Aisha. Katon gida ne wanda tsarin gidan kamar zane ne gidan ya tsaru daga gani mai gidan ya tada kai da naira. A bakin gate yai horn mai gadi ya leko Aliyu ya bude window yana ganin sa ya rissina yana gaishe shi sannan ya koma da sauri ya bude masa gate din. Ciki suka shiga a parking space yai parking, inda wajen aka kawata shi da shuke shuke a compound din gidan ya kara kyau da sanyi. Bag din ta bude, ta dibi kati nan sannan ta kalle shi yace
"Kada ki shanya Mijin ki dai!"
Murmushi tayi tace
"Insha Allahu!"

Ta bude motar ta fita, ya bita da kallo yadda take tafiya a nutse yarinya karama ta gama tafiya da shi gaba daya. Idon sa ya sauke kan mazaunen ta da suke a bude a cikin doguwar rigar tata, ido ya lumshe yana cije lips din sa na kasa tare da shafa sumar kan sa. AC motar ya dado ya lumshe ido kamar mai bacci.



Sallama tayi a bakin kofar sitting room din, aka amsa mata ta shiga Mum din su Aisha ce a zaune a kan daya daga cikin kujerun da suka kara kawata dakin masu kyau. Dakin sai kamshin yake da sanyin AC, tana ganin Maryam tace
"Ah Maryam kece a tafe?"
"Wallahi Mum! Ina yini?"

Ta fada tana durkusawa har kasa suka gaisa sannan tace ya mutan gidan. Bayan sun gaisa tace
"Aishan na ciki yanzu ta shiga bata ce min kuma zaki zo ba."

Kan ta a kasa tace
"Eh bance mata zan zo ba."
"Ayyah to shiga tana ciki."

Ta mike ta nufi dakin ta. Knocking tayi Aisha dake kwance akan gado tace
"Yes come in!"
Maryam ta bude ta shiga, Aisha ta juyo tana ganin Maryam ta mike da sauri ta sauko tazo ta rumgume ta tace
"Daman kina hanya baki gaya min ba dazu!"

"Nima bansan zuwan ba sai da muka gama waya."
"Zauna bari na kawo miki lemo!"
Ta nuna mata gefen gadon ta wanda ya sha zanin gado mai kyau ga laushi kayan dakin duk lemon green ne sunyi kyau sosai.

Zama tayi tace
"Daga gida fa muke kuma tafiya zanyi"
"Haba daga zuwa."

"Ni da Yaa Haiydar ne fa!"
"Ah ai nasan ba zama zaki ba tinda kuka zo tare."

Ta mike ta nufi fridge ta dauko mata lemo biyu da ruwa biyu tace
"Kisha ki kai masa wannan!" Jakarta ta bude ta dauki kati nan tace
"Gasu ki bawa Mum ni wallahi kunyar ta nake ji na bata da kai na. Dan Allah ki kaiwa su Abra, Widad, da Muwadad!"
Yan uwan su Aisha ne wanda tare sukai graduation ya'yan yayen Mum din ta ne da kuma Kanenen Dad din ta.

"Sannan duk wanda yake na kusa dake anan zan kaiwa Rukky ma please Sister kinga Ammi tace wai daga yau bazan kara fita ba."
"Kada ki damu insha Allah zan bawa duk wanda ya dace zanyiwa Rukky magana sai muji yadda abin zai kasance."

"Nagode!"
Ta fada tana mikewa.
"Menene na godiya ai mun zama daya."

Ta dauki lemo kan tace
"Tinda kinki dauka bari na kai masa da kai na."
Suka fita a falo suka samu Mum ta kalle su tace
"Ba dai tafiya ba Maryam?"

"Eh wallahi!"
"Mum kati ta kawo ga naki dana Dad!"
Aisha ta fada.

"Masha Allah! Allah sanya alheri ya kaimu lokacin."
"Amin!"
Aisha ta amsa.

Maryam tace
"To Mum sai anjima!"
"To ki gaida Ammin taki!"

"Zataji!"
Suka fice ita da Aisha. Motar takarasa ta bude yana inda yake tace
"Yaa Haiydar!"

A hankali ya bude ido ya sauke akan ta murmushi ta saka masa ta shiga ta zauna wanda hakan yasa yaga Aisha dake bayan ta. Murmushi ya sakar mata yace
"Kawar Amarya."

"Na'am Yaa Haidar ina yini?"
"Lafiya lou ya gida yasu Mum?"

