Showing 183001 words to 186000 words out of 228147 words
Chapter 62 - MAGE (Mai kwanciyar Daukar Rai) Book Complete Na Sajida complet.txt
kalleta, hakama dukan mutanen wajen,, a takure a birkice , a wahalce ya ce" Shin na kama sunna a furucina ne a nan? "
Gannin ta sada kai baki daya jikinta ya kwashi rawa sai kawai ya mike tsaye, ransa bace ya shiga kai kawo
Juyowa ya yi murya a kausashe ya ce"
😁
[31/03 à 22:00] Sadjida: 🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
56
Juyowa ya yi murya a kausashe ya ce" shin kin aikata abinda zai sakani a cikin halin tashin hankali, kunya, matsanancin bacin rai? "
Kuma dago dubanta ta yi, baki daya jikinta bari yake ta rasa ina zata kalla, gani take ko'ina na dakin ya zama idannuwa ne, baki daya ta ringa gannin tamkar an tsatsarata a gaban alkali ne, duda kasancewarsa miju a gareta wanda ta yi rayuwar shekara da shekaru da shi aman sai ta tsinci kanta da kasa kallonsa sai tsabar tsoronsa da ya rufeta ta shiga barin jiki baki daya
Kai ya dan juya a hankali ya juyo dubansa kanta a lokacin da ya rage tsayinsa
Da dan karfi, zuwa lokacin muryarsa ta fara amayar da tsarin dake cikin zuciyarsa, tamkar zai hadiyeta danya dan bacin rai ya ce" Zaki budi baki ki bani amsa ko sai na aiwatar da abinda zai tayar da hankalin kowa a nan? "
Da sauri AMMI ta dora hannunta na dama ta saman kan NAJEEBA da ta cusa kanta cikin jikinta sakamakon irin yanda amon muryarsa ya yi mata rashin dadi a cikin kunnayenta
AMMI na shirin yin magana suka ringa jin maganar Nadia a firgice sannan muryarta a shake, sai ta shiga dan harbe harbe irin zata tare wani abin sannan ta kwala razananen ihun da ya saka baki daya akayi kanta
Ido rufe take fadin" kar ya sare ni, ka dauke min shi zai sare ni, walahi ba wanda zan fadawa, tsoron maciji nake ka kama shi yana lauye min kafata innalilahi wa'ina ilaihi raj'une wayo Allahna, wayo zai kashe ni "
A rikice mamanta ke ta girgiza hannunta dake cikin nata tana kama sunnanta sai dai kamar bata san ana yi ba
Da sauri ya duko da wani abu a cikin kofin glass da ya jika ya dan yi gyaran murya hakan ya sa UMMU bashi damar kama kanta
Bakinta ya gumtse da hannunsa sannan ya dura mata abin nan ta hancinta hakan ya saka baki dayanta ta yi wani irin tasowa a gigice sannan ta koma ta zube ta shiga amai ta hanci ta baki
Lokaci daya kuma idannuwanta suka bude jajajir da su tana ta zubar da hawayen wahala baki daya jikinta rawa yake tana bin dakin da mutanen dake wajen da kallo
Wani irin kuka ne Zinaria ta fashe da shi gannin Nadia ta tashi,
Ba wanda ya kula domin Nadiar du aka fi baiwa hankali wace gaba daya jikinta na rawa sannan ba karfi ta shiga fadin" Ban fada ba ko? Bai bari ya sare ni ba ko? Ba zan tona asirin ba kar ya kashe ni dan Allah "
Najeeba dake kallonta tana jin hawaye na ziraro mata daga gurbin idannuwanta zuciyarta cike da tausayinta, ta san za'a rina ne irin tsoron NADIA bare wannan abin ita kanta ta tsorata, ba zata manta ranar da ta ganshi yana ta damukar maciji ba, sai kawai ta shiga tsoron ko dai shima macijin ne?
Sai da ya yi iya yinsa sannan ya dan sasauta muryarsa ya shiga kiran sunnanta
Kanta take girgizawa tana maimaita ba zata fada masa ba
Mahaifiyarta ce ta kama hannunta ta rike a cikin nata da kyau ta ce" Nadia, kale ni, na zo, na zo fa, ba na fada maki zan zo ba? Kin ganni ni ce, fada min meye? Me kika gani, me ake fada? Idan har kika ci gaba da boyewa kin san da sannin ba barinki zai yi ba, domin kuwa ba zai taba yarda cewar kin rufe masa asirinsa ne, zai dauka cewar kina son tona masa a kowani irin lokaci, ki sani da ba dan Allah ya yi kina da sauran numfashi ba da yanzun an jima da goge babinki a duniya, ki sani kafin ke an kashe wata, idan kuma kikai shiru kema zaki bita, Nadia koda kuwa Allah ya yi wannan shi nr hanyar da zaki mutu kin fi so ki mutu ba tare da kin fadi abinnan ba? Bale da izinin Allah an kare, ba wanda zai kuma taba ki, ki buda idannuwanki ga mijinki, ga mahaifiyarsa, ga mahaifinki, ga yan uwansa da iyayensa , ki fadi koma menene"
Nadia ta dora kanta saman cinyar mahaifiyarta ta rintse idannuwanta, ta ce" Amintace ne, da kuma wannan mai rike katuwar bulala kusa da Sultan idan an zo shara'a, su ne suke zance, shi wancen ya ce shi dai baya cikin maganar kisa, abinda yake so kamar yanda aka hana masa jin dadin aure shima ya wayi gari Sultan baya iya jin dadin aure..........
Sai ta fashe da matsanancin kuka ta dora da fadin", shine Amintace ya ce" kamar yanda ya katse masa dukan farin ciki, ya dawo ya dauke shi a matsayin dogari ya ajiye komai nasa na farin ciki, to lalle shima sai ya kai ga ransa, kafin nan sai ya cikawa Gimbiya burinta na son raba shi da kowace mace ko ta halin kaka sannan ya kashe ya kashe Sultan"
Wata irin faduwar gaba NAJEEBA ta ji, har ta yi gagawar kallon SHAHEED dake tsugune kusa da Nadiar yana kallonta tamkar TV
Da sauri Zinaria ta sauko kasa hannayenta saman kanta ta ce" Na san a duniya idan akoy abinda na fi tsana shine mijina ya rabi wata macen, burina koma wacece ta bar min mijina koda kuwa mutuwa zata yi, aman ban taba gigin kashe kowa ba, ba ni nake kashe masa mata ba, ban taba zuwa dan kashewar ba, na san bakina na furta kalamai aman ban taba gigin kashewa ba, kuma haduwar da nake yi da shi ba wani abu bane sai taimakon da yake kawo min ba dare ba rana cewar na aikata ko na zubawa Sultan a abinci hakan zai saka ya tsani matan da ya aura, ni ban san maganar maciji ba, banma san cewar wai har ta kai shi ga haka, tabas ina da matsanancin kishi, ba zan iya raba mijina da kowace mace ba, aman ban taba aikata kisa ba....." ta karashe tana mai fashewa da matsanancin kuka
Kamar wace aka kunna ta kuma zabura ta dora da fadin " kuma a jiya a jiya kirana ya yi, bamu hadu ba yake ce min zai saka ni farin ciki yau, zai fara rabani da daya kafin dayar, ni ban san nufinsa zai kasheta ba "
Ammi kai kawai take girgizawa hawaye masu zafi suna zuba daga gurbin idannuwanta sunna sauka saman fuskarta, NAJEEBA kanta a zaune take ta zubawa mutanen nan uku ido, tun daga kan SULTAN, NADIA, uwa uba Zinaria
Haka kawai take jin abin sosai a ranta, harma irin tsayuwar da ya yi na yan mintunna ya kura mata ido ya bata tausayi
A hankali ya juya ya nufi dakansa wanda hakan ya saka du wani mutun dake wajen rakashi da ido, UMMU kanta hawayen take cike da mamakin wata amanar ta mutanen yanzu da sam basu da amana, shekara nawa kana tare da mutumen, du yawancin sirinsa da yardarsa ya yarda ya baka shikenan rana tsaka a kama irin wadinnan magangannun a kansa
Bai jima sosai ba ya bayana, cikin shigarsa ta sarakai sosai ya fito a yanda yake fitowa da
A yanzu sai ya zauna saman kujera ya dake
Ya dan jima a haka sannan ya dago da dubansa ya sauke kan NAJEEBA dake zaune jikinta doguwar rigar nan ce kawai ba wani lulubin da ya dace , dan haka a sanyaye ya furta " AMMI da UMMU, a lulube GIMBIYA NAJEEBA da NADIA "
AMMI na kallon yannayinsa cike da wani irin tausayinsa a zuciyarta ta janyo hannun NAJEEBA ta sakata a jikinta sannan ta lulubeta da alkyabar dake jikinta hakan ya sa sosai ta baza Alkyabar kasancewarta mai fadi da tsayi ga kauri sai ta wadace su ta baje da kyau ta rufe su su duka
Hakama UMMU ta aiwatar ta hanyar mayarwa da Nadia tata jikinta bayan ta kara lulubeta
Sandar dake hannunsa ta sarautarsa wace a yanzu a komawarsa ya daukota ce ya doka da karfi wanda hakan ya saka lokaci daya daga Zinaria, UMMU, AMMI, suka yi kasa da kawunnansu, Nadia da mahaifanta ne basu gama gane wasu sirinan maganar sarki ba hakan ya sa sai da suka kalli yanda su AMMI suka yi sannan suma suka sada nasu
Budewar da aka yi aka shigo da salama ne ya saka gaban AMMI yankewa ya fadi, muryar Amintace ne ta bayana rikeken Namiji maji karfi, tsayaye mai yannayin tsayayen namiji,
Sai da ya dan saci kallon mutanen wajen sannan ya yi irin gurfanar da yake dan kawo gaisuwa ga SULTAN SHAHEED
SHAHEED kallonsa kawai yake, sai da ya jima a haka sannan ya ce " Ka kula da bata mutu ba, gatanan ta mike da ranta AMINTACENA? "
irin yanda ya furta kalmar AMINTACENA din yana mai cije lebensa da karfi ya saka Ammi rintse idannuwanta cike da bacin rai da fargaba
Kara sada kansa ya yi, du da irin yanda gabansa ya kwonci kwonci ya fadi, sai ya yi kokarin anfani da kwarewarsa ta wajen yaudarar mutanen dake tare da shi da zuciya daya wa'inda basu gama fahimtar shi din ko wanene ba ya kara tausasa kalamansa domin sam bai taba tunanin Zinaria wawuyar da zata iya sakarwa lokaci daya bane harma ta fadi abinda ke faruwa dan haka ya dauki aniyar karyatar da Gimbiya a gaban sarki duda hakan baban laifin da ake iya gurfanar da shi ne, sai dai zai yi anfani da tarin yardar da Sarkin ya yi masa shima ya kwatanta kwatar yancinsa, dan haka ya ce " wace bata mutu ba ya uban gidana "
Shaheed ya kara lumshe idannuwansa cike da dacin zuciya ya dan saki murmushi yana kawar da kansa, ta yaya zai zauna su ci gaba da wulakanta junna? Dan haka dubansa ya kai wajen mahaifin Nadia ya ce" honorable, gashi a tafi da shi PeJi, ka sani wannan yaro horona ne, domin tun yana da yan dabarunsa na kasancewa police a da, na kara nitsar da shi na bashi horo kala daban daban na yau da kulun, sai kun yi taka tsantsan da shi, sai kun dora idannuwanku a kansa sosai, kar ku saka shi a daki mai kasa ko mai ruwa, ku kiyaye saka shi a daki mai duhu , ya kasance a kejin da hasken wata da rana ke iya haske shi, ya kasance koda mutun daya ne na ganninsa hakan zai hanna masa du wani yinkuri na gannin ya kubutar da kansa"
Dan sasautawa ya yi gannin irin yanda ya dago a gigice yana kallon SULTAN
SHAHEED ya maido dubansa cikin idannuwansa, ya kasance sun yi ido cikin ido da wani irin kakausan kallo da idannuwansa da suka dauki ja yake kallon na Amintacensa, da sauri ya sada nasa duban dan kuwa baba da babansa fa, sai dai baki daya jira yake ya karasa ya bashi damar yin magana aman sai ya ji ya dora da fadin " A bincika maganar Gimbiya NADIA, sannan a yi anfani da shaidar abokiyar aikatawar tasa, na baku damar ku shigo fada ku yi binciken da ya dace da su baki daya, du wanda ya taka doka ta taka shi koda kuwa *Gimbiya Zulaihat* ce ! Ya karashe yana mai doka sandar nan a kasa a kausashe ya furta " *Idan har ka yi gigin tashin da kake kokarin yi a wajen nan zan tashi mu gwada karfi da kai wulakantace mai wasa da Amanar Allah! Domin ina mai tabatar maka ba zan barka ka huta ba har sai ka samu naka hukunci daidai da laifinka, sai ka girbi abinda son zuciyarka ya kaika aikatawa!*
Sakwat ya yi ya mayar da kafar tasa, ba zai yarda du haukansa Sultan shaheed ya ajiye alkyabarsa dominsa ba, shi kam ba yau ba ya ringa tunanin karfin Sultan Shaheed kamar mai iskokan dake doka mutun da kasa, irin mutanen dake kawo masa tsagerancin da wani sa'in dole sai shi zai iya tankwasa su bake wa'inda suka shigo da takamar asirinsu dake tatare da su hakan ke sakawa su gagari dogarai, daga ya fuskanci hakan yake gagawar yiwa tufkar hanci tun kafin a gane gazawar dogaransa da ba gazawa ce sukai ba, lale lale shi din ne ya san abinda ya taka shi yasa du wani kwaro mai jin kansa na hayaki yake yin lakwas a gaban Maza, dan kuwa makashin maza maza ka kashe shi ba shaka!
Sojoji ne su hudu suka shigo, babansu ne da yara uku,
Suma dukawar suka yi suka kawo gaisuwar sannan mahaifin Nadia ya kora masu bayani, da irin tsaron da ya kamace su da komai, sannan suka sakawa Amintace ankwa wanda ke ta fitar da huci yana son kallon Zinaria dake kuka ya kasa har suka fita da shi
Sai da ya kuma rintse idannuwansa ya bude a sanyaye yana kallin iya mutanen da suka rage domin mahaifin Nadia an tafi da shi, sai mahaifiyarta , ya kai dubansa wajen AMMI ya furta" A kilaceta bangaren bayi "
.yana gama fada ya mike inda baki daya Zinari ta idasa kara zubewa tana son kama kafafuwansa dan ta bashi hakuri, aman ina ya ki bata damar hakan domin na farko da ta rike irin yanda ya wancakalar da ita ne ya sakata idasa fashewa da kuka tana fadin ita bata yi kisa ba, bata yi zina ba za'a kilaceta a bangaren Bayi? Ita ba baiwa ba jinnnin sarkin Agadez, matar Suktan shaheed wace ta bashi d'a, itane yau za'a kai bangaren bayi? Dan ta yi kishi shikenan sai a wulakantata?
Da zafi zafi AMMI ta ce" wato har yanzu baki ga ilar tarbiyarki da mashawarantarki da son zuciyarki ba har kike furta kalaman nan? Wato har yanzu baki gane alfarmar kin amsa kiran sunnan matarsa ya saka ba'a saka maki ankwa an fita da ke a gaban talakawanki ba? Wato har yanzu baki gane kina cikin matsala mai girman gaske dan kuwa ke kanki baki san irin abinda yake bakin ko na menene ba har sai sun gama bincikensu a kanki sun gano irin girman laifinki shin ya cencenta a barki a hora ki a sirri ko kuwa dole a fitar da sirrin ba? Ke baki gane cewar alfarmar mahaifinki kika ci ba?, Baki gane cewar a yau, a yanzu ke din nan ba kowa bace sai sakaryar macen da ta kasa yin hakatacen kishi ta tafka kuskure wa rayuwarta ta wulakanta kanta ba? Baki ji daga bakin wanda kika yi mugun abun dan ki malake shi naki ke kadai din kin cenza sunna daga ZINARIA zuwa Zulaihat ba?, kaicon ki ZULAIHAT, kaicon ki, ke kau kin shiga uku, ki rasa wanda zaki ci amana sai mijinki?, kishi ai ba hauka bane ZULAIHAT! Ke yau koda an samo gaskiyar lamarin cewa babu hannunki a maganar kisan nan kina tunanin SHAHEED zai sauko da wuri wuri ya dube ki ne? Zaki samu irin darajar da ya baki a da ta kasancewarki matar da ya fara aura, wace ya fara haihuwa da ita ne? Zaki yi asara ta yardar da mijinki ya baki, zaki yi asara ta irin gannin girmanki da kimarki da yake, zaki gani a aikace ke din ba wanda kika fi, zaki fahimci halayanka sune limamin dake jan ragamar rayuwar da zaka iya fuskanta da mutane tun a nan gidan duniya! Kin san kina son sa kika yarda aka aura maki SULTAN? Inace y'ayan zamani akoy gungiyar dake kare hakin ku, koda kuwa mahaifinki ne sai su hanna shi yi maki auren dole, ita mahaifiyar take da ta kasance babar banza ta isa ta hanna kanta zama da kishiyar ne? Yaya bata iya hanna komai da nata rayuwar gidan mijin ke kike gannin ta isar maki? Dan ta haife ki shikenan komai halayanta sai aka ce ki yi mata biyaya? Ke din sakarai ce da baki san abinda ya dace da rayuwarki bayan haihuwa guda da bari uku da yanzu y'ayanki hudu a gidan nan, da a gabansu zaki amshi hukuncin cin amana wa abihnsu? Yaya zaku yi auren gidan sarauta ku yi tunanin zaku kasance ku kadai jal?, ke a zamanin nan ko talakan da bashi da ko sisi ya samu damar jera mata hudu jera sun zai abinsa koda kuwa bashi da abinda zai ciyar da su ne, bale wanda Allah ya horewa? ke da kina da hankali, ko da kina tare da magaya masu nazari da sun nusar da ke cewar idan akoy mai dama a wajen mijinku ke ce, ke kika fi kowa sanninsa kafin wata, ke ce mai dauke da lakanin da zaki iya zuwa kai tsaye gare shi kafin wata, ke din nan da kin koya masa yanda a duniya koda ya so wata fiye da ke to fa tsananin girmanki, darajarki, kauna ta zaman tare zai hanna masa wulakanta ki, an fada maki matar farko abin wasa ce a zuciyar mijinta? Idan kin ga namiji yana abun kirkin da a da ba haka yake ba sai bayan aurensa tabata harda gudunmuwar matarsa, idan aka ce lalacewa halayansa suka yi tabata wace ta ja hakan ita ne, menene burinki? *MULKI, ARZIKI, KI KADAICE SHI IYA KE* dan kar KAWAYE SU ZAGE KI, ko a gazawarki? Sai gashi ina mai cike da tsoron kar a je kin rasa komai.......AMMI ta karashe tana mai share hawayenta sosai
Dubanta ta mayar wajen mahaifiyar Nadia da