Showing 84001 words to 87000 words out of 228147 words

Chapter 29 - MAGE (Mai kwanciyar Daukar Rai) Book Complete Na Sajida complet.txt

13 May 2025

10420

kallonsa
DAYABU da hankalinsa ke tashe ya shiga fadin" ba zan iya kuma zuba maku ido kuna yawo haka ba, du ku fitar da mazan aure a cikin manemanku a yi maku aure ku tare a gidajenku hakan zai saka mani nutsuwa a cikin zuciyata, walahi idan ayar nan ta kuma kasancewa a kan wani a cikinku bana tunanin zan iya yafewa Abih!

Lebunanta ke hadewa da junna sai jimkesu take tana kara budewa
A rikice ta ce" me me ya yi ne wai? Me ya yi?

DAYABI ya sasauta masu rikon jin du sun dago shi suke kallo

Kansa ya sada ya kasa magana hakan ya saka Ummukulsum dora hannunta a kai ta shiga zunduma ihu tana son mikewa ta yi burgima ko zata ji sanyi, cikin muryarta take fadin" shikenan uwa karuwa uba karuwi ko dai ni shegiya ce ban sani ba?

NAJEEBAma dake kuka tana kallonsa ta ce" yaya waye shege a cikinmu?
Ummulkhair kam sai ta kame, gaba daya ta kasa kuma motsa hannayenta tambayar da yan uwanta ke yi take jiran amsarta

Hannunsa ya saka ya rufe bakin Ummukulsum sannan ya ringa bin Najeeba da kallo wace ta zama uwa wata wada ke son tashi sai tsale take tana kai kawo sai kuma ta tsaya tana kallonsa gashi kanta baki daya ta balbaza shi hannunsa ya saka ya jata kasa da karfi hakan ya sa ta yi wani irin zama dabar a gabansa gabanta na yi mata wani irin tsalen albarka kamar zai bale ya fito daga kirjinta

Wayarsa ya dauko ya shiga galeri
Hoto ya fitar saman wayar tasa ya mika masu

Har rige rigen amsar wayar suke suka tsurawa hoton ido

Yannayinsa a kansu ya ce" sunnanta *HUWAILA* , sati daya ne tsakaninku ita da Najeeba,
Tana nan garin zaune gidan kannin mahaifinta tana karatu a lycee

Du da iein tarin kamanin da take kamar an tsaga kara ita da su bai hanna Najeeba cewa " yar gidan waye? Me hadinmu da ita mu kuwa?

Murmushin takaici ya yi yana kallonta ya ce" NAJEEBA MUTALAB idannuwanki sun samu matsala ne? Wannan da kike ganni yar gidan MUTALAB ce, jinnin MUTALAB ce wace ya samu a zamanin da baya jin magana!

Kamar ya kuma dima masu guduma haka suka kasance du sunna kallonsa
Sai cen Najeeba ta yi ihu tana zazaro ido a firgice ta ce" lalle akoy tashin hankali a gabana, ina tare da wannan lamari a tsatsona nake tata rashin mutunci a garin damaram? Ashe nima da nama lamarin a boye a tare da ni ban sani ba? Innalilahi wa'ina ilaihi raj'une

Ummulkhair ta ringa share hawayenta tana jan hanci ta ce" ko shine abinda yake saka matarsa yi mana wata magana cewar y'ayan yan iska?

Ummukulsum ta yi murmushi, ita abin sai take ganninsa wani iri, ashe ba mahaifiyarta kadai ce ke tare da wani mugun lamarin rayuwa ba?

DAYABU ya sasauta muryarsa ya ce" ku zauna

Irin yanda ya yi maganar ya nuna masu gabansa ya saka suka zazauna sunna kallonsa

A sanyaye ya ce" a kadan zai kai shekara shida da na san da yarinyar nan
Na bibiyi rayuwarta da ta mahaifiyarta har na samu cikaken bayani a bakin kannin mahaifinta wanda ke rikonta
Ya ki amsar yarinyar a bayane ya amsheta a boye ne
Komai nata shi ke mata , karatunta bukatunta aman kuma hakan na nufin kar ta yarda ta fitar da ko waye mahaifinta a garin nan,
Ban san nufinsa na yin hakan ba,
Yana yi ne dan ya boye sirinsa saboda idan sirrin nasa ya fita zai shafi y'ayansa, mutuncinsa ko yana yi ne dan son ransa??
Ajiyar zuciya ya sauke ya ce" abinda na sani shine kasata kasar hausa ce, mai dauke da al'umar da idan irin haka ta faru yakan zama matsala, yakan shafi y'ayan mutun, abin ya zama na gori, idan mata ne ka ga har ana gudun aurensu bayan ba su suka aikata ba kuma shi kansa wanda ya aikatan na tabata da ya san abinda zai je ya dawo da ya hanna kansa aikatawar

Kamar yanda na fada maku, ni DAYABU MUTALAB, na baku umarnin fitar da mijin aure kwana kusa ba nesa ba!
Sannan Abinda aka yanke shine.....Anmy ta roki Mai martaba alfarmar hadaku da masu tsaro sakamakon abinda ke faruwa a cikin gidan wanda yake cikin bincikensa
Ya zama dole ku dawo nan da zama sanadiyar abinda ya faru da Ummu, ta rantse ba zaku bi Abih gida ba shima kuma sai bai ja ba na tabata yana tsoron kadaicewarsa da mu yana gudun tambayoyinmu hakan ya sa aka dora dokoki a kan shiga da fitarku baki dayanku
Zaku ringa zuwa wajen neman iliminku a kan lokaci ku dawo a kan lokaci
Zaki bude saloon dinki wajen karfe goma na safe ki rufe goma na dare ku dawo gida tare da masu tsaronki

Tap.....shine abinda Najeeba ta fada a zuciyarta kennan, masu tsarona? Ana nufin za'a hada ni da wasu langayayun dogarai su ringa bina ko police? Ta yaya zan samu mijin na ware da wasu karti a bayana? Hala ba zan ringa zuwa wajen hutuna ba?

To yaya, zance fa? Ka san da dole sai mun ba wanda ke neman aurenmu dama zamu iya aminta da shi ko?

Idannuwansa ya zaro ya ce" Ummulkhair, ni da ni aka bi ba zaku yi wani zance ba! Sai Anmy ta kuma rokar cewa kuna iya baiwa mutun dama ya zo nan, ku gana da yama ya koma inda ya fito a falon da mai martaba ke saukar baki

Da sauri Najeeba ta ce" kana nufin falin da yana iya ganninmu sannan ya ji du abinda zamu tatauna da saurayin yaya?

NAJEEBA ko baki da gaskiya ne? Ya tambayeta yana mai kallonta da son jin amsa

Kanta ta ringa girgizawa ta koma ta zauna tana sauke ajiyar zuciya, wani irin zance zata yi ita kuwa bayan ta san wannan mutumen da ya tsaneta na iya ganninta yana jin abinda zata fada?
Sai kuma wani abu da ya diro mata shine yayan banki! Yanzu idan aka ce ta zauna da saurayi daya ana nufin nauyin aljihunta zai rage?

Aby daya da ta sani shine lale lale zata samo mijin aure, zata tsayar da daya kwalin kwal wanda zai zama mijin Najeeba

Bai bar dakin ba sai da ya kara kwontar masu da hankali, shi kansa ya samu hankalinsa ya kwonta da damuwar da yar uwarsa ta tsinci kanta a ciki kafin ya mike ya fice a tankamemen dakin nasu

Su duka sun yi shiru ne a kwonce, a hankali Najeeba ta lalubo wayarta ta turawa Zahrau message kamar haka" me kike ?

Zahrau dake zaune kunyar Mai gidan nata na neman kasheta sai hira yake mata yana kara son ta saki jikinta ita kuwa tarin kunyarsa ta lulubeta da tsoron yannayin kusancin da suke ciki ya hanna mata daukan wayarma bale ta ga message din hakan ua sa Njaeeba ta fita a wajen Zahrau ta shiga contact dinta ta ringa bi daya bayan daya sunnayen samarinta tana kallo tana tuna yannayin mutun da halayensa da komai da komai


Zaune yake bayan ya fito daga bangaren Zinaria wace ya taka yau da kansa ya kai mata ziyara dan gannin yaya yannayin jikinta yake? Ciki dai ya lalace domin bai kai lokacin haihuwarsa ba a dole aka fitar da shi akai mata wankin mahaifarta hakan ya sa take kwonce cikin damuwa da tsoron daga wayar mahaifiyarta
Ko da ya je ganninta ta yi mamakin ganninsa a bangarenta sai dai bata iya bashi wata kulawa ba har ya bar wajen dan hankalinta bama a jikinta yake ba

Sosai yake jin ba dadi na lalacewar cikin jikinta, sai dai ya dauki dangana ya barawa Allah tare da fatan samun wasu masu albarka masu zama

Alkyabar jikinsa ya saka hannunsa a hankali zai cire,
Da sauri ya dakata sakamakon wani abu da ya fado masa a rai

Idannuwansa ya daga ya kai dubansa kan agogon dakin.........................

Da sauri ya mike tsaye yana sauke Alkyabar kasa ya shiga taka kyawawan kafafuwansa saman lalausan cafet din wajen ya nufi wajen kujerar dake ajiye

Zama ya yi ya dora kafarsa daya kan daya ya shiga warware rawanin dake kansa

Sai da ya warwareshi tas sannan ya kuma tsurawa waje daya ido
A cikin ransa ya shiga ayanna : *IDAN FA BA BINTU AKA ZO KASHEWA BA, NI AKA ZO KASHEWA?*

Ba zai manta ba, ana zaune a dakin karatu a lokacin da aka gama daurin aure du kawunansu a sade sai ya so yin raha da su, domin mutanen dake wajen daga amintatunsa, sai iyayensa wa'inda suke tsofafi da datijai ne

Ba zai manta kalmar da ya fada ba, wace ya ce" *NI ZAN JE DAUKO FADIMA BINTU*
Ya fadi kalmar ne dan ya saka su sakin raha, sai dai maganar ta so ta bada armashi a lokacin da mahaifin Bintun ke godiya cike da farin cikin jin shi da kansa zai je daukota

An rarage mutanen dake ciki sai ya kasance saura mutun shida

Amintacen bafadensa ne ya kuma tambayar maganar cewa" ALLAH YA KARA MAKA LAFIA, SHIN A WACE MOTA ZAMU JE DAUKO GIMBIYAR?

Ba zai manta amsarsa da ya bada a bayane ta hanyar fadin : Sabuwar motar nan a ita zamu je dauko gimbiya.........................ya katashe yana mai sakin murmushi mai dan sautin da ya saka du mutanen wajen suma sakin murmushin sunna jinjina maganar cewa wai da gaske zai je ne da kansa?

Da sauri ya mika hannayensa ya janyo farar takarda da byro ya dora sama

Sunnayen mutanen dake wajen ya shiga rubutawa daya bayan daya
Sai da ya gama rubutawar aman bai saka na amintacensa ba

Bin sunnayen ya shiga yi da kallo
Idan akoy abinda rayuwa ta koya masa shine jiran komai daga kowa
........ya jima yana wannan tunanin har ya ga dare na tsalawa

A kan sunayen ya ringa dora number tun daga 1 har na karshe kafin ya mike ya nufi bed dinsa dan samun hutu komai kankantarsa domun rabonsa da ya huta har ya manta tun ihun fitinaniyar yarinyar nan

Wata irin mika ya yi a saman bed din , bukatar kebewa da mace yake, hakan ya saka baki dsya jikinsa ya mutu wata irin kasala ta dirar masa

Tsintar kansa ya yi da kiyasta irin abinda ya dace da damkarsa
Da sauri ya rintse idannuwansa sakamakon hotunnan da suka shigo zuciyarsa
Korar shedan ya ringa yi ido rufe dan samun nutsuwa kafin ya mayar da kansa ya kara dannawa a saman fillow din yana jin yanda bugun zuciyarsa ya cenza
Dolema ya auro uku ya jera!
Daga bakin lokacin da ya fahimci cewa daya ba zata iya da shi ba ya san cewar sai ya kawo, zai karo uki ne a kwana kusa ko dan ya ringa zagaye su
A cikinsu ya tabata ba zai rasa wace ta dace da bukatar zuciyarsa ba!


..........................................

Aiki take da kanta yau, tana kitsa gashin wata bafulatanar mata mai son gyaran kanta, ana yi mata kitso kananu masu kyan gaske

Idan tana kitso a tsaye take yinsa wanda take yiwa kuwa sai ta hau kujerar saloon sunna yi tana kallon abinta

A saman gashinta ta totse abin caje kan, sannan abin tsagawar daya a kan matar daya kuwa a cikin gashinta domin gashin nata hade shi ne ta yi ta kame shi a sama

Hira suke da Nadia tana yar daria
NADIA ta ce" NAJEEBA, ni da yau na maki abinda bakya so, Najeeba Huzaifa ya matsa min walahi, kin ga ko yau da sasafe shi ya tasheni a baci ya rantse cewar ba zai iya hakuri ba
Najeeba meye laifin Huzaifa ne? Idan kudin ne ke kin san waye HUZAIFA a damagaram, yaro ne mai kudin balaki
Idan kyan ne meye laifinsa?
Gashi baki ne kamar yanda kike so mijinki ya kasance me ya sa ba zaki amsa shi ba? Shi fa a shirye yake da yau kika ce ya fito zai fito

Tsaga wani kitson ta yi ta dauka sannan ta dubeta ta ce" numberna kika bashi hajia ko me kika min?

Nadia ta dan kebe bakinta ta ce" walahi na bashi numberki, na fada masa inda kike bi, na fada masa harda da food din dake birke ki

Najeeba ta ringa gyada kanta tana idasa kitse jelar kitson matar, domin har karshe take kitse mata shi ya kwonta yar yar da shi shi yasa matar ke masifar son ta zo saloon din, bata barinsa sai an yanyara mata kitso da kunshi an wanke mata kafarta sannan ta sayi dadadan turarukansu masu birge mijinta ainun

Najeeba ta ce" kin san meye, ya cika daria wa kowa ne,
Nadia ina son namiji mai wasa da yawan yin daria aman fa ni kadai nake so ya ringa washewa hakora ba kowace mace ba haka kawai

Kwonkwasa wajen da ake ne ya sakata kai dubanta kofar

Gabza gabzan dogarai har biyun da aka hadata da su ne suka tarewa wanda ake maganarsa hanya

Saurayi ne jikake, ya jiku har ya jike da cefa ga iya kwaliya
Yana da kyakyawan nasaba, gashi da fara'a
HUZAIFA dan kasuwa ne sannan yana karatunsa wanda ya fi baiwa kasuwancinsa karfi domin karatun mamansa ce ke matsa masa aman ya malaki abubuwan rayuwar da ba shi ba ko wani masa ya huta

A duniyarsa yana son mace mai irin halayen Najeeba,
Ya santa ne dalilin cousine dinsa Nadia,
NAJEEBA na kashe shi, shagwabarta na haukata shi, idannuwanta na tsuma shi, uwa uba tafkeke kugunta mai kara masa yardar cewa yes shi namiji ne sakamakon idan ya ganta yakan rasa nutsuwarsa ke kara haukata shi da son malakarta ta kasance tasa
Yakan je wajen da take buga basket ball ya zauna a motarsa yana hangen yanda take wasanta ransa na tafarfasa da kishin mazan wajen
Yakan sakin murmushi idan ya ji wajen manya manyan maza irin ana hirar yan mata an yi katari wani ya sako zancen babyn
Irin yanda take wawusar aljihu na kashe shi hakan ya saka yake so ta shigo nasa aljihun domin yana kara kaimin nemansa dan ya bude mata bakin aljihun nan ta shiga ta yi burgima ta yi jina jina ta wanke kafa ta fito

Sai dai abinda ke damunsa ta kasa bashi dama

Ta raina shekarunsa, ta kuma raina yannayinsa
Ya kwatanta tashi daya amsar da ta bashi shi je" murmushin sangarta kafin ta dora da fadin" aman tsokanana kake ko? Ka dai san koda ka girme min bai fi da shekara biyu ba, gaka mai arhar daria a kowa, yaya kake so na maka wayo ka hada ni da hukuma??????










