Showing 186001 words to 189000 words out of 228147 words

Chapter 63 - MAGE (Mai kwanciyar Daukar Rai) Book Complete Na Sajida complet.txt

13 May 2025

10388

Nadiar kanta dake zaune kawunnansu a kasa ta ce " Ku yi hakuri, a yanzu ba zai iya bayar da hakuri ba, ku tashi a raka ku bangarenta ta huta "

Da sauri Nadia ta ringa girgiza kanta, a tsorace ta ce" AMMI, dan Allah aa, akoy maciji a cen "

AMMI ta dam sauke ajiyar zuciya ta ce " to ku tashi ku je bangarena, nima gani nan zuwa "

Ai kuwa mikewar suka yi ita ta yima mamanta jagora hanyar bangaren AMMI suka bi suka shige

Dubanta ta kai wajen UMMU a sanyaye ta ce" idan yaya ya dawo zamu yi shawara da shi kan maganar wannan ware waren turakar, bana jin zan iya kuma barin hakan ta faru"

Ita dai kai ta gyada kawai, domin baki daya jikinta ba karfi, harma mamakin irin karfin zuciyar AMMI din take, duda takan share hawaye lokaci zuwa lokaci aman sai kokarin gannin ta daidaita komai take

Wayarta ta ajiye, tana kara taba jikin NAJEEBA

Cen sai ga tsohuwar JAKADIYAR dake kula da kebantacen wajen da ake kebe ahalain gidan da wani abin ya ritsa da su

Sosai ZINARIA ta fashe da wani irin kuka tamkar zata side a lokacin da suka kamata suka mikar da ita

A kausashe Jakadiyar ta furta" Hatara dai Zulaihat, sasauta muryarki a falon mai damagaram kike "

Ai kuwa ta yi kitttt tana ji tana ganni suka fice da ita duda an bi ta sirri da ita aman ina ta tabata wannan magana har ta gama yada fada, ita kam ina zata saka ranta? Ina zata tsoma ranta? A irin yanda take da wulakanci, yanda ta dauki masu yi mata hidima da sauransu tamkar wasu bayinta, sam ba maganar mutuntawa sai tarin wulakanci da tozarci, dan ta tofa maka yawu ta kireka dan talakawa bawanta ba wani abu bane, dan ta saka a yi maka bulaka ba wani abu bane, tana jin dadi idan tana wulakanci, takan ji kwonciyar hankali da nutsuwa a zuciyarta idan tana wulakanci, a ganninta wannan shi ne bambancinta da sauran, wannan shi ne bambancinta da talaka, sai gashi yau zata je kebantacen wuri, wajen da ba rasa ci, sha , sutura zaka yi ba, bambancin shine bata da wata alfarma a wajen sarki, bata da damar ganawa da shi, bata da damar dora doka ko taka wani, tana da yan hidima sai dai bata da damar wulakanta su domin inci ne da su, suma sunna wajem da suke fada a ji ne, zata je duniyar mahidimta ne, wajen da suke nasu sarauta ne, y'aya da jikoki ne, bata da damar sakawa ko hannawa sai abinda hali ya bada ne, hakan ya matukar razanata, ya hanna mata sukuni har aka karasa da ita fadi take a bata wata

Basu hanna mata ba, suka bata wayar , nan da nan ta yi kiran mahaifiyarta ta shaida mata wannan labari da ya kusan saka maman nata jin zuciyarta zata tsaya
Itama hankali tashe ta nemi gannin sarki a kusancin magaribar nan wanda a yau bangaren Zahrau yake, sai dai amsar da aka bata cewar ba zata samu ganninsa ba ya sakata yin zaman yan bori, a nan kasa inda kuyanginta suka rikice harda yar kazaginta wace ta fece da gudu bangaren Yarima dan kai masa labarin halin da mahaifiyarsa ke ciki


Wannan kennan


Sai da AMMI ta ja numfashi ya fi a irga sannan ta kara shafa kan NAJEEBA a hankali ta ce" tashi Najeebana "

Da taimakonta da na UMMU ta mike tsaye

Ammi ta kama hannunta da niyar tafia da ita bangarenta , duda ba haka take so a kasan zuciyarta ba sai dai gannin kamar NAJEEBAR nada bukatar taimako sai ta kasa barinta a nan din

A hankali UMMU ta ce" AMMI, me zai hanna ita a barta a nan? Mai yiwuwa ta taimaka masa da wani abin?"

