Showing 111001 words to 114000 words out of 228147 words
Chapter 38 - MAGE (Mai kwanciyar Daukar Rai) Book Complete Na Sajida complet.txt
da hannu bibiyu, bata taba tunanin ita Nadia zata tare a matsayin amaryar mai martaba, ita zata ga fuskar mai martaba, takan yi daria ta furta" Najee, ina kika shige, yau daukaka ta tardoni a gida ni zan zama matar abokin gabarki, kar ki damu kawata zan shirya ku!
Bangaren Anmy hankalinta ya so rabuwa biyu, sai dai mahaifiyar Najeeba ta kaleta ido cikin ido ta ce" idan har kika yarda shiriritar yarki ta saka maki damuwa to fa ta samu nasara a kanki, ki gane tana kara langwabewa du idan kin shigo ne, ki zo ki kula da baki ki barta ta gama shan karin ruwan, idan lokacin fitar da ita ya yi za'a fitar da ita koda a sume ne a jinginar da ita, ban taba gannin bataciyar ya irin yarku ba! Kun wani rikice dan tana abu nan Abihnta har ni yake fadawa magana wai ina ruwana da ita, han
Murmushi kawai Anmy ta yi, domin a lokacin da aka basu damar su shiga su duka su kara ganninta a jiya ne suka yi kicibis da Ummu, du daburcewa Abih ya yi sai neme nemen kys din mota yake a aljihun rigarsa har sai da Dayabu ya yi murmushi ya kama hannunsa ya ja shi, har ya gifta ta ya juyo ya ja tsaki kamar wani yaro ya ce" an ji kunya, me kuma ya maido ki nan? Ki koma mana wajen neman kudinki, ki barmin y'ata babu ruwanki da ita
*FADA* ta rikice, ta hautsine wajen ya dinke da jama'a, dogarai ne sun sha rawani daidai misali du sun bazu sunna bada wani irin tsaro sai sojojin da suka barbazu suma sunna bayar da tsaron
Tsaye yake a cen sama ta wajen window dinsa mai duhu wanda shi yana iya gannin na waje aman daga waje ba zaka iya hango shi ba
Bashi da riga a jikinsa, ya gama moysa jikinsa ne da wani dan tawul karami yana goge zufar jikinsa yana kallon du wasu shagulgulan dake kai kawo a cikin fadar
Hannayensa masu taurin gaske ya daga ya dan dora a jikin garun ya kara kurawa wajen ido
Tabas ya jima rabonsa da ya ga taro haka, ya tabata Anmy ta bada babar gudunmuwa dan tana aurar da y'a
Murmushi ya yi yana girgiza kansa ya juya cike da kadaita ya nufi bayi da kansa
Ya jima ciki yana wanka da dukan uzurinsa kafin ya fito
Agogo ya kaiwa duba, nan da awa daya da rabi za'a gabatar da daurin auren dan haka sai ya zarce wajen tarin kayansa ya buda ya tsaya yana kallo
Saka sababin kaya ba yau ya fara ba, sannan ba sai ana wani abin yake sakawa ba, sai dai na yau din a sabinma bugagu ne wa'inda suka amsa kiransu
Da hannunsa ya ciro su da sabon rawaninsu hade ya ciro duka ya ajiye gefen gadonsa
Zama ya yi ya dauki karamar wayarsa ya danna kira
Tana fara ringin aka daga ana mai aiko da salama da neman fara kirari
Da sauri ya furta" yi shiru, abinda nake so da ke ki saka a yiwa yan mata kamar goma kwaliya ya kasance an laya su a matsayin amaren nan da ake yi, ina so ku ringa gardamar ba zaku bayar da amarya ba,
Ina so ki saka mata simple shiri ki bata hijab da nikaf ta fara fita ta tsaya ki a cikin kwanar gidanku kafin ki sandi mutane ki fito
Akoy dan sahun da zai dauko ku ya kawo ku
Idan kun zo yau gidan ba'a hanna shiga ko fita, zaku samu hanyar shigowa
Idan kun shigo zan wakilta macen da zata sada ku da bangarenta sai ku gabatar da abinda zaku yi
Dan shiru ya yi yana sauke ajiyar zuciya kafin ya dago yar yatsarsa guda ya ce" ku kiyaye, rayuwarta ko nace rayuwarku baki daya ke cikin hadari, idan har kuka kuma falasa wani abin ko me ya biyo baya ku kuka da kanku
Yana gama fada ya datse kiran sannan ya dan dane lebensa na kasa
Kuma mikewa ya yi da tawul din dake jikinsa ya nufi wajen window din
Abubuwa da dama sun shiga idannuwansa, irin yanda ake waje waje ana kuskus daga inda yake ba zai fahimci komai ba sannan a yau ba zai fitar da droon ba har sai an fara hawa dokunna domin a yanzun ana cen ana hawan kaho ne ana ta zubda maza
Suturarsa ya ringa sakawa cikin adu'a da iya daukan wanka
Sai da ya saka abinda zai kara rufa asirinsa duda wandon shadar ba karami bane aman gwara a kara daurewa dan kar a ji kunya
A lokacin da ya dora babar rigar shi da kansa sai da ya tofawa kansa walahaula wala kuwata ila bilah domin dinkin ya dauke shi ya amshe shi sosai haka kuma kalar ta karbe shi sosai
Sai da ya saka farin yadi mai haske a fuskarsa mai shara shara kafin ya yiwa masu jiransa umarnin shigiwa dan gabatar da nadin rawanin da suka takanas dominsa
Su biyu ne, kwararu ne, aikinsu ne, nadin za'a hauda shi daidai yanda zai bada kalar tsuntsun da aka yi dinkin irin kalarsa wato Dawisu mai hasken fari kar kar kar sai dan kalar blue mai haske jefi jefi
Sosai suka gabatar da aikin nadin da ya dauki lokaci kusan minti talatin kafin su saka masa safa fara kar su saka masa takalmi kafa ciki shima farin ne kar kar mai kyan gaske domin fata ce akaiwa adon fari tas tas
Dawisu ya gama bayana a lokacin da suka miko masa sandar sarautarsa,
Sandar baka ce mai adon zeba daga sama
Sandar wata irin sanda ce mai shegen kyau ga tsada
Rike sandar da ya yi a hannunsa na dama a lokacin da ya mike tsaye ya kara masa wani irin cika da girma
Baki daya ya haske wajen har ya kasance su da kansu suka shiga kirarin dole domin kuwa wani yabon zaka yi shi ne a lokacin da kai kanka baka sani ba
Irin yanda karamar wayar da zai rike ta sha masa kai da ringin ya saka shi dubawa
Idannuwansa ya lumshe, bai san yaya aka yi suka cika takura ba , auntyn Nadia ce wace take kanwar mamanta uwa daya uba daya, da kansa ya amshi numberta bisa kwakwaran gargadin kar ta yarda wasu su san yana magana da ita sai Nadiar sai mamanta
Dagawa ya yi ya kara a kunnensa bai yi magana ba
Sai da ta kara sada kanta sosai sannan ta yi tambayar zuwa wani lokaci ne?
Idannuwansa ya daga ya kai wajen agogo, daurin auren a yanzu bai fi saura minti goma na, dan haka sai ya sada idannuwan nasa a hankali ya ce" bayan awa biyu da komawar *GUDGE MOCTAR*
Amsawa ta yi ya kashe wayarsa
Dubanta ta maida wajen yayarta da suka yi tsuru tsuru ita da Nadia sunna jiran amsar
Amsa ta basu dan haka suka shiga neman nikaf da bakin hijab domin kaf a cikin gidan babu ba mai sakawa!
Cike da kasaita ya ringa tafia
Yana fitowa dogaran dake laye a cikin katon falonsa suka kwashi wani irin kirari mai saka tsigar jiki tashi
Busa ce ta karade wajen irin ta sarakai hakan ya saka shi lumshe idannuwansa kafin ya bude ya sauke dubansa kan sarakai hudu da suka halarci taron da manya manyan mutanen da suka zo dan taya shi zaman wannan ranar
Da kansa da kuma idannuwansa ya yi anfani wajen gaisar da kowa ta hanyar dan sada kansa da kuma idannuwansa sai baban dogarin dake isar da sakonsa ya isar yana jinjina da hannayensa, sauran kuwa sai su kwashi kawo gaisuwa sunna fadin Sarkin garin maradi ya amsa gaisuwar *MAI WUKAR YANKA*, yana yiwa *GURNANIN ZAKI* fatan alkhairi
A haka dai har suka kara cinye wasu lokutan masu mahinmanci kafin a fita baki daya a bijiman dawakan dake dauke kwaliya ta mamaki da wata bazara a gefe dogarai majiya karfi suna ririke da ita
Sai da ya taka hannun Amintacensa kafin ya dora kafarsa daya a abin dokin sannan ya hau da kyau indo dogarai suka kare hawan nasa
Sai da ya zauna ya rike sorsin dokin sannan da kafarsa ya dan daki gefe da gefen dokin a hankali, nan fa dokin ya shiga wata tafiar kasaita domin yanda yake tafe fari kar da shi ga irin yanda yake daga wutsiyarsa mai dauke da yalwatacen gashi itama tana sama tana yawo irin ya koshin nan ya gaji da koshi kamar ya fashe tafiarsa ta koma ta kasaita
Haka aka layu anna ta rangada buda ga busa ga yan rakiya har suka fice daga fadar wada ba wanda bai fito gannin kwaliyar sarki da fitar sarki ba
Yayar Zinaria ta juyo tana gyada kanta ta ce" a gaskiya, da kamar wuya SULTAN SHAHEED ya iya zama da mace daya, koda bai je nema ba za'a zo neman alfarmar aurensa
Zinaria, ki duba ki ga yanda baki daya ya haske wajen cen, da ace nice ke, zan yi kwaliya irin tasa na bashi goyon bayan da zai saka ko wa ya karo sai dai ta biyo bayana! To ke Zinaria yaya kike tunanin mutun har haka ya zauna da ke daya? Kin yarda da kanki har haka ne? Wace irin kula kike bashi wace zata saka shi haka? Kar ki manta Aba da Abihnsa suka maku auren hadi, kar ki manta a zamanin nan mutun ko dan rufin asiri yake da shi shikenan ya kama hange hange bare wannan? Zinaria mijinki sarki ne, kuma mai kudi ne....yaya zaki kasa yiwa kanki adalci ki ringa summa dan zai yi aure?
Mahaifiyarsu ce ta daka mata wata irin tsawa ta hanyar fadin" kilishi anya kuwa ke jinni na ce? Baki san mulkinsa da dukiyarsan ne ya saka lale lale zamu tanadesu dan kanmu da y'ayanmu ba? Baban bakin cikina ace har yanzu babu wani abu da take da shi da zan iya fara dora rai a kansa, kilishi, ko ki min shiru, ko na hautsina kwonciyar hankalinki sakarai ke da kika ne kike yiwa kishiya bauta ai ke kika gani!
Shiru ta yi ta koma ta zauna domin ba zata furta wani abin ba kuma cibi ya zama kari, gani take da wannan zaman da suke sunna sake sake da kiraye kiraye da tsare tsare, da mikewa suka yi suka saka akai mata shiri irin na wanda ake yi, suka tarbi amaren nan da kansu da sai sun fi girgiza mutane, aman sun tare a nan sun hadu sunna ta abu kamar wasu jahilai
Ita kam gaskiya ko yanzu zata mike ne ta je wajen kiahiyarta domin tare suka zo da mijinsu sarkin tsatsunburun ne su shirya a tarbi amare da su, ita kam Alhamdulilah tana zaune da kishiyarta lafia, ita ta je ta sameta a gidanta da y'ayanta , matar tana da hali na datako hakan ya saka cikin nutsuwa suka hada kawunnansu suke zaune kalau, ko irin asiran da Gimbiya ke bata ta zuba a abinci dan ta raba su ita kam bata taba anfani da shi ba, tana amsa dan su zauna kalau da mahaifiyarta aman ko nisa bata yi take zubarwa ya bi iska domin ita dai bata dauki duniyar da zafi ba, kuma iliminta ya fi gaban wannan gaskiya, ta gane cewar idan ba kanka ka sauke, ka nemi zaman lafia da kowa ba to da dan da ka haifa ma sai dai ya bika dan dole!
Ana gama salar azahar aka gabatar da daurin aure
Auren da aka fara daurawa shine auren da ya saka zukata da yawa zabura da jin tamkar an dika masu guduma a kansu
A lokacin da aka furta kalmar sunnan nan wato *NAJEEBA MUTALAB* sosai zukata suka rikice, da yawa kuwa suka hangame baki cike da mamaki
HUZAIFA bai iya tsayawa ya ji sauran daurin auren ba ya fita daga cikin tanfatsetsen masalacin yana jin tamkar numfashinsa zai bar gangar jikinsa
Kuka ya fashe da shi a cikin abokansa yana son sai sun barshi ya doka kansa da madubin motarsa
Yana kukan yake fadin" ta cuce ni, ashe dama bata so na? Ashe dama mai gida zata aura shine ta yaudare ni? Dama ashe aurenta za'a daura na dinka sabuwar shada na zo ni ga sirikin sarki? Dama ashe aurenta za'a daura na zo nan? Nadiama ta cuce ni, ashe ta san haka ne ta barni nake ta fama da soyayar Najeeba a zuciyata?
Hannun abokinsa latif ya rike ya ce" Abdul latif, ka taimaka ka kaini wajen Nadia, ka kaini na ji me na mata a duniya? Walahi du rashin jin maganata na ajiye dan kar Najeeba ta kubuce min, ina nan ina ta neman inda zan ganta kulun a kofar shagonta nake wuni dan na sameta ta yi hakuri da abinda na mata, ni ban yi dan bata ranta ba
Ku shaida ne nan wayarta a hannuna na ringa korar du wani mai kiranta dan bana so idan na zo malakarta wani ya zame min matsala
Kune shaida summar da ni aka yi kan wayarta ni kaina ban san mutumen ba aman shine yau zan ga daurin aurenta?
Shi dai Abdul Latif kama shi ya yi domin kwarai ya san yana son Najeeba da gaske, dan haka bai tsaya yi masa shakiyanci ba ya taimaka masa suka shige mota
Yana shirin tayar da motar docter ya fito yana langwui
Tsayawa ya yi ya dafe habarsa ya furta" kan uba, lale na yarda cewar *MAGE, MAI KWONCIYAR DAUKAN RAI CE NAJEEBA* da ta tashi kawo mana dukan sai ta kawo da wajen da ko mun sha kwaya ba zamu tunkara da salon iskanci ba
Soja ne ya fito har ya zarta ya dawo yana kallon Docter
Daria ce ta kubce masa kafin ya girgiza kansa ya yi gaba, lale ya san yarinyar nan ta fi karfinsa kuma ya yarda Allah ne ya kareta domin matar manya ce, shi irin ya dan yi hira da itama bai samu ba sai dai daga nesa
Da yawa sun ji jiki ciki harda likitan zuciyarta, da ambasador
Ambasador kansa ya sada a cikin masalaci idannuwansa sukai masa wani irin jajajir gashi kuma shi a cikin masalacin yake ba a balbalin masalacin ba bare ya mike ya fita, sai ya zama a lokacin da ya dago dubansa sai da gabansa ya fadi domin yana kallon sarki sai baki daya ya raina kansa, shima shaheed din shi ya kalla kafin ya cire kansa yana sauraron haramar daurin aurensa da Nadia kasan zuciyarsa kuwa haka kawai ta hanna masa sakat, gani yake du inda ya kai dubansa ba zai rasa samarin yarinyar ba, kai da ba dan an masa kwakwaran bincike kan kawar nan tata ba, da ba zai aureta ba, an fada masa cewar yarinyar girman kanta ya saka samari da yawa ke tsoron tunkararta, har fadi ake cewar tana da nauyin jinni, sosai iyayenta ke faman ta tsayar da miji domin kawancen nasu da Najeeba shekara uku ta bata, Nadia na dauke da shekaru ashirin da hudu tana cikin ta da biyar, ita kuwa fitsarariyar na dauke da shekaru ashirin da daya tana cikin da biyu
Idan ya kalli Ambasador ba abinda ke fado masa irin maganar.....ina so na ganki, na zo maki da dukan abubuwan da kika ce kina so na tsarabarki, ina so na ganki ko zaki bani nutsuwa!
Lalle uwa uwa ce
Bai yarda da iyaye a kasar musulmai sun isa da y'ayansu ba sai a kansa
Gashi dai ya kai inda ya kai Alhmdulilah aman kuma gashi a karo na biyu an daura masa aure da zabin da ba nasa ba
Idannuwansa ya kuma lumshewa ya maida hankalinsa wajen da ake kara raraba su goro ne ba kadan ba mutane sunna ta amsa a bokitai anna ta fita da su kafin a shiga haramar wani daurin auren, ga Dayabi, ga ABIH, ga sarkin agadez, ga yarima a kusa da shi sai ya shiga salatin annabi da fatan a watse lafia..........
Hi mutanen arziki,
Zan yi posting na biyu yanzu, idan kuka fitar da shi za'a janye dokar bibiyu🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣
[31/03 à 21:42] Sadjida: 🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
37
Yana langwui ya shige dakin da Nadia ke zaune da kawayenta da auntynta da kuma daidaikun yan uwanta, dakin mai girma ne hakan ya sa kowa ke sha'aninsa an fi raja'a wajen daukan hotunna Nadia ta sha kyau domin aida ce ta zo ta mata mak'up har gida tana shaida mata cewar Najeeba bata fita kwana biyu yayarta ke fita saloon aman da ta fito zata shaida mata, ita kuwa ta dauki niyar ai Sai an nemo mata Najeeba ta tsantsara mata firgitaciyar kwaliyar da zata haukata mata sarkinta
A lokacin tana shirin shan wasu magungunnan hausa ne da auntynta ta dama mata da nono mai tsami, sosai fa Nadia ke amsar tsumi daga wajen iyayenta domin suma wayayun mata ne duda ba'ai mata gyaran jiki ba sun bar hakan a zuwan sai ta tare dan lokaci ya kure yawon neme nemen abubuwansu ya ishe su
Yana zuwa ya zube , mamanta da ta ga yannayinsa ta tsame daga mutane ta yo dakin
Auntynta kuwa tun da ya fashe da kuka ta shiga korar mutane cike da tashin hankali tana kallonsa
Su hudu suka yi saura sai tambayarsa ba'asin kukansa ake
Yana dago kai cike da muryar kuka ya ce" ashe Nadia ta san haka ta barni na yi ta hauka a kan kawarta? Ashe ta san wacece kishiyarta ta kyaleni na ringa barnar zuciyata da dukiyata ina hauka?
Nadia ta ringa kallonsa tana son ta ji abinda yake son fadi
Sai da ya share hawayensa ya ce" Allah ya isa tsakanina da ke Nadia, shine kika kyale ni ina haukan Najeeba ashe da ita za'a daura auren Sultan?
Nadia dake ta kallonsa ta yi wani dan tsam kafin ta taso da sauri