Showing 177001 words to 180000 words out of 228147 words
Chapter 60 - MAGE (Mai kwanciyar Daukar Rai) Book Complete Na Sajida complet.txt
irin yanda ta ringa kokowar da shiSHAHEED sai abin ya fara bashi nishadi, da gangan ya ringa biye mata har sai ya barta ta tashi sai ya mayar da ita baki daya, ita kuwa hakan ke kara tsoratata sai ta kuma fashewa da kuka du ta yaye tawul din garin kokowar kwatar kai
Zaunar da ita ya yi dangalgal saman bed din ya zamanta sunna kallon junna sai sauke ajiyar zuciya take a tsorace tana masa wani kallon da bai san me yasa yake saka masa bugun zuciya ba
A hankali ya kure dubanta, har ya dangana da lebunnanta
Idannuwansa ya lumshe ya damki lebunnanta, iya su ya ringa yi masu wani irin horo mai zafin gaske, mai zuwa da zafi zafi wanda ya sakata baki daya zaro ido jikinta ya kara daukan bari, hannayenta na ture shi tun karfi aman abin ya gagara domin sai ta kula kamar idan ta tura shin kara mane mata yake a jikinta
Tun tana kukan zuci har hawaye ya kama zarya a kan fuskarta, wata irin mugunta ce yake mata iya lebunnan bakinta da mamanta aman hakan ya sakata soma fita hayacinta domin kuwa irin yanda kan mamanta ke mata zogi kamar zata mace take ji hakan ya sa daga ya dan cika mata lebe sai ta aniya hada shi da Allah da kuka da komai kan ba zata kuma ba, sai dai baya bari ta idasa magiyar zai kuma damkarta
Sam bai nemi hanyar da yake yiwa tanadi ba, hasalima du idan tawul din ya yaye har wajen yakan janyoshi ya rufe ne, aman hannayensa da hakoransa sun yi mata damkar da shi da kansa sai da ta dawo bashi tausayi
Baban tashin hankalinta tun a haka ta gama ganewa bambancin tsagerancinsu ina ga ya kai inda take? Sai kawai ta bi ta idasa sarewa, kwarai bai mata ihu ko duka kp hargowar da zai tada mata jama'a ba, aman a iya hakan ta ringa dana sannin zuwa wannan waje
Kansa ya dora a dokin wuyanta yana sauraron yanda take ta shasheka da ajiyar zuciya
Idannuwansa ya rintse da karfin tsiya, domin kuwa a yanda ransa ke bace du irin yanda ya tayarwa da kansa hankali ba zai yarda ya zo mata a haka ba, dan kuwa ya tabata zai yi anfani da damar ne dan huce haushinta da yake ji, hakan ya sa ya mike a hankali ya saketa ya nufi bayi yana ta hada hanya tamkar zai kife a kasa
Baki daya ta kasa tashin da take son yi, dan kuwa gaba daya hannayenta da jikinta ne sukai mata nauyi ta rasa dalili, sai hawayen da take idannuwanta lumshe dan ko tawul din ta ja ta rufe kirjinta ta kasa ga ajiyar zuciya wata na korar wata
Tsayuwa ya yi kasan shower ya sada kansa
Lebensa ya yi masa jajajir sai dan rawa yake masa sanadiyar irin halin da yake ciki
Hannunsa na dama ne ya jimke ya kai duka jikin garun nan yana kara taune leben nasa dan so yake ruwan nan mai sanyi dake zubar masa ya bashi yar nutsuwa ko yayane
" *ALLAH NE YA TSARE MIN ITA* " ya furta a hankali muryarsa a cinkushe,
" *ya Allah ka kara tsare min ita* " ya idasa fada a saman labansa
Baki daya mararsa ce ta kama ciwo, cikinsa ya aniya kulewa waje guda ya kasa kwakwaran motsi
Bai saba da irin wannan matsalar har haka ba, idan ba dan ita ba ba zai taba sannin wannan maysalar ba, dan jarabar idannuwansa du ranar da ya ganta sai ya kurewa kallonta, haka zai zo ya yi ta fama
Ajiyar zuciyar da ya ringa saukewa ce ta fahimtar da shi idan fa ya yi da wasa yana iya kwonciya rashin lafia
Rausar zuciyarsa ya yi ta yi kan tinasar da shi abinda yake yawan fadawa kansa dan ya rarashi kansa koda a xen baya
Sai da ya tabatar da ya rage bacin ran sannan ya juya a hankali ya fito mata hakansa
Bata ga fitowarsa ba, bata san da ya nufota ba, sai ji da ta yi an kuma fara taba mata jikinta
Sai dai a wannan karron a sanyaye ake taba mata jikin, ga sanyin ruwan dake haduwa da fatar jikinta, ga ji da take kamar za'a cinyeta ya sakata kasa buda idannuwanta sai barkewa da ta yi da wani sangartacen kuka
Hancinsa yake ta kai kawo a wajen jigidar nan mai sansanyan kanshin sirri
Kasancewar a yanzu yana mai binta a hankali, yana kokarin gannin ya baiwa komai hakinsa duda kasantuwarsa a yannayi na bacin rai da mugun bukatuwa da ita aman sai ya ringa bin du wajen da ya yiwa muguwar damka a hankali yana mai hura wajen da lalabashi
Tsoronta, da zafin da guraren ke mata ya hanna mata karbar sakonsa yanda ya dace, duda haka nan da nan lamari ya kwace a jikinta domin kuwa a shirye yake da karbar sakon ko yayane
Lokaci daya komai ya kwonkwonce masa, lema lemar da ya ringa ji ya saka shi kai dubansa, a fili ya furta" *Wayo ALLAHNA*, a hankali yannayinsa na son ya bita a sanyaye ya yi masa kaura wanda shi kansa bai san hakan ya bar kwakwaluwarsa da aikinsa ba, a yauma ya zo mata, zuwan da ya kusan sumar da su baki daya, ita kam ta gama sarewa duniya da abinda ke cikinta, ta yi dana sannin karbar abubuwan da auty Zahrau ke dudura mata , sannan ta yi dana sannin guje masa na kwanaki hudu domin kuwa a kalaman dake dan kwace masa idan ya juya kai ya kuma juyar da kansa zai ce" Me ya sa kikai nesa da ni har tsayin lokaci?"
Wasa wasa cikinta ba komai, ta karbi kari mai sanya juwa idan ba'a karya ba, ta amshi bulaliyar da ta gwamace duka da ita, ta amshi wani irin horon da ta gama sakawa zuciyarta ba zata anfanu ba daga nan, ta kasa mugayen kalaman da ta yi a wancen ranar domin maganar da ta fi yi shine neman ya barta kar ya tsagata gida biyu, ya barta kar ta mutu, ya sasauta mata ba zata iya ba
Har sai da ya kasance ya yi niya dan kansa sannan ya saki kansa ya samu nutsuwa
Wata irin murya cen kasa mai nuni da mai dauke da ita na tsikin matsanancin hali Najeeba ta ja numfashinta da karshi sannan a wahalce ta ce" da ka halakani gwara ka sawake min SHAHEED, aikinka na nuni da burinka ka kasarani bayan nima BA SON KA NAKE BA"
Shi kam bai iya bata amsa ba, hasalima gefe ya koma bayan ya yi irin kwonciyar da aka koyar dan gudun komawar lamari jikinsu, sai ya samu kansa da tsurawa fuskarta ido, kallonta kawai yake yana jin tsigar jikinsa na kuma tashi, baki daya lamura na son kara bijiro masa...............
Farin ciki ne madaukaki ya dira a zuciyar ABIH a lokacin da ya ji wannan sako na UMMU, gashi dai a zaune so yake ya zabura ya je ya ganta ido da ido ta shaida masa da bakinsa aman ya kasa domin yaransa sun zagaye shi sai neman afuwar fadan da suka yi suke
Da wani murmushi ya shafi gefen kumatunsu ya ce" kun ga, ku je dakunnanku kun ji? Yanda ta yi da mu maman naku nima idan harda ni a hukuncin ba laifi zan karba ne"
AMMI dai daria kawai take sosai, dan Walahi irin yanda yayan nata ya yin ne ya bata daria, sai kawai take hango da cen,
Kiran da Zahrau ta yi a wayar AMMI ta shaida mata ta isa ne tana falonta yanzu haka ya sakata sakin murmushi tana fatan alkhairi sannan ta shaida mata kayanta zasu zo Agadez gobe in sha Allah za'a kai a auna mata su a tura su
Shi dai Abih kara buda idannuwansa kawai yake dan gannin UMMU wace da gangan ta yi zamanta a daki ta rufe tun da ta ji ya cewa AMMI gashi nan zuwa
......................
"Haba Nadia, yaya kike son ki saka ni asarar kudina, ki saka ni asarar likacina da tunanina ta hanyar mayar da kanki wawa kamar ba ke ba? Na ji na sanni mijin Najeeba kika aura wanda yake mijinki kema a yanzun sai me? Ina ce aure kika ce, kuma auren nan ba wai kin san za'a yi shi bane kika yarda, kuma ba tashi kika yi kika je kika auri mijin kawarki ba dan cin amana aman shine sai ki ringa irin abinnan kamar wata sokuwa? Me kike so yanzun? Da kike baya baya bakya anfani da koyarwar da akai maki dan mijinki ya san da ke so kike ki zama ta karshe a cikin matayensa? Kin san dai ba saki idan har ba kama ki aka yi da laifin zuna ko kisan kai ba, a kan me zaki ringa irin wannan abin?" Mahaifiyar Nadia ta karasa mata magana ta waya tana yi kamar ta shiga cikin wayar ta ganta gata ga ita
Nadia dake cikin hali na tsoro, tun dazu da safe ta budi muryarta dake rawa rawa ta ce" Mama, ba wannan ne damuwata ba, ina tsoron a je na kawo kaina gidan halaka domin kuwa a dazu da safe na ga abinda bai dace a ce na gani ba, baban tashin hankalina zan je na samu sarki da maganar ne ko zan yi shiru ne? Wanda na gannin ya ganni ne? Idan ya ganni me zai min? Mama na shiga uku na lalace ana neman rayuwar sarkina ido rufe na je bangarensa na yi na yi wajen ya ki buduwa ban san dalili ba, ina tsoron wani abin ya same shi ko ni ya sameni, una tsoron ace wanda na kama shima ya kama ni? Magangannun da na ji dole sarkina ya sani ya kuma ji daga inda na ji su
Hankalin mahaifiyarta ne ta ji ya tashi, dan kuwa a muryar yar tata kana iya gannin tsantsan tsoro da tashin hankali da kaka naka yi, da sauri ta mike tsaye tana kallon agogo ta ce"
Kuka ce na baku shi a haka ko? To gashi☹️ ni dai oh sunna sai ya kare a bakin maman abdul,
[31/03 à 21:58] Sadjida: 🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
55
Baki daya a rikice mahaifiyarta ta ce" kina ji na? Kar ki kashe wayarki, ki barta a haka Nadia gani nan zuwa"
Nadia ta ce a sanyaye" mama, idan kin zo zaki samu shigowa ne? Ina tsoron ki rasa hanyar bi idan har magautan Sultan sun san da na san abinda ke faruwa, mama ina jin tsoro sosai"
