Showing 51001 words to 54000 words out of 228147 words
Chapter 18 - MAGE (Mai kwanciyar Daukar Rai) Book Complete Na Sajida complet.txt
ba zai yi ya gama ne ya bashi lafia yau ya ga iskanci
A takaice dai wannan mutane da suke mata da miji dama haka suke, sukan tayar da balaki su daki junnansu har titi ne
Tabas matar bata zauna dam ba, shi kuwa mijin hakan ya saka ya zama wani irin marar tausayi da daga mata kafa a rayuwa
Idan ba yan anguwarsu ba a wajen anguwar ana zaginta cewa ta fi karfinsa ta hanna masa zaman lafia
Yan anguwar kuwa sun san waye shi domin mutun ne mai dukan mace kamar ya samu ganga, yaka daketa ta rama daidai gwargwadon iyawarta su yiwa junna gori sannan su koma cikin gidansu,
Y'ayansu ba mai mutuntasu, yawonsu suke son ransu ba matan ba mazan ba wanda ya isa ya hana su ko ya saka su a cikin iyayen nasu...........................
Wayarta ta ciro ta nemi layin wani farkanta ta koma gefe tana juran karasowarsa dan ba zata je gida a yanzu yanzu ba a yanda ta zage shin nan ta san a irin lokacin nan sai ya kusan kasheta
Anmy kam ko bayan tafiarsu sai ta kasance mai baiwa Najeeba kulawa duda ta ga ta dan warware ta shige cikin yan uwanta sunna cin abincisu aman sai ya kasance tana yawan tambayarta yaya take ji har suma suka so tayar da hankalinsu sai ta basar ta nemi zuwa kwonciya
A ranar da Bintu ta cika kwana tara da rasuwa da safe ya kasance du an watse sai masu hidimar gidan sai yan matan Anmy da basu tafi ba sai an yi sati biyu zasu koma gida
A yau da safen ne kuma suka soya fara, sukai mata suya mai dadin gaske suka zauna a nan falo tare da Anmynsu itama tana cin kambolinta basu saka mata yaji ko daya ba
Sunna yar hirarsu falon sai ya su ya su, hirar ba wani ta shan dariya bane aa, aman lokacin sunna raba shi ne da wani irin shakuwa da kulawa da junna
Maganar da jakadiya ta duka tana fadi ne cewar matar Abih na neman iso ya saka Gimbiya kallonta da kallo irin na son ta maimaita
Kara sada kanta ta yi ta maimaita maganar
Dago kanta gimbiya ta yi daga kallon Jakadiyar ta sauke saman yaran
Ta dan jima kamar second talatin tana kallonsu sannan ta cire kanta a kansu ta gyadawa Jakadiya kai
Mikewa Jakadiya ta yi ta juya, dan ta gane amsar cewa eh aman ba yanzu yanzu ba
Cike da kauna Gimbiya ta kalli yaran ta dan gyara muryarta ta ce" kunna ji?
Du dubanta suka juyo yi
Gimbiya ta yi masu murmushi ta ce" bana so a raba hali
Du sun fahimci inda ta nufa aman dan ta tabatar cewa sun fahimtar sai ta masu shiru daga haka itama ta ci gaba da dan daukan kambolin farar tana dan ci har tana mamakin kanta yanda aka yi take cinsa da yawa haka ko dan tare da mutane ne
An dauki kamar minti goma zuwa lokacin Har Gimbiya ta wanke hannunta, yaranma kananun ne basu gama cinye fararsu ba
Da salama suka shigo falon
Masu yi masu jagora ke amsawa da karfi karfi sunna fadin" ku shigo a hankali, Gimbiya na falo
Ku sada kanku kasa ku gaishe da mace daya tamkar da goma mama a wajen sarkin damagaram
Ku tako sannu sannu
Bakinta ta dan tabe tare da yayarta suke wace ke biye da jakadiyar dan aiwatar da abinda ake nuna masu
Sunna zuwa du suka nemi zama a kujera
Sai dai basu kai ga karasa nufinsu ba da sauri Jakadiya ta tare tana nuna masu wajen da ya dace su zauna domin idan ka ga Gimbiya na sama wani na sama toh sarki ne, sai y'ayanta dake hayewa jikinta su dora kansu a saman kafarta, su kansu idan ka ga sun layi da ita to a saman diner ne
Ko yanzu Zahrau ce kwonce kanta saman cinyarta ita kuwa tana shafa mata gashin kanta
Daga kasa kuwa Najeeba ce ke gyara mata akaifunta tana ta kankare mata su tana yanke mata duda ba wani datin dake jikinsu aman ta saba idan tana zaune ko ta dora rigimar sai ta yi mata kitso, ko ta kama gyare gyaren mata su akaifu ne da sauransu
Komawa suka yi wajen suka zauna domin wajenma waje ne mai alfarma dan ba kasa ne dabas ba aman duda haka ita ta so ta hau kan kujera dan a ganninta ai ita matar yayanta ce
Yayarta ta fara mika gaisuwa, kafin itama ta buda bakinta cike da yatsina ta ce" Fatan kun wuni lafia, yaya aka ji da hakuri?
Gimbiya ta dan dauki lokaci kafin ta lumshe idannuwanta, hakan ya sa Jakadiya fadin" Alhamdulilah, Gimbiya ta amsa Hakuri an gode Allah
Da kallo ta bi Jakadiyar sannan ta sauke kan Gimbiya
Sai ta ji shakarta ta shigeta domin irin kamalar dake tatare da fuskar gimbiya ba zaka iya takata kai tsate ba komai rashin kunyarka dan ba lalenema ka ji muryarta ba idan ba hakan ta so ba
Idannuwanta ta dago ta sauke a fuskar Zahrau wace ke iya gannin hakan
Dan mukewa Zahraun ta yi tana gyara gashin kanta ta bi kannenta da kallo baki dayansu, kallon nan da ake kallonka kuma a kalli mutun
Du yawanci sai da suka dan turo baki kafin a hankali da daidaya suka shiga gaisheta, gaisuwa kamar haka" barka da yamaci, fatan kun zo lafia?
Bakinta ta tabe tana dan jijiga yarta dake bayanta wace ke ta ihun a sauketa tun da ta ga yan uwanta aman uwar ta ki kunceta dan haka sai take kukanta irin kannanun kukan nan
Basu wani jima sosai ba, ko gaisuwar yaran ba yanda ya dace ta amsa ba yayarta dai ce ke amsawa kafin su mike su juya su fita
Sauri sauri take har suka karasa fita waje sannan suka shiga cikin motarta da suka zo da ita
Sai da ta kama hanyar gidan iyayenta dan cen suka nufa tana ta jan wani uban tsaki
Ita dai yayarta tana ta jijiga yar da ta ki yin shiru tana kiran sunnan yayanta dan saurayin
Sunna karasawa suka sauka suka shiga ciki
Mamansu dake shanya hijab din yar yarinyarta ce ta dago tana dubansu ta ce" aa, me ya samu kishiyar ne haka take wantsala kuka tun daga waje?
Yayar Mardiya ta mikawa mamansu yarinyar ta zauna tana dan tabe bakinta ta ce" mama, anya kuwa Mardiya ba tana hada mu da y'ayan mijinta da kanwar mijinta dan ta kasance mai son kanta bane?
Da sauri Mardiya ta dubeta ta ce" wani irin ina hadaku da su?
Hararanta ta yi ta ce" kwarai kin ji abinda na fada! Mardiya du irin rashin mutuncin dake tsakaninki da yaren nan sai na ga da sauki tunda har zasu budi bakinsu su gaishe ki, sannan ke maimakun ki yi masu amsa irin ta uwa ko dan idannuwan mamansu sai kike wani binsu da harara
Ke dai kece mai neman fitinar a bayane domin ni dai ba fada min aka yi ba ni na raka ki
Mardiya ta zaburowa Nusaiba tana fadin" zaki min shiru ko sai na ci uwarki a nan yarinyar nan?