"Suna lafiya."
"Amman tare dai zamuje gidan su Rukaiyyan ko?"

"Ban fadawa Mum bafa."
"To jeki fada mata kizo muje ma dawo dake."

"To bari naje!"
Ta mikawa Maryam lemon ta juya tayi cikin gida. Kofar ta rufe tace
"Ga ruwa!"

Ta fada tana bude masa ta bashi, amsa yayi ya dan kurba sannan ya bata tasha kadan ya kara sha ya rufe. Lokacin Aisha ta dawo ta shiga baya suka tafi gidan su Rukky.

A compound suka same ta tana zaune a gefen gidan su inda garden din su yake tana ganin su ta mike tazo suka rumgume juna. Yaa Haidar ta gaisar sannan sukai ciki a falo suka sami Mom din ta suka gaishe ta, ta amsa sannan suka tafi dakin ta suna shiga mai aiki ta fara kawo musu lemo da kayan motsa baki.

Maryam tace
"Mu da zamu tafi!"
"Uhmm ke haka kike daga zuwa sai tafiya."

Murmushi tayi tace
"Sauri muke!"
Ta kwaso katin ta ajiye mata tace
"Kema ki basa su Sakina, Hibba, Izzatullah, sannan sauran ku sasanta yadda zaku rabawa sauran yan ajin mu, gana Mom da Dada!"

Ta bata amsa tayi tace
"To Aisha ya zamuyi?"
"Kinga kawai in zaki fita ki biyo ta gida mukai ko?"

"Eh hakan yayi gobe sai mu fara kinga lokaci ya kure ko?"
"Allah kaimu."

"Yauwah wai yaushe zaku taho?"
"In munzo ranar kamu shikenan ko?"

"Har sai ranar kamu please kuzo Talata mana!"
"Ba dai ranar Laraba kamu ba, Alhamis dinner, Juma'a daurin aure da yini da kai amarya so kinga muzo Laraba mu taho Friday ko?"

"Lallai ma ni Talata zaku zo ku dawo Asabar!"
"Kai Besty kin fiya rigima."

"So kuke na zauna ba kowa a tare dani kunsan bani da kowa dai sai ku ko?"
"To shikenan ya isa zamuzo Talatar amman sai yamma ko dare saboda zamu lalle da gyaran kai ko?"

"Kuzo da wuri mu tafi tare ko?"
"Shikenan zaki ji mu."

Ta mike tace
"To nidai na bar Yaa Haidar a waje fa."
" *Matar Yaa Haidar* Allah tabbatar da alheri!"

"Amin!"
Ta nufi kofa. Rukayya tace
"Ke bakici komai ba shima ba zaki kai masa komai ba."

Aisha ta dibar masa suka fita sukai sallama da Mom. Mota suka shiga suka maida Aisha gida sannan suka tafi gida. Yana parking ya kalle ta yace
"Nawa zan bayar kudin abubuwan ne?"

"Ka barsu zanyi magana da Ammi in akwai bukatar abu zanyiwa Abbi magana."
"Yakamata mu na hutar dasu Abbi by now zan turo miki kudi ko da bukatar su zata tashi, in kina bukatar dadi ki min magana."

Har ga Allah ta manta da tana da wani account dan ko kudin da aka bata 1m ma yana ciki tacewa Abbi ya amsa yace ta ajiye a wajen ta, bayan Yaa Aliyu da yake yawan saka mata kudi banda duk lokacin da yaji alert har in ya samu kudi tura mata yake.

"Tunanin me kike?"
"Na tuna ina da kudi ne Yaya ba sai ka turon ba zanyi amfani dasu nagode!"

"A'ah wannan hakki nane ki amsa kawai."
"To nagode Allah saka da alheri ya biya maka bukatun ka. Ya rabaka da iyayen ka lafiya."

"Amin *Matar Haidar* ki shiga gida ana kiran magariba bari naje masallaci."
"Ai mana addu'a!"

"Insha Allahu!"
Tayi ciki shi kuma yai alwala anan compound sannan ya tafi masallaci.


Washe gari tin safe aka farai mata gyara na musamman wanda daga daki sai daki ko babban falo bata fitowa duk abinda take bukata Biba ke mata ta kai mata. Wanda cikin kwana biyun nan ta kara haske sosai kirjin ta ya kara cikowa, kamshi kuwa har ya zauna a jikin ta duk inda ta zauna sai ya kama.

Kwance take akan gado lokacin karfe goma saura sanye take da wando three quarter da vest a jikin ta kan ta sanye da hula waya kare a kunnen ta tana fadin
"My kayi hakuri jibi zani lalle da gyaran kai sai mu hadu kaji!"

"Ba zan iya ba wallahi ba zan iya ba kawai ki fito in ba haka ba zanyi knocking Allah ko Ammi tace menene zance ke kika kirani gwara ma ki tashi tinda Ammi ta kwanta kizo ki bude ki fito naganki kawai."
"In ganina kake so kayi in hada mana vedio call!"

"No bana son ido cikin ido nake so na ganki!"
"Please....."

"Ma'ul Ayn kada kice komai kinsan dai ba kyau ko?"
Jikin ta ne yai sanyi dan daga yadda yai maganar ma kasan yana cikin damuwa. Mikewa tayi tace
"Shikenan ka taho bari na bude maka!"

"Ina kofar part din naku!"
"Toh!"



*Allah ya yafe mana ya jikan mu yasa muyi kyakyawan karshe amin*


MS INDABAWA
ANTTY

ο»Ώο»ΏπŸ’—πŸ’— *MATAR HAIDAR* πŸ’—πŸ’—
Page 17

By
*MARYAM S INDABAWA*
HAJOW


*Bismillahir Rahmanir Rahmin*


Ta saka hijab ta fito tana sanda a hankali ta fito ta bude ta juya ta kalli kofa sannan ta rufo ta fito da sauri. Tana juyowa taji ya rumgume ta.

"Yaa Haidar ka bari a waje fa muke kada wani ya ganmu!"
"Ina ruwa na, ni dai tinda naga matata."

Tai murmushi ta tsaya kallon sa tace
"Ai ka ganni ko sai da safe!"
Ta juya zata shiga yai saurin kamo hannun ta wanda ya dada taushi kamar auduga, ido ya lumshe yace
"Kin dai mai dani kakanki ko?"

"Ah haba ina fa."
Hannun ta ya kai hancin sa yana shinshinawa tare da sakin ajiyar zuciya hadi da lumshe idanun sa. Yace
"Wannan kamshin fa? Wane irin turare ne haka?"

Hannun take son janyewa ya janyo ta jikin sa gaba daya yana son cusa kansa cikin jikinta dan yadda kamshin ta ke tada masa hankali. Idon sa ya gama rufewa ga kewar ta ga kamshin ta mai tada hankalin ya rikita masa lissafi. Jikin ta sai rawa yake na tsoro a hankali tace
"Yaa Haidar, Ammi fa!"

Da kyar ya sake ta yana mai da numfashi yace
"Wannan turaren ki daina saka shi sai mun tare kina ji ko?"
Kai ta gyada sai yai sauri ya juya yace
"Koma kije ki kwanta sai da safe!"

Yai magana muryar sa a sanyaye. Gaban sa ta dawo tace
"Menene Yaya nah."
Murmushin karfin hali ya sakar mata yace
"Ba komai!"

Ya kamo hannun ta ya bude kofa ya saka ta sannan ya rufo maimako ya koma dakin Alkasim sai kawai yayi gidan su dake gefen nasu Maryam.

Wanda a tsarin ginin da girman sa har yafi nasu Maryam girma da tsaruwa. Mai gadi yana kwance yaji knocking ya taso ya bude masa yana shiga ya wuce bangaren sa. Sanin ba anan yake kwana ba yasa bai rufe kofar ba kawai ya koma ya zauna.

Aliyu yana zuwa bangaren sa ya shige wanda yake kamar na wani magidancin dan komai akwai. Yana shiga ya fada bathroom din sa ya fada ya sakarwa kan sa ruwa ko zai samu saukin abinda yake ji amman ina kamar ana kara masa wutar sha'awar ta. Kan gado ya fada yana jin yadda jijiyar sa ta mikewa tana bukatar agaji. Ido ya runtse dan jin yadda marar sa tayi tauri kamar dutse.

Wayar sa dake cikin aljihun jallabiyar sa ce tayi kara da kyar ya saka hannu ya zaro wayar ba tare da ya duba wanda ya kira ba ya kai wayar kunnensa ya saki nishin wahala sannan yai sallama da kyar. Da sauri ta mike daga kwanciyyar da take ta amsa sallamar hadi da fadin
"Lafiya Yaya meyake faruwa ne?"

"Me kika ji *Matata* "
"Jifa muryar ka, ka fada min me yake damun ka."

"Ba komai fa."
Kuka ta saka masa tana rokar sa ya fada mata wanda kukan nata ke kara ingiza yanayin da yaje ciki sai faman nishi yake da danna marar sa yana mai hade kafafun sa.

"Dan Allah ka fada min!"
"Zan fada miki amman ki min alkawari zaki sama min mafita."

"Nayi Yaya zan sama maka nasan addu'a ce zan maka ka fada menene?"
"I need you *Matar Haidar* wallahi ina cikin wani hali Matata, ki taimaken ki gusar min da wannan yanayin da nake ciki dan Allah "

Hawaye ne yake zuba a idon ta, ta rasa me zata ce masa yace
"Kina ji na?"
Sheshekar kukan ta ya jiyo ya cije baki yace
"Ni nasan ba zaki iya ba, ciwo na ba naki bane ko? Damuwa ta ba taki bace ba ko? Shikenan sai da safe ki kwanta kiyi bacci."

Yana gama fadar haka ya kashe wayar gaba daya ya cilla ta gefe ya dinga fama shi kadai. Yana kashe wayar ta fada kan gado ta fashe da kuka a ranta take magana can ta dauki wayar tana girgiza kanta, ta fara neman layin sa amman a kashe. Da sauri ta mike ta saka hijab ta fita falon. Kofa ta bude tayi bangaren Yaa Alkasim tana isa ta tsaya ta kasa taba kofar tafi mintina sannan ta tura kofar a hankali taji ta a bude ciki ta shiga ba kowa a falo dan haka ta nufi kofar bedroom din sa ta fara knocking.

Alkasim dake bacci ne yaji knocking ya mike yana salati ya duba yaga ba Aliyu mikewa yayi ya fita ya bude kofar. Maryam ya gani tsaye kallon ta yayi yace
"Menene?"

"Ina Yaa Haidar?"
"Ina jin yana bandaki menene?"

"Ina son ganin sa ne!"
Ciki ya koma ya tsaya bakin kofa yace
"To kai kayi sauri matar ka na waje tana jiran ka."

Ya koma ya kwanta kawai. Maryam dake falo ganin kusan rabin awa yasa ta kara komawa tai knocking Alkasim yana bacci ya kuma mikewa. Agogo ya kalla yaga sha daya da rabi mikewa yayi ya kara fita da mamaki yake kallon ta wannan lokacin yace
"Menene kuma?"

"Ina yake?"
"Wa?"

"Yaa Haidar?"
"Bai fito ba?"

Kai ta gyada tana share hawaye komawa yai da sauri ya bude bandakin ba kowa dan haka ya fito yace
"Kila ya tafi gida fa."

"Yaa Alkasim dan Allah ka kira min shi mana."
Waya ya dauka ya fara kira amman a kashe ya dago yace
"Wayar tasa a kashe lafiya?"

"Muje ka kira min shi dan Allah."
"Dare yayi fa har sha biyu saura menene?"
Durkusawa tayi tana kuka tace
"Ni dai ka kira min shi."

"Zan kira shi amman kinsan menene tashi kije ki kwanta kar Ammi ta leko taga kofa a bude kinji in na kirasa zan zo sai mu taho."
Ta mike ya rakata har kofar part din su sannan ya fita amman sai ya kasa buga kofar gidan su Aliyu dan dare yayi kada ya tada musu da hankali ya jima a haka dai ya jingina da kofar ji yayi kofar taja baya ya shiga kawai ya samu mai gadi na ta baccin sa. Kai ya girgiza kawai yayi sashen Aliyu. Kwance ya same shi ko numfashi bayayi da sauri ya dago shi yana kiran sa amman ina bai ji. Ruwa ya debo ya shafa masa nan ma bai farka ba da sauri ya mike ya je ya taso mai gadi yazo ya taimaka masa suka sashi a mota ya tafi asibiti dashi yana zuwa aka amshi shi emergency, sai wajen daya sannan suka samu ya farfado allurai sukai masa sannan suka barshi dan ya huta take baccin wahala ya dauke shi.

Alkasim ya shiga ya zauna a kusa dashi karfe uku ya farka yaga Alkasim akan sa dakin ya kalla ya mike da sauri yana fadin
"Me muke anan? Tashi mu tafi."

"Aliyu baka da lafiya fa!"
"Ni lafiya ta kalou."

