Showing 117001 words to 120000 words out of 228147 words
Chapter 40 - MAGE (Mai kwanciyar Daukar Rai) Book Complete Na Sajida complet.txt
hakama Nadia tana tare da aunty da wasu yan uwansu biyu manyan mata du sunna zazaune ne saman manya manyan kujerun falon sun cika sosai sosai kowace na dan murmushi idan sun hada ido da wata, su kuwa matan kowace kanta sade da alkyabarta
Wayar da ta dauka umarni ta bada kan a rako Najeeba da zahrau, da dayar matar sarkin
Tana kashewa ta kuma kiran SHAHEED
A lokacin an gama masa wani nadin ana ta binsa da turaruka ne
Tambayar da ta masa kan me yasa ba'a zauna a rumfa ba?
Amsa daya ya bata a hade cewar" Eumfar na dauke da hatsari ne
Ajiyar zuciya ta sauke, gaske ta ga dogarai da mai wasan maciji sunna tsaitsaye sun tsare ko'ina da alamu hayaki zai yi
Ajiyar zuciya ta kuma saukewa tana mai bin wajen da kallo
Waye? Waye ke son gannin bayan auren yaronta? *Shin yaron nata ake son gannin baya ko kuwa matan da zai aura?*
Ajiyar zuciya ta sauke haka kawai ta tsayar da dubanta kan mahaifiyar Zinaria wace fuskarta ba yabo ba falasa tana yake dai irin kar a ga kasawarta aman sam abin bai kai zuci ba
A kansa zuciyar Anmy kuwa tambaya take *GIMBIYA, shin abin iya kishin ya tsaya ko kun saka kanku a ukun rayuwar duniya da kiyama?*, da sauri ta ringa kore shaitan tana cire maganar daga ranta daidai lokacin da aka shiga shelar za'a shigo da NAJEEBA
Du dubansu suka kai banda Nadia, da kuma zinaria da suke nitse kawunnansu sade
Da mamaki Gimbiya ke kallon wa'inda suka shigo da ita, su biyu ne kawai wato kishiyoyinta sai jakadiya da wasu bayin dake tafe sunna zubar da flowers pink da fari a hanyar da take takawa
A haka har suka karaso wajen zamanta suka zaunar da ita sunna mai gyara mata abin rufarta kanta sade alkyabarta ta rufe gaban fuskarta
Kamshin turaranta tuni ya ringa kaiwa hanci hanci, du kuwa da falon kansa yana da kamshinsa aman kamshin nan nata ya rigaya ya gama kama jikinta sandal Rose na ruwa
Gaban Nadia ne ke dukan tara tara , a hankali ta rike hannun auntynta kanta sade tana jin zuciyarta na mata rawa sosai
Ita dai Gimbiya ta ki dauke idannuwanta, burinta ta san wacece a rufen nan? Dan yanda ta damu ta ga fuskar wace kiahiyoyinta suka shigo da ita ko Nadia bata damu da gannin kamaninta ba! Ina danginta? Shine abinda take ayannawa a ranta
Cen ta yatsine fuska a lokacin da ta yi tunanin yanzu haka wata diyar wani kasurgumin talaka ce aka lulube dan kar a gane
A hankali ta kai dubanta kan takalmin kafar Najeeba
Takalmin fari ne kal kal da shi mai dan gashishika kadan a samanta, sau ciki ne takalmin irin babuche, kyalkyalin dake samansa suma fararen ne sannan ya yi yar kwana kadan
Kana ganninsa ka san babar harka ce
Kuma daga idannuwanta ta yi tana juya su suka hada ido da Ummu
Irin yanda Ummu ke binta da kallo, ita kuwa sai ta kakaro murmushi ta sakarwa umu
Ummu ta yi murmushin itama kafin ta kara gyara zamanta ta kuma daga dubanta ta sauke das a kan y'arta, lalle yanzu ta yarda yarinