Showing 30001 words to 33000 words out of 228147 words
Chapter 11 - MAGE (Mai kwanciyar Daukar Rai) Book Complete Na Sajida complet.txt
sauri ta shiga neman abinda zata yafawa kanta tana fadin" gani nan zuwa
Su kuwa tafia suka yi mai dan tsayi ya tsaya wajen masu gashin kaji
Siya ya yi ya shigo motar da su ya tayar ya karasa wajen stade, wajen da yawanci samari ke zuwa su kebe da yan matansu su yi hira cikin aminci
Sannan wajen akiy duhu hasken bashi da yawa sosai
Kashe motar ya yi ya dauki wayarsa ya haska yana duban fuskarta
A hankali ya ce" ina son ki Najeeba, ke kuwa kina wahalar da tsufana
Murmushi ta masa ta ce" ka daina kiran min kanka da tsoho, ka fi yaro karami a wajena kai din jarumina ne na yarda da hakan
Kansa ne ya ji na huruwa ya kawo hannunsa a hankali ya shafi gefen fuskarta wanda hakan ya saka ta dauki hannunta ta bige hannunsa har wayar nasa ta fadi
Ranta ne kuma ta bata ta ce" meye haka? Ka san dai ba kyau ko?
Kansa ya dafe yana kallonta ya ce" wai wani irin ba kyau? Yaya kike son ringa cutata ne a rayuwa? Ni bance zan je cen ba, na adana zuwa cen har mu yi aure aman kuma dan taba jikinki ba zaki barni ba sai ki ringa hanna min ko dan ba ni ake yiwa son auren ba?
Idannuwanta ta lumshe cike da rakaicin soyayar zamani,
Soyayar zamani na bada gudunmuwa sosai wajen kokarin tatsar mazan zamanin da take
Dan me maza suke kokarin nunawa mace iskanci koda kuwa da nikaf suka ganta? Yanzu har fadi ake masu nikaf din sun fi masu yawo ba hijab munafurci shin laifin matan ne ko mazan?
Hannunta ta saka zata bude motar da sauri ya ce" hala har kin yi fushi? Kin ga kar ki min fushi dan Allah dawo mu ci kazarmu ki amshi tsarabobinki kin ji?
Najeeba ta juyo tana kara hade rai ta ce" bude min na fita
Hannayensa ya saka gaba daya ya janyota jikinsa yana fadin" come on baby meye na fushi bayan ko dan shan mintin nan baki taba barina na yi ba
Sosai ya riketa a jikinsa ita kuwa ta saka dukan karfinta ta hankade shi ta mika hannunta da sauri ta danna mabudin dake gefensa ta bude motar ta fito da wani irin karfi
Wani kukan takaici ne ya zo mata lokaci daya lafayarta ta warware
Bayanta ne ta ji ya daki wani abu
Da sauri ta juyo jin an rike damtsen hannunta
Kamshin turaran da ta shaka ne ya so halaka tunaninta da sauri ta saka hannunta da lalube ta lalubo jin jikin baya dauke da babar riga hakama fuskar ba nadi
Wata mota ce ta hasko wajen
Idannuwanta ne suka sauka a fuskar wanda ya riko hannunta
Idan ana fadin an yi gamo takan dauka a wai ne sai yau da ta yi gamo da kanta
Wannan mutumen aljani ne , aljanninma mai aljanin kyau
Girarsa biyu a hade take kamar ransa a bace sai dai kyan fuskarsa ya batar da bacin ran
Wani dogon hanci ne da shi da lebunna jajaye uwa na macen da ta san kanta take gyaran kanta
Kamshi yake mai dadi da sanyi
Kirjinsa wasu rikakun pecto biyu daka daka ne suka gaje wajen
Damtsen hannunsa kuma tamjar zasu fasa rigar jikinsa baka wace ta dame shi
Tsayinsa sosai ya yi mata tsayi hakan ya saka gaba daya kanta ke kallonsa sama sama
Rigar jikinta ta kasan abayar fara ce mai dogon hannu aman ta dameta sosai
Ya take dayan hannun lafayar nata hakan ya sa take kara karkacewa
Bata taba jin mutun mai karfinsa ba, irin damkar da ya yiwa hannun nata ya sakata jinta ficik a hannunsa
Gaba daya jikinta ne ya kara daukan rawa tana dubansa shima ita din yake kallo yana son gane shin abinda ya fitar da shi ya ganni ko ba haka ba?
Takaici, haushi, tarin tsanarta ne yake ji a ransa hakan ya sa ya kara matse tatausan damtsen hannunta
Bakinsa ya buda a kausashe ya ce"
To fa, waye wannan?
Ina sarki?
Zai samu damar hukunta NAJEEBA kamar yanda yake fata?
Najeeba gamo fa kikai mun shiga uku😲😲😲😲😲
[31/03 à 21:37] Sadjida: 🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
12
Bakinsa ya buda zai yi magana, sai dai ta rigaye shi ta hanyar juyawa ta waiwaya ta kuma juyowa wajensa
A rikice take, hankalinta a tashe yake hakan ya sa a hargitse ta nuna masa motar ta ce" zai zai taba min jikina
Idannuwansa ya kausasa yana dubanta,
Sai da ya yi iya yinsa ya kara matse damatsunnan hannayenta dake cikin dafin hannayensa ya ce" ba abinda ya kawo ku nan kennan ba?
Magana ne ya yi mata a kausashe, a kidayance ,
Iskar bakinsa dake kusa da ita sosai ne ta fito ta daki hancinta
A hankali ta lumshe idannuwanta tana jin zafin rikon da ya yiwa hannayenta
Kanta ta ringa girgizawa da sauri ta ce" aa, aa, ni ba yar iska bace
Idannuwansa da sukai ja ya kai dubansa wajen motar, gannin na cikin motar na kokarin fitowa ya saka shi yi mata wani ja tamkar ya ja dan karamin yaro sosai
Sai da ya kara yin cikin duhun da ita ya sasauta mata rikon karshe ya saki hannayen nata
Da yake ya jima cikin wajen, ya fita ganninta sosai duba da ita a rikice take sai abin ya mata yawa take ta neme nemen inda zata saka ranta
Bakinsa ya tabe ya juya da sauri zai tafi
Da wani irin karfi ya ja ya tsaya hakan ya sa ita da ta tarbi gabansa dukan kirjinsa da goshinta
Hannunta ta kai gaban goshin nata tana sosawa a hankali ta ce" aushhhhhh
Tsayawa ya yi kawai yana kallonta
Sai da ta sosai sannan tana dubansa ta ce" dan Allah ka taimaka ka fitar da ni daga wajen nan, walahi ban taba zuwa ba kar wancen mugun ya cin min
Ji yayi gaba daya ta gama raina masa wayo, itane take gudun kar namiji ya cin mata? To ko ta danfaro shi wasu kudade ne take gudun ya kamata ya amshe?
Sai dai irin kallon da yake mata zai iya gannin yar karamar wayarta a jikinta ta cikin rigarta sakamakon rigar a matse take sosai
Bayanta baya gannin kudi ko abin kudi idan dai ba a cikin sket dinta ta saka ba
Shi zata kalla ta rainawa hankali?
Kansa ya girgiza ya ce" ba saurayinki bane?
Najeeba bata taba zuwa wajen nan ba, sannan zata iya rantsewa bata taba samun kusanci da namiji irin yanda Ambasador ya yi mata a yau ba
Hakan ya sa baki daya jikinta ke rawa takaici ya gama rufe mata zuciyarta
Hannunsa ya kai ya damki hannunta ya juya ya shiga janta
Bin bayansa kawai take
Bata san shi, bata taba haduwa da shi, bata san mutun ne ko aljan ba, bata san shima zai cutar da ita ko akasin hakan ba abinda ta sani daya ne tana son ta yi nisa da motar Ambasador
Tana so ta yi nisa da shi baki daya dan tana da muradin kasancewa ita daya
Gani take ko ina ta bi idan ta zo wucewa yana iya ganninta, gani take zai kuma yin yinkurin aikata mumunan aikin nan da ya yi na hada jikinsa da ita
Sai da ya fito bakin titi da ita ya saki hannunta
Juyawa ya yi yana tafia cike da wata irin kasaitar da ta sakata zubawa bayansa ido
Tsalaka titin ya yi wanda har sai da ta rintse idannuwanta sakamakon wani mai mota da ya so kade shi cikin ikon Allah maimakun ya tsere da sauri ko ya yi gudu dan tseratar da rayuwarsa sai ya zama mai motar ne ya take birki har hakan ya yi kara sosai
Tana buda idannuwanta ta ga ya tsalaka, bai kade shi ba mai motar ya leko kansa yana fadin" ka ga malan rai zaka yiwa kwombo? Ka wani hau bakin hanya kana tafe da takama tamkar *mai DAMAGARAM?*
idannuwanta ta yiwa luuuu ta ga ya shige kwanar hakan ya sakata daga kafarta a hankali tana gyara rufar lafayarta
Ta sha cika dare a shago dan takan kai har sha daya idan aiki ya mata yawa
Aman yaya DAYABU ke zuwa ya tarbota su tafi gida
Yau sai ta ringa tafia tana hankalce da mutane cike da tsoron daren
Da haske ko'ina ba wani duhu ya game garin ba
Mai mashin ta tsayar ta hau ta fada masa ya kaita anguwar gidan sarki
Yana kaita ta bashi mai akun nan guda dake bayan wayarta
Ido ya zaro ya ce" haba dai Hajia yaya zan samu cenjin wannan?
Bata yi masa magana ba ta juya ta nufi ciki tana tafe cikin nutsuwa
Baki da hanci ya saki yana kallonta har ta shige babar kwanar gidan sarki
A hankali take tafe tana jin zuciyarta na dokawa dan bata san yanda za'a yi ta samu shiga ba
Motar da ta hasketa ne ta sakata rintse idannuwanta ta rabe waje daya
Kusa da ita aka tsaya tana jin jikinta ya dauki rawa dan sam bata son aikata laifi a wannan waje
Wanda ya fito daga motar ya sakata sauke ajiyar zuciya
Da gudu ta karasa ta fada jikinsa lokaci daya ta saki kuka tana kara dora kanta a jikinsa
Kiransa Anmy ta yi cewa bata ga NAJEEBA ba, maza ya samo mata ita
Gabansa ne ya fadi ya shiga kokarin cireta a jikinsa sai dai ta ki bada dama tana kara shiga jikinsa tana hawaye
Muryarsa a cakule ya ce" NAJEEBA, meye? Me ya faru? Me ya same ki? Ke da wa?
Kukan take tana jin ciwo a ranta , gannin ya bambareta daga jikinsa tana kallonsa ta ce" yaya, me me yasa kowani namiji yake son nuna min shi dan iska ne? Yaya me ya sa suke son nunawa mutun iskanci?
Gabansa ne ya kara faduwa hakan ya saka shi kurewa fuskarta kallo
Muryarsa na rawa rawa ya ce" Najeeba, kar ki fada min abinda zan tsani kaina , kar ki fada min abinda zai sakani yin gaba da ke
Mutuncinki kika zubar?
Da sauri ta rintse idannuwanta dan jin maganar da girma sosai a kunnayenta
Sai kuma ta bude tana girgiza kanta tana kokarin rungume hannayenta a kirjinta
Hannunta ya kamo ya sakata cikin motar ya tayar ya juya cikin gidan
A hankali yake tafe har ya karasa wajen ajiyar motoci
Yana dakatawa ya kashe motar a hankali yana sauke ajiyar zuciya
Sai da ya sanyaya muryarsa sosai sannan ya ce" da me kike jiran ganni bayan kin ce zaki amshi abubuwan hannayensu?
NAJEEBA ke baki yarda sun san gidanku ba, wanda ya san gidanku ya tabata mai naci ne ya kai kansa gidanku
Najeeba ke baki yarda sun san kina da mahaifi tsayaye da kuma yayan da zasu ringa shaku ba
Najeeba, kin mayar da aljihunsu wajen wasanki , kin kware wajen iya juya tunaninsu su fitar da dukiyarsu su kashe maki
Dubanta ya yi ya ce" me kike jira? Me zasu so su kuwa a wajenki? Bayan sun san ba su kadai bane, sun kwana da sannin basa layin wa'inda zaki aura
Me zai hanna su yi tunanin iskancin kike so bara su nuna maki ba?
Kansa ya sada gannin ta kure shi da ido kuma harga Allah du ta fi su magana ga shegen karfi da idannuwanta ke gare su
A hankali ya ce" kin san wani namijin na nuna irin haka dan ya gane shin matar ya kilace ce ko matar a watse ce?
Wanin kuwa da kika gansa dama dan a watse din ne
NAJEEBA, shi irin haka a haka ake rasa na kirkin
Tsorona a haka na kirkin ya sulube maki ke kanki baki ankara
Hannunta ya kamo ya dago yana dubanta ya ce" idan kika kare mutuncin kanki, kon kare mutuncinki ne a farko, kin kare na y'ayanki, sannan kin kare namu
NAJEEBA, kin fito daga tsatson da ya yo sunna, Allah ya daukaka
Abu kankani ake jira karamin abu ya zaga gari
Shi yasa nake maku nasiha cewa ku kama kanku ku rike mutuncin kanku
NAJEEBA ta lumshe idannuwanta a hankali ta ce" ya, kai ka san ni ba yar iska bace ko?
Kansa ya daga yana dubanta
A hankali ta dantse lebenta na kasa tana jin ciwon abin a kasan zuciyarta
Dan kawai na so abin aljihunsu sai su so jikina?
Ta tambayi kanta da kanta
Sai ta girgiza kanta tana mai bawa kanta amsar cewa" da ya kare aikatuwa a duniya, da na gile shi da hakorina na kashe shege! Kudinka sai na ci idan har kana iya saki aman fa ba zaka zo ajiyata ba karya ne!
Hannun yayan nata ta kamo ta ce" zaka raka ni wajen Anmy? Kar ta min fada
Murmushi ya yi ya bude motar suka fita
Sunna tafe tana tsara irin abinda zata yiwa Ambasador, sai na ci ubansa na rantse! A haka har ta dauki alkyabarta da ta ajiye ta dora ta kara gyarawa suka nufi ciki
...........................................
Karfe biyu na dare
Alkyabarsa yake cirewa a hankali
Sai da ya cireta sannan ya shiga warware rawanin kansa
A hankali ya gama warwarewa sannan ya kama babar rigar ya sauketa
Sai wata riga dake ciki baka ta kama jikinsa sosai sai wandon shadar dake kasan rigar
Mikewa ta yi tana karasawa inda yake tsaye ya baiwa wajenta baya
Sai da ta dawo gabansa ta daga kanta tana kallon fuskarsa
A hankali ta kai hannunta wajen sajen fuskarsa ta dora
A hankali ta shafa tana kallon yanda idannuwansa ke lumshe
Hannunta ta saka ta shiga kokarin cire masa rigar sai dai tsayinsa ya saka sai dadafe take ta kasa cirewar
Dan murmushi ya sakar mata ya tayata ta hanyar rage tsayinsa
Rigar ta cire masa sannan ta kai wajen hancinta tana sinsinawa tare da lumshe idannuwanta
A haka har ta kai hancinta wajen bakon turaran da ta ji a hancinta
A hankali ta kara rintse idannuwanta jin yannayin kanshin Princsss a jikin rigar
Tana kallonsa ya shige bayi ita kuwa ta zauna saman lafiyaye tatausan bed dinsa da rigar a hannunta jikinta a mace ranta a bace hankalinta a tashe
Ya jima sosai a bayin kafin ya fito yana tsane ruwan wankan da ya yi
Turarensa yake shafawa yana hangenta ta madubin dake gabansa
Ya so ya yi nafila, sai fai gannin ta zo harka tana zaune har warhaka ya saka shi karasa kimtsa kansa ya saka kayan baci riga da wando mai dogon hannu sannan ya karasa saman bed din
Hawa ya yi ya kwonta yana kallon sama
A hankali ta karasa ta haye saman kansa ta dora kanta saman kirjinsa