Ai kuwa hakan ya sa ta kara rikita mamanta, da gudu gudu ta fito da kys din motarta da wata wayar tana kiran number mijinta haka kuma dayar wayar bata kashe lasge ba, sannan sai maimaitawa Nadia take cewar kar ta kashe kar ta kashe
Kira kan kira a irin wannan yamaci aman ta kasa samun mijinta, hakan ya sa ta nufi ma'aikatarsa duda bata da tabacin samunsa
Sha'ani da waya, a lokacin da ta kusa karasawa kampanin wayar suka shiga shaida mata kudinta sun kare bai fi yan second a yanke layin ba, hakan kuma ya yi daidai da lokacin da Nadia ta zabura hankali tashe ta shiga furta" innalilahi wa'ina ilaihi raj'une, muryarta sama sama, wanda hakan ya saka mahaifiyarta maimakun ta take birki kusan office din mijinta sai ta take accelerator motar ta je ta daki abin dake kafe da sunnan mijinta goshinta ya daki sitoyarin motar ta koma ta kuma dakar kujerar
Goshinta ne ya fashe a lokacin ne kuma mutane du suka taso a guje ana ta fadin Subahannalah, ciki kuwa harda mijinta baban juju datijon da ya rike datijantakarsa
Gabansa ne ya fadi gannin motar matarsa, uwa uba kafarta da ta fitar waje tana son karasa fitowa
hankali tashe ya nufeta yana matsa mutanen dake son taimaka mata ta fito
A rude yake tambayarta lafia, bata ji ciwo ba, me je faruwa ta fito haka daga ita sai dan kwali da doguwar rigar shan iska?
A rikicen itama ta kama hannunsa, ido rufe fadi take" Nadia, Nadia, Nadia ce sun kashe min ita, Nadiata ta mutu, shikenan sun kashe min ita, dama tun da aka ce min auren gidan nan ba na Nadiata bane na nuna ta hakura, aman tsabar son sarauta da sarkin nan ya saka ta nuna ta ji ta gani, shikenan sun kashe ta"
Gannin kamar bata cikin hayacinta ya saka mijinta kama damatsunnan hannayenta da hannayensa bibiyu ya shiga jijigata ya ce" ke Hawau ki nutsu, me kike son fada min haka? Waye ya kashe Nadiar?"
Wani irin kuka take, ta shiga labarta masa abinda Nadia ta fada sannan tana ta nuna hanyar da ya dace a bi dan zuwa gidan Sarki, fadi take" sun kashe min ita "
Shi kansa hankalinsa ne ya ji ya tashi, nan da nan ya fara jin zufa na neman karyo masa, rabonsa da barin jiki irin wannan har ya manta, da sauri ya koma ciki, iya wayarsa da kys din motarsa ya dauko ya bar yarensa a ciki ya fito da wani irin sauri
Budewa sukai suka shiga, ya harba motar bakin titi yana yi yana gwada kiran Nadiar, sai dai tana shiga aman ba'a daga ba
Gani yake kamar an ninka nisan wajen , du irin yanda yake sheka gudu kuwa sai yake gannin ya kasa karasawa, sau uku yana gwada kiran Shahees sai ya yi gagawar kashewa domin dai Shaheed ba mutumen zuben da zai iya dirowa kai tsaye haka bane, hakan ya saka shi ajiye wayar a lokacin da suka karaso gate na farko mai dauke da manyan dogarai
Ai kuwa duda sun kasance sirikan gidan sai aka tsatsare su da tambayoyin da suka kara rikita mahaifiyarta
So take ta furta an kashe mata y'a, sai dai mijin ya tatareta ya hanna mata magana, karshema sai ya nuna sarki ne ya basu damar zuwa
Gannin irin kukan da Maman Nadia take ya saka suka nemi layin sarki wanda suke samunsa a kowani lokaci dan su ji daga bakinsa
A lokacin ya gama gasa Najeeba ya dawo da ita saman bed din ya fito ya ja ya tsaya dan ya afka tunanin ta yanda za'ai ya sama mata tea mai zafi wayarsa ta shiga kuka wace take a kafe a falonsa wace dogaran kofa baba ke kiransa da ita ne
Sai da ta katse aka kuma kira sannan ya karasa ya daga muryarsa a sanyaye ya amsa salamar da sarkin kofa ya yi masa a risine sannan ya shiga kora masa bayani cike da ladabi da biyaya da sada kai
Jim ya yi cike da mamakin jin mahaifan matarsa ne suka zo, mahaifiyarta na kuka , mahaifinta ke tukawa sannan sun yi zasu hadu da shi
Dan gyaran murya ya yi da fadin a basu damar tsalake get din
Ajiye wayarsa ya yi ya koma dakin
Da sauri ta mayar da idannuwanta ta rintse da karfi sannan ta yi lamo tamkar wace ta fara baci
A hankali ya cenza tufafin jikinsa zuwa manyan kaya kamar yanda ya saka ko gajiya baya yi, sannan ya yi simple rawani ba mai girman nan ba sai dai ya rufe har hancinsa kamar yanda ya saba sai idannuwansa kawai ake gani
Juyowa ya yi ya sauke dubansa a kanta, gannin fatar idannuwanta na motsi ya saka shi dan sakin murmushi a boye sannan ya shiga takawa har gaban gadon ya ja ya tsaya
Jin shiru shiru ba motsin kimtsawa sai ta buda idannuwanta
Ai kuwa da wani irin sauri ta mayar ta rufe har tana tura bakinta
A hankali ya ce" shine zaki ringa kallona ina saka kaya ko baki koshi na?"
Da sauri ta kuma buda idannuwanta, sai dai wannan karron ba kallonsa ta yi ba, gefe guda take kallo a tsorace take girgiza masa kanta, muryarta na rawa rawa ta ce" wajen AMMI nake son zuwa, ka ga yama ta yi gashi bani da kaya a nan "
Bakinsa ya tabe ya dan daga kafadunsa sannan ya juya a hankali ya kama hanyar ficewa
Da sauri ta so yinkurawa ta tashi, sai dai bata idasa hakan ba ta koma da wani irin saurin tana sakin yar kara tana rufe idannuwanta, du irin yanda ya gasata tamkar masa ya juyata ciki da bai bai hannata jin kamar zata mutu dan azaba ba, bata taba sannin wannan mutumen *MAGE* ne ba sai yau, da dariya da shafa da laluma ya yi mata damkar da zai iya halakata
Ba zata iya yarda ya tafiarsa ya barta a wajen nan sannan ya dawo ya sameta ya idasa halakata a daren nan kwaya daya da ya yi mata saura na amarci, a gaskiya ta daina mamakin irin ihun da Nadia ta ringa yi, sannan ta ji takaicin Zinaria dake kishi da wannan abin, wahalar? Tashin hankalin? Azabar? Kai gaskiya bariki hauka ne, a haka yan bariki ke rayuwa da maza kala daban daban? Wani daidai su wani ya girme masu, a haka su kamu da cutar kaikayo da sauransu (Allah ka shirye mi, ka rufa mana asiri, ka shiryi zuri'armu , ba dan halayanmu ba, ba dan wata ibadarmu ba, Alfarmar fiyayen halita da alkur'ani, ka raba mu da zina koda ta ido ce, ko wace iri ce), ita bata ga abinda zata yiwa kishi ba in dai ba dan dan kyan nasa da dan kudin nasa da dan farin nasa ba, to meye abin kishin? An ce mata shi sukewa kishi, ashe kuwa mata basu san ciwon kansu ba? Ita kam gaskiya ya fi karfinta, gaskiya sam ya fi karfinta...
A hankali ta idasa saukowa ta shiga bin bango bayan ta idasa zuge zif dinta ta rufe bayanta da kyau
Zama ta yi waje guda ta ringa sauke ajiyar hutawa,