Happy weekend peopleπŸ’“
[31/03 Γ  21:39] Sadjida: πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»πŸ§•πŸ»


*Na*


*SAJIDA*


πŸ’«βœ¨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🀝

β˜† *[ T.M.N.A]* β˜† πŸ“–πŸ–ŠοΈ

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_


29



Ta ce" ni banma ga dalilin da zan nuna na san shi ba, bai min ba, ko a layin mutanen da zan iya jin nauyinsu ba,
Sam mutumen bai min a cikin tsarin rayuwana ba

Mikewa ya yi tsaye hakan ya bayanar da irin tsayinsa,
SHAHEED ya kasance namiji daya kwal da babu irinsa
Yana da tsayi daidai misali,
Shaheed ba shankalale bane kuma ba rubdede bane
Jikinsa ya kasance jiki kamame mai tsafta
Kirjinsa yana da fadin gaske sannan cikinsa ba a shafe bane yake luwai kamar na mace aa, a shafe yake aman da wani gida gida irin na masu daga karfen nan
Ya kasance mai hannaye masu tsayi da kauri, damatsunnan hannayensa tamkar na dan dambe wanda baka gane hakan sai ya saka irin rigunnan nan na gudu
Irin yanda ya kware wajen sarafa doki haka ya kasance tamkar doki a kowani fani, sam bashi da wasa ko laso laso
Fuskarsa dauke take da gira mai yawa wace har ta kusan hadewa da yar uwarta baka sidik,
Idannuwansa kuwa manya ne ba fici fici ba masu dauke da gashin ido mai yawa baki sidik, sannan sunna dauke da kwali mai ruwan maroon mai duhu wanda yake kyalkyali ko a cikin duhu ne
Hancinsa yana da dan girma sannan yana da karan hanci mai tsayi
Lebunansa masu fadi ne kadan sannan pink color ne yas da su ga taushin tsiya
Yana da cikar gashi irin na larabawa domin ya dauko gashin Anmy ne wanda yake yawan aske shi sai dai duda haka ya ajiye kyakyawan sajen da ya je masa har wajen habarsa ta fitar da san gemun da yake dan ragewa yana gyara shi yana kara hawa fuskar yasa das da shi ga baki ga kyalkyali
Cinyoyinsa sunna da tsayi da wani irin tauri irin na wanda ya sabawa jikinsa da sport sannan kaurinsa masu kauri ne da tauri suma a rike suke a jikinsu
Yana da manyan tafin kafafuwa irin na manyan mutanen nan na da duda basu da tuwo sosai

Cike da kasaita ya ringa takowa ya yi taku uku ya kasance tsaye kikam a gabanta hakan ya saka ta zama wata yar firit da ita tamkar wace zai yi kujera da ita


Kirjinsa ta dan kurawa ido kafin ta dan matsa kusancinsu ta dago da kanta tana kallonsa da dan mamaki ta ce" kanshin turaran nan, a ina ka samo shi?

Idannuwansa ya lumshe ainun a kanta a kasan zuciyarsa yana furta lale na yarda baki da kunya ko daya yarinyar nan, muryarsa da ta dan fara kausasa ya buda ya ce" kin san shi ne?

Fuskar tasa ta dan kurawa ido kafin ta cire dubanta daga kansa ta mayar gefe tana mai sakin ajiyar zuciyar da bata san dalili ba sannan ta ringa dan girgiza kanta

Fitowar dogarin dake tare da ita baban ya saka shi cije lebensa na kasa yana son kara kawar da fuskarsa irin na dazu don kar a je ya gane shi a hankali ya furta" na yayana ne na dan fesa, turaran ne na birge ni

Dan murmushi ta yi, bata ce komai ba, karamar eayar dake aljihunsa ya ciro ya mika mata yana kallonta ya ce" tunda yau kin aminta da abotakata, saka min number ki

Wayar ta kai dubanta sama, wata irin waya ce yar karama mai sulbi sannan fara ce kal kamar hannu bai taba tabata ba bale a yi tunnanin ana ajiyeta a wani waje

Tabas mutumen nan yana da tsafta, yana

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login