Sai da ajiyar zuciya ta kwacewa Ammi, aman sai ta kada furta komai ta ja ta tsaya tana kallon yannayin NAJEEBAR

Gannin kanta a kasa tana ta wasa da yar yatsarta sai AMMI ta lumshe idannuwanta ta juya a hankali ta yi gagawar kama hanyar tafia, kwarai tana son ya samu kadaicewa da mace koda kuwa ba abinda zai shiga tsakaninsa da ita, koda kuwa ba zai yi maganar abinda ke damunsa ba, koda kuwa ba zai kulata ba, tana son wani ya kasance a kusa da shi, shima fa mutun ne, mai rauni, mai tare da damuwa, mai son idan yana cikin damuwa ya samu mai taya shi, mai bashi shawara, mai nutsar da zuciyarsa

UMMU ta kama hannun nata da take wasa da shi, a sanyaye ta ce" ki shiga ruwa masu zafi ki jima a ciki sosai, sannan ki sha ibuprofen"

NAJEEBA ta dan gyada kanta tana hadiyar yawu masu zafi a makogwaronta cike da yannayin damuwa

UMMU ta dago habarta a sanyaye ta ce" my BEEBA? "
Najeeba ta kaleta jin wani sunna da ta fada

Ummu ta yi dan murmushi ta ce" SHAHEED ne yake ce maki MY BEEBA, a lokacin da ake kawo ki wuni wajen AMMI din ki "

Da mamaki a fuskarta, muryarta a sanyaye ta ce" Dama yana min magana ina karama? "

Murmushi UMMU ta yi ta ce" yana son yara kananu, burinsa AMMI ta haifa masa kani shima, ganninki a wajenta sai ya samu abin nishadi idan ya baro fada da wajen horo da hawa doki, yakan yada zango a bangaren da aka zuba maki kayan wasa da masu kula da ke, sukan bara maku wajen shi kuwa ya ringa saka ki tatata kamar yanda kike tafiarki a hankali sai ya ce *ZO NAN MY BEEBA* , tun baki iya sunnansa ba, irin yanda yake zuwa da ke wajen mai martaba shi kuwa yana kama sunnansa ne kai tsaye har kika iya da maganar yara sai ki ce " JAHITT, wai SHAHEED "

Wani murmushi ne ya dan subuce mata , sai kuma ta kalli UMMU ta ce" to me ya da daga baya ya tsane ni? Me ya sa daga baya na kasance babar makiyiyarsa? Kaf cikin yan uwana na dawo ni ya fi tsana? "

Ummu ta lumshe idannuwanta, a hankali ta ce" ni kaina ina son sani, ko zaki yi kokari ki samo mana amsar nan?"



.............hi............
[31/03 à 22:01] Sadjida: 🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻


*Na*


*SAJIDA*


💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝

☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_



57




Kanta kawai ta sada bata iya baiwa mahaifiyarta amsa ba, a haka UMMU ta saki hannunta ta bi bayan AMMI

Ta jima nan tsaye tana saka tana kwoncewa,
Tana ta nazari ne a kan rayuwarta ita kanta, kafin ta daga kafarta da kyar ta shiga takawa ta nufi dakin da a ranar ta ga ya fito da Nadia daga ciki

A hankali ta idasa saka kafafuwanta tana bin dakin da kallo, ba sanyi domin Ac a kashe, sai dai da kamshin sansanyan turatan wuta