Kamar wace take fada ta sada kanta sosai ta ce" Allah ya ja zamanin sarkina, Allah ya karawa mai martaba lafia da jisan kwana, Allah ya tsare mulkinka mai gidana
Idannuwansa kawai ya lumshe, bai san yaya aka yi yake jin kalaman nan a waje sannan ya ji su a dakansa ba, yana son jin wasu kalar kalamai na kulawa ba irin wadinnan ba masu zafi yake son ji wasu kala daban aman sai ya fita waje ya ji kirari ya dawo daka ya kebance da macen da ta fi kowa sannin sirin jikinsa wace suka rigaya suka zama daya itama sai ta bi shi da kirari
Hannayenta ta kai ta kashe wutar dakin, yar karamar dake gefen bedma ta saka hannunta ta kashe
Sannin cewa bai taba mu'amalantar mu'amala da ita da haske ba ya saka ita da kanta ke kashewa a irin wannan lokacin, kwarai ta fi kowa kiyasta sanninsa domin ba idannuwanta suke gane mata ba, jikinta ke daidaita mata irin girmansa
Idannuwansa ya lumshe yana jin kwarai yana da bukatar hakan,
A hankali ta shiga zamewa ta kwonta sannan ta janyo hannunsa tana sauraron kulawarsa
Ta kasance a kulun sai dai ta yi kwonce abinta shi kuwa ya bada kokarin komai
Hannunsa ya kai jikinta a hankali, sai dai ya ji laushin riga a hannunta
Rigar ya amsa ya ajiye gefe kafin ya shiga kokarin gannin sun samu nutsuwa baki dayansu
Ta fi so su yi ta romance, ta fi ganewa hakan ,
Tana samun hakan, mai sakata samun nutsuwa kuwa sai dai sam gogan nata shi baya samun nutsuwa a iya hakan
Sai da ta kankame jikinta cike da tsoro jin zai kai gareta
Hakan ya saka shi sasauta mata rikon da ya yi mata a hankali ya ce" ki saki jikin ki dan samun gamsuwa cikin salama
Ajiyar zuciya take ta saukewa tana son sakin jikin nata sai dai ta rigaya ta saka tsoronsa da tsoron abin a kasan zuciyarta hakan ke bata wahala matuka
Ta gurzu sosai dan sai da ta biya kwanakin nan kafin ya saurara mata
Bai koma saman bed din da dauda ba sai ya nufi bayi
Sai da ya tsaftace kansa sosai sannan ya fito ya dawo ya tarar ta cenza zannin gadon kamar yanda ya gindaya mata
Sai da ta gama ta dauke wancen zannin ta nade shi sosai ta mike bayan ta mayar da kayanta jikinta
Rigar dake ajiye ta karasa ta dora hannunta zata dauka
Sai dai bata kai ga dauka ba ya saka hannunsa ya rike rigar hakan ya sa ta sakar masa ta kara sada kanta tana dan murmushi ta ce " ka huta lafiya sarkina, Allah ya hutar da gajiyarka uban y'ayana
Cike da kasaita ya sakar mata murmushi yana kallonta ta juya ta fice
Me yasa bata iya zama a bangarensa komai dare bata iya kwonciya saman gadonsa sai dai ta je falo ta kwonta?
Kafadunsa ya daga yana baiwa kansa amsa cewa bata da ra'ayin hakan ne
Rigar d aya lura ta yi ta sinsinnawa da nishadi sai dai daga baya fuskarta ta cenza ya kai wajen hancinsa yana mai sinsinawa
Da sauri ya maida baya baya kusan ciki inda idan ya saka zata kawo masa daidai cikinsa ya shinshina
Da sauro ya cire daga hancinsa yana mai dafe gaban goshinsa
Kanshin turaranta ne wannan
Wani irin turare take anfani da shi mai kamshi mai tsayawa a jikin mutun haka?
Bakinsa ya tabe yana ayanna" idan har kere na yawo.....zabo na yawo na tabata wata rana zasu hade........................
Tun da sasafe suke kinkimtsawa
Sai da