"To bari na kira Dr!"
Ya fita yaje ya taho da Doctor wanda abokin Aliyu ne yana zuwa yace
"Alhamdulillah jiki yai sauki ko?"

Kai ya gyada yace
"Dadin tama dai ka kusa aure amman da baka kusa ba wannan matsalar zata iya halakaka, kana kiyayewa!"
Kai ya gyada yace
"Insha Allahu."

Alkasim yace
"Me yake damun sa ne?"
Mikewa Aliyu yai ya fita. Dr yace
"Yana da matsananciyar sha'awa wacce take sa shi shiga wannan halin in ta motsa masa."

"Shege jarababbe ai na jima da gane hakan zan fadawa Abbi ai maza a daura auren kar ya mutu."
Ya mika Dr hannu suna murmushi yabi bayan Aliyu.

A mota ya same shi yana zaune kan sa jingine da kujera ya lumshe ido. Murmushi yayi yace
"Ashe jarabarce ta motsa ince zuwa kayi ka tadawa yarinya hankali dazu tazo tana tai min kuka sai na kira ka."

Bai motsa ba bare ya kulasa, Alkasim sai iya shege yake masa amman ya ki kula sa. Suna shiga ya wuce yai wanka ya shirya suka tafi masallaci. Shida suka dawo gida a falo ya kwanta Alkasim ya shige yana fadin
"Bacci nake ji wallahi."

"Wa ya hana ka bacci?"
Aliyu ya fada yana gyara kwanciyya kan three sitter.
"Au haka kace?"

Alkasim ya fada yana yin ciki ya cigaba da cewa
"Zaka sani ne."
Ido ya lumshe ya fara karatun Alkur'ani a hankali cikin muryarsa mai dadi da sanyi.


*
Maryam kuwa gaba daya ta kasa sukuni dan ba alamun Yaa Alkasim ta kira sa amman baya dauka wajen daya ta koma dakin nasa babu shi ba Aliyu daki ta koma ta zauna akan sallaya sai kuka. Haka wajen biyu ma ta kara komawa amman babu su kwata kwata. Karfe uku ma ta kara zuwa babu su. Daki ta koma ta dinga kuka dan ta rasa nutsuwa me yake faruwa ina Yaa Haidar ya tafi. Har aka kira sallah asuba ta tashi tai alwala tai sallah.

Ta na idar da azkar ta mike ta fito ba kowa a falo kitchen ta shiga ta gaisar da Ammi da Baba Ramma sannan ta fita ta nufi bangaren Yaa Alkasim tana bude kofa ta fara jiyo kira'ar sa, ido ta lumshe sannan ta shiga kwance ta ganshi akan three sitter da sauri ta karasa ta zauna a kasa gaban kujerar cikin muryar kuka tace
"Yaa Haidar!"

Idon sa ya bude a hankali ya sakar mata murmushi yace
" *Matar Haidar* "
Sai ya fara kokarin mikewa. Kallon sa tayi har ya zauna duk ya fada na lokaci daya.

"Ka yafe min Yaa Haidar!"
Hannun sa ya daura akan ta yace
"Na yafe miki *Matar Haidar* na yafe miki. Kin tashi lafiya?"

Hawaye ne ya zubo mata yace
"To menene na kukan?"
"Yadda kake so na, ni na bata maka na kasa kawar maka da bukatar ka duk da....."

Hannun sa ya daura akan bakin ta yace
"Kada kice haka ni nasan kina so na kuma kin damu da bukatata nasan dalilin ki na bijire min ba komai mun kusa mu zauna cikin inuwa daya wacce zamu kasance cikin nutsuwa nasan a lokacin zaki ban duk kulawar da nake so kada ki damu kinji sauran kwana nawa ne?"

Kai tayi kasa dashi, yayi murmushi yace
"Sauran kwana hudu ko?"
Kai ta gyada masa a kunyace yace
"Ina fatan kinyi bacci dai!"

Kai ta girgiza tace
"A'ah Yaya nakasa na kasa saboda bansan a halin da kake ciki ba nace Yaa Alkasim yaje ya kira ka amman bai dawo ba da tini nazo da kai na to kada Ammi tazo taga bana nan ne kayi hakuri!"

"Ba komai, *Matar Haidar* bata laifi kuma bana fushi da ita."
"Nagode Yaya nah!"

Ta mike tace
"Ban gaishe da Abbi ba bari naje!"
Ta nufi kofa mikewa yayi yabi bayan ta yana fadin
"Muje nima na gaishe sa."

Tare sukaje

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login