A haniali ta taka ta nufi bayi du kuwa da irin yanda take jin jikinta ba karfi kwata kwata

Ruwa ta tara masu zafi ta rintse idannuwanta a hankali ta fara saka kafafuwanta sannan ta rintse ido ta zauna wanda hakan sai da tmya sakata kama abin nan ta rike da karfin gaske

Idannuwanta rintse suke kakam, abubuwan rayuwa take ta tunawa, yau gata a gidan da ba saki sai ka aikata kisa ko zina, biyu daga cikin abubuwan da rana bata fitowa ta fada bata nemi da Allah ya tsareta daga mumunar kadarar da zata kaita aikatasu ba
Yau gata a matsayin matar aure, matar farin mutun,
Sai dai abinda ya ki barin kwakwaluwarta shine irin yanda yake son ya jata da dan wasa duda ba wai wani sakewa ya yi ba aman yannayin da yake nuna na kamar zai tsokaneta na bata matukar mamaki

Kafarta ta riga dan wanawa a cikin ruwan tana kara hauda shi jikinta a hankali ya ringa salabcewa har zafinsa ya ragu sosai

Wannan karron sai ta hada na sabulu mai kunfa sosai mai sansanyan kanshin da ya sakata lumshe idannuwanta,

Ta jima a cikin ruwan nan har sai da ta ji kiraye kirayen sallah sannan ta dauro alwallah ta fito daga bayin da tawul din da ta gani

Tsaye ta yi a dakin daga ita sai tawul, tunaninta kayan da zata saka

A hankali ta fara leko kanta dan so take ta je wajen wayar cen dake ajiye ta yi kira bangarwn AMMI a kawo mata kayanta, sai dai tana lekowar sai ta hangi akwatinta wace take malakinta

Da dan sauri ta fito ta kama tana janta har ta shige dakin sannan ta datse tana sauke ajiyar zuciya

Bata buda akwatin ba sai da ta je wajen turarukan dake ajiye

Ido ta buda sosai gannin turaran nan, sai kuma ta turo baki tana dan gunguni ta dauki guda ta buda ta shiga yiwa jikinta barinsa sosai har kai tana ta kara juyawa da daria a fili ta ce" Na rama cicije min nan da ka yi malan ehe"

Sai da ta gama barnar da gangan dinta sannan ta koma wajen akwatin ta shiga bubudawa
Wata doguwar riga mai hade da hijab dinta har kasa ta ciro wace ta tabata an saka mata ita ne dan sallar

Pant da bras ta ciro sababi ta ajiye
Sai da ta fesa masu tyraran nan son ranta sannan ta saka ta zira rigar ta shiga neman abin sallah
Sai dai sama ko kasa babu, tana nan tana ta zagaye kamar da wasa ta tsinkayonkiran salar isha'i, hakan ya sakata zaro idannuwanta da sauri ta fito ko kashe fitilar da ta kunna bata yi ba tana son yin saurin sosai aman har yanzu ba wai ta saku yanda ya dace bane, ta dai rage jin azabar da take ji dazun aman kuma har yanzun wajen na sukanta

Ba tare da tunanin komai ba ta tura dakin nasa da salama kasa kasa ta shiga

Tsayuwa ta yi tana kallon dakin, ba kowa ciki aman da kanshin turarrn wuta da ya garwaye da turaran daki da kuma na jikinsa da ya fesa sai abin ya bada kamshin ya hade ya cika ko'ina na fakin
Ga sansanyan sanyi dake dakin na AC din da bai kashe ba

Dan tabe bakinta ta yi ta nufi kebantacen wajen da ake sallah a dakin

Wajen a kawace yake, ga alkur'anai mai girma a saman wani dan sif fari kal a jefe da litatafan musulunci da carbunna dai masha Allah