Yar ta yi shiru tana kwontar da kanta saman kirjin kakarta ta kai dubanta wajen yayarta da yannayin fada ta ce" malama kar ki wani fada min haka dan ke baki san abinda nake ciki ba!
Yanzu dai a gabanki zuwa muka yi zamu hau kujera aka hanna mu aka nuna mana kasa muka zauna
Sannan kina ganni mu muka buda baki muka fara gaisheta bayan mune ya dace ta gaisar! Da kike maganar yaran ba sai da ta harari katuwar guzumar ba sannan suka gaishe mu ba?
Itama idannuwan ta ruko mata ta ce" kin fa san bana tauye gaskiya ko a gaban waye, ba zan boye gaskiya dan kina kanwata ba
Me kike so? Ki hau kujera ki layu da Gimbiyar Damagaram? Uwar sarki ce fa Mardiya baki da hankali ne? Ke ki kasance da ita a waje dayama ai arzikin arziki kika ci! Kuma maganar kujera ba a kasa aka sauke mu ba, na lura wajen saukewar an dora mu mafi karamci ne a cikin waje uku ne
Da kike maganar sai da ta harari yara sannan suka gaishe ki inaga ashema da tarbiyarsu yaran dan har an isa a sakasu ko a hanna su duda kuna cikin haki na gaba da tsanar junna?
Ke ki rufawa kanki asiri ke kin san cewa Allah ya baki dama, na rantse da Allah da ace kin sada kanki da matar nan da na tabata kun samu kusanci da fahimtar junna yanda ya dace, da ke ya dace a je a yiwa gaisuwar nan ba wai na tirsasaki na kaiki mu yi dan zama mu tashi ba
Haba Mardiya, ke kin san waye mijinki, igiyar aure daya ta tsinke tsakaninku, ke kin san kafin ki shiga gidansa da manufarki ta yin hakan, kin shiga gidansa ne dan ki rama kwace maki saurayi da y'arsa ta yi, kin shiga ne dan ki muzanta rayuwarta ki hanna mata zaman lafia da kwonciyar hankali
Baki shiga dan ki haihu ba
Baki shiga dan ki jima da shi ba,
Da biye biyen abokansa suka shunna masa ke ya aura
Ke kin san kina cin ribar baba malan ne
Ki kiyaye Mardiya, ki kiyaye dan wannan kadai ya isa ya shaida maki cewar Allab na tare da shi, kwarai kina haye masa da izgili kala kala aman Allah ya hanna rabuwarku, ke kanki nan da ya sake ki saki daya a nan kika ringa zuba mana hauka sai da muka neme shi aka mayar da ke
Kin je kin saba da rayuwar gidansa idan kika ce zaki balo ki fito kece da shan wahala
Ki duba ki ga jikina, kwoncen kayan da kika bani ne aman ni kaina na zama abar kwatance a cikin sa'a dan kina bani su ina ketawa ina shiga cikin jama'a har fadi ake kanwarta ce ke auren MUTALAB fa, me kika rasa a gidanki? Mijinki ba ke ba ko mu idan ya tashi tsokanarsa zai sako mu gaba ne sai an sha wasa da daria,
Kudi sai dai ki ba wani
A wajen kwonciya ya gaza maki ko a me? Mardiya idanma muzgunawar ne fa kin masu , ya dace ki gane cewar kece da faduwa idan kika ci gaba da rayuwa a haka domin ko a irin yanda kansu ke hade zaki gane mai shiga tsakaninsu fa walahi ba dai mutun ba sai dai Allah!
Mardiya ta zauna tana hucin maganar yayarya bayan baki daya gaskiya ta fada mata
Sai a lokacin mamansu ta kawo kujerar zama irin tayani tsegumin nan ta zauna tana kallonta ta ce" ke kuwa, rashin wayo ne ko rashin hankali ke saka ki aikata abubuwan nan?
Jiya yayarki ke ce min wai kin yiea yaren iyaka da taba Yarinyar nan
Ashe baki da hankali? Ke din kin isheta tuwo da miya ne? Ke yau ace mijinki na raye har ta kai aure yaran nan suka fita a harkarku yaya zaki ji? Ko macen nan ta isa ta yiea yarki kayan daki idan kina da hankali ai y'ayan miji abin so ne abin a jawo a jiki ne domin baka san waye wane ba, koda baka kwadayin lada ai kana kwadayin duniyar tunda ita ta rufe maki ido har kike tafka iskancin nan
Mardiya zan fada maki, ba zan kuma barin yarana shiga fadanki na iskanci ba
Da ace kece da gaskiya kin san wacece ni ko ni ba zan yarda a wulakanta min ke ba, aman na lura dadi ne ya maki yawa kike ihun Allah ya kasheki ki huta
Bana son ki yi nadamar haka,
Aman kuma dahuwar mutun mai kosai
Ita dai sauraronsu kawai take, ita ita ta san me take ganni da yaren nan
Yaren dake tunanin ita tsararsu ce? Yaren dake kiran sunnanta kai tsaye?
Muryar yayarta dake idasa shanyar mamansu ta ji da haushi haushi tana fadin" wai wani ita ya dace ta gaishe mu, matar da idan haihuwa ne ta haife ki dan kawai kina auren yayanta kuma tana matsayin shugabar garinkima sai kawai ta wani gaishe ki? Ai da na rainata kennan, ke da ko bakinta ta buda ta ringa mana zuba ni sai na raina mata wayau!
..........................................
Tsuru ne ta yi sanye da hijab baki har kasa mai hannu ta saka Anmy a gaba tamkar ta fashe da kuka tana kallonta
Muryarta na rawa ta ce" Anmy mana, dan Allah a bar tafiar nan na yafe
Anmy ta juyo da mamaki tana kallonta ta ce" NAJEEBA, a kan me za'a bar tafia gannin likita bayan zuciyarki na maki suka? Mai martaba zai yi fitar boye dan dole sai ya ga wani bincike a tsaye a gaban idannuwansa dan bai yarda da kowa ba, gashi kuma clinik din daya ne zaku je shikenan da daren nan sai na barki ki tafi ke daya ko a fasa? Ki fita a idona na rufe ba za'a fasa ba kuma tare zaku je kima dauko alkyabarki dan kin san ba zaki bi shi haka daga ke sai hijab ba ko?
Gabanta ne ya kara tsinkewa ya yanke ya fadi har tana dafe gaban nata, ita? Ta shiga motar sarki? Ta zauna a ina? Wato ya makure mata wuya ya karya mata kai ya halakata ya kasheta dama abinda yake nema kennan ya ga ta mutu? Bama wannan ba, ita da zata je wajen cen dan ta yi neman magana ta hanyar samun kula alakar soyaya da mijin matar nan idan suka je aka yi mata binciken a gabansa aka shaida masa lafiyarta kalau yaya zasu kwashe?
Ita kam ta rasa meye aikin wannan jarababen! Idan ba jaraba ba ko abin aunawar ka nemi a kawo maka ai kawo maka shi za'a yi har dakinka na baci ka yi aune aunen aman shine zai wani je da kansa?