Sallah ta kabarta a hankali ta shiga gabatarwa, tun daga Azahar da bata samu damar yi ba, la'asar da bata yi ba, magariba, sannan ta dora da isha'i

Tana salamewa ta ji muryarsa kasa kasa ya ce" du kina me kika tara sallah haka a kanki NAJEEBA? "

sai da gabanta ya fadi, domin ita dai sam bata ji shigiwarsa ba bale takun tafiarsa, uwa uba kanshin turaran nasa dake shaida mata zuwansa waje itama shi din ne ta kilkila a jikinta ya kasance har hancin nata ya daina jiyo kamshin zabar ya shaka da yawa
Sai da ta dauke numfashi kadan sannan ta dan sada kanta da carbin da ta dauka fari mai kyau a hankali ta ce" Nafiloli na yi "

Dan murmushi ne ya kwace masa a kan labansa, bai ce komai ba ya koma ya gyara zamansa saman gadon ya jinginar da bayansa a jikin kan gadon kadan sannan ya ci gaba da binta da kallo kasa kasa yana mai jan carbin dake hannunsa

Du sai ta kasa jan lokaci mai tsayi tana jan carbinta, tana ganawa ta daga hannunta a cikin zuciyarta ta yi adu'o'inta ta shafa sannan ta ajiye carbin ta mike ta dan ninka salayar ta bi wajen kur'anan nan da kallon sha'awa tana ji a zuciyarta inama ace nata ne duka? Kai da ta caba

Dan satar kallonsa ta yi, sai ta ga ashe ya yi baci, dan haka dan ta yi murmushi ta juya a hankali da niyar tafiarta wancen dakin ta kwonta

Kasa kasa ta ji ya furta " Baki ji ba? "

Har sai da ta dan tsaya ta juyo ta kale shi, gannin bai motsa a yanda ta barshi ba sai kawai ta juya ta ci gaba da tafiarta a hankali

Idannuwansa ya dan buda kadan ya ce" Najeeba idan kika fita ba zatai maki dadi ba "

Juyowa ta yi tana turo bakinta gaba tana dan magana kasa kasa , cewar haka kawai ashema ka san sunana malan

Shi dai kallon bakin nata kawai yake a yanda yake, sai kuma yanda ta tsaya masa wani kerere a tsaye a ka da yake mamaki

Dan buda idannuwan nasa ya yi ya sauke duban nasa a fuskarta, irin yanda ta turo bakinta da tsayuwar da ta masa kamar wata yar baby sai mutsu mutsu take da bakinta

Hannunsa na dama ya mika mata a hankali ya ce " Zo "

Sai da ta bi hannun da kallo , a ranta fadi take, kawai mutun sai fari uwa wani aljanni, irinsu ne kana ta kanka a gida kana faman girki da tsantsara masu kwaliya sun fita waje wasu matan na wawarsu, haka kawai kana ta kanka a jaza maka abinda ba shi ba, sai wani yanga da wani langwui salon ka kara tara matan, to dai matsalarka ce malan idan kana so tara million ma

A hankali ta dora hannunta saman nasa , tana kara shagwabe fuskar tata ita bata ki zuwa ba, ita bata yarda zata je har zuciyarta ba

A hankali ya janyota gaba dayanta jikinsa ya dorata saman jikinsa ya saka hannayen nasa ya bata kyakyawar runguma
Muryarsa sanyaye ya ce" yaya zaki gudu ki barni bayan kin ga matata ma cikin wani hali, nima ina cikin damuwar saka mai so na a wani hali? Duda na san ba so na kike ba aman idan kika zauna da ni zan rage zafi "

Bakinta dake daidai wuyansa ta turo sosai tana tabewa, a hankali ta ce" to ka yafe mata mana, ai na ga ba ita ta kashe maka mata ba, kuma ba ita ta so kashe maka mata ba, bayan wannan ai dan tana son ka ta aiwatar da hakan, kishinka take shi ya sa "