Fuskarta ta kara shagwabewa ta ce" Anmy, to ya bani sakon mana na yo masa ni, ko kuma ki ce da shi ya tafi kawai ni fa na warke
Anmy ta dago daga danna watar da take tana magana da mahaifiyar Najeebar kan Najeebar ne kuwa uwar na so ta hasko mata ita a hoto ta ganta aman ta rasa ta yanda zata daukar mata ita ta harareta ta ce"
[31/03 à 21:38] Sadjida: 🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
19
Sai da Anmy ta harareta ta ce" NAJEEBA MUTALLAB, tashi ki dauko min alkyabarki
Najeeba ta kara turo bakinta ta mike jikinta a sanyaye ta dauko alkyabarta fara aman kuma adon baki ne ya fi yawa a jikinta ta saka sannan ta bade jikinta da turare ta dauki yan cenji da wayarta ta dawo falo
Jakadiyar dake duke ne ta shaifa mata cewa har sun fito ita suke jira
Kollan Anmy ta kuma yi, sai ta ga Anmy din ta dauketa hoto da wayarta tana dan murmushi ta ce" ki fan saki fuskarki mana kema an mata
Bakinta ta kara turawa gaba ta juya tana tafe a hankali tamkar wace kwai ya fashewa a ciki jakadiyar na biye a bayanta tana nuna mata inda zata bi din hanyar da zai bi ya fita ba budadiyar hanya bace
Gabanta banda faduwa ba abinda yake, har sai ta fara jin da gaske wani zazabi na son kamata da karfin gaske ba da wasa ba
Ita dai ta san ya tsaneta, duda bata san falilinsa na tsanar nata ba
Takan kama mugun kallo daga gareshi, harma da kallon da zata iya kiransa na kyama
Tun fa ta nuna mata motar sai ta ja ta tsaya kanta sade
Najeebarma ta tsaya tana kallonta, muryarta na dan rawa rawa ta ce " mu, mu je mana
Da sauri Jakadiyar ta dago, sai kuma ta mayar da kan nata tana dan girgiza kai ta ce" Allah ya huci zuciyarki amintacen sarki kadai ke shigowa wannan waje ko ZINARIYARMU bata taba saka kafarta a wannan hanya ba, domin hanyar boyayiyar fita ce ta sarki
Sai ta ji ta kara tsorata da bayannin jakariyar, hanyar boyayiyar fita? To a kan me za'a zo da ita nan? Ko dai a nan ne ya yi niyar kasheta ya huta?
Idannuwanta ta rintse tana jimke wayarta a hannunta
Najeeba mana, meye haka ne? Ki je, ki je kawai, ki yi tawakali da Allah, ba zai kasheki ba ......zuciyarta mai karfin ke karfafa mata gwuiwa, nan take matsoraciyar shawararta ta ce" aa, ki rubuta message ki bari a wayarki, idan aka ga kin bace shine! Dan mutumen nan shi kansa kama yake da aljannu!
Hannayenta na rawa ta fitar da wayar ta rubuta message ta yi seving a wayar nata sannan ta shiga karasawa jimin motar jikinta du a mace
Mutumen dake tsaye ne ya saka gabanta yankewa ya kara faduwa
Wani irin girma ne da mutumen tamkar wanda ya fi ka'idar tsayin dan adam
Gashi da wani irin jiki mai abin tsoro, fuskarsa kuwa zata rantse bai taba sallah ba dan ba annurin hasken sallah a tatare da ita ko daya!
Bude mata motar ya yi ba tare da ya furta ko A ba
Da sauri sauri ta daka dan tsale ta shige motar gabanta na faduwa ta zauna tana ta waige waigen tsoro
Wata kwalba ce ajiye saman kujerar daga tsakiya haka, kwalbar mai duhu ce sannan ga duhun cikin mota hakan ya saka sam bata gane ko meye a ciki ba
Cikin motar ba kowa sai wani irin sanyin AC din dake kunne da kuma wannan dadadan kamshin turaran nasa
Hannayenta ta dora saman cinyarta ta jingina da jikin kujerar ta saki wawuyar ajiyar zuciya da tarin sarewar dake adabarta
A hankali ta ringa furta kalamai kamar haka" ke kuwa ta haka zaki mutu ashe Najeeba? Koba motar zai yi ya ce na yi hatsari ko wannan katon zai saka ya dane min hanci sai na daina motsi? Wayo su auntyna zaku yi rashina, wayo yayana kana ina? Yau du ban ganka ba kuma ban nemeka ba, yayana ka