Idannuwansa dake lumshe ya dan kara lumshewa sakamakon abu biyu, gannin kamar maganarsa batai mata zafi ba, da irin hucin dake saukar masa a dokin wuyansa

Sai da ya jima tamkar ba zai yi magana ba sannan ya ce" zan duba maganarki, kafin na yafe mata zan kara aure "

A hankali take jin haushin magangannunsa, to a me wai ya dauketa ne? Ita ga wawa ko? Da dan zafi zafi ta ce " idan ka tashi ka auro farare tas tas tas bakakenma ka sake su SHAHEED "

Murmushi bayanane ya yi gannin a yanzun maganarsa kamar ta mata ciwo, dan haka ya ce" sai nake gani kamar kin ji haushi? "

Bakinta ta yatsina tana dan son tashi aman sai ya kara matseta a jikinsa hakan ya sa ta daina kiciniyar son tashin
Itama sai da ta jima tana tunani sannan ta ce" ba biya ba bege me ya kawo jin haushin maganar abokin zama ?"

"Haka ne kuma, aman ko ba komai zan duba shawararki zan kawo wata tsaleliyar fara, sai dai ni bana ajiye bayi a matsayin matan da zan ringa zagayawa, kema musulunci ai ya yi karfi yanzun ko " Shaheed ya fada yana mai kara rungumeta a jikinsa

Sai da ta datse lebenta na kasa a dan kausashe ta ce" sake ni! "

Kansa kawai ya dan girgiza mata bai sake tan ba bai kuma bata amsa ba

Huci ta furzar kafin ta ce " Allahn da ya sa nima ba ni nace ina son farin ba! "

Murmushi ya yi a bayane bai bata amsa ba, sai kawai ta ringa sauke ajiyar zuciya, sai da ta dan daga dubanta ta sauke a kan habarsa , gannin idannuwansa a rufe sai ta zabga masa harara harda murguda bakinta

Dan murmushi ya yi a hankali ya ce" Na yafe maki "

Ido ta zaro da mamakinsa, wani irin karfin gani ne da shi haka?, wai kuma me yasa ya cika son yi mata komai cikin sanyin lamari bayan shi din mutun ne mai zafi?

A hankali ya ce "BEEBAHHH?"

dagowa ta yi da sauri dan jin muryarsa a wani irin sanyaye sannan irin yanda ya ja sunnan sai ta ji da bambanci sosai kan yanda UMMU ta fada, nasa har wani irin yamyamyam ya sakata ji a jikinta, sam sai ta kasa amsawa kiransa sai wani zuru da ta yi tana kallon wuyansa domin daf take da wuyan nasa numfashinta na sauka a wuyan nasa

A hankali ya ce" BEEBAH ki janye hancinki daga wuyana, kin ga sai wani yannayi nake shiga kar na zo na kara kuma a ce ban kyauta ba "

Idannuwanta ta lumshe a hankali, tana mai jin yanda maganarsa ke sauka a cikin kunnayenta, sunna samun wani muhali mai tsafta a cikin kwakwaluwarta, kasancewarsu ba zafi ba ihu ba kausasa sai take jinsu wani bambarakwai harma ta kasa tuna waye mai furta su haka a sanyaye, a rashin sani ta dan matse masa wajen mararsa da hannunta na dama ke sama hakan ya saka shi rintse idannuwansa a hankali ya furta " Washhh zata kashe ni "

A dan tsorace ta dauke hannun nata, sannan ta yi gagawar janye jikinta daga irin mamukar da sukaiwa junna, cike da kunya gannin ya ki saka mata duwai ya mata wani damka ya sakata dam gyaran murya kasa kasa ta ce".......





.................🥳🥳🥳🥳🥳😎🥳🥳🥳🥳🥳🥳🥳





[31/03 à 22:01] Sadjida: 🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻


*Na*


*SAJIDA*


💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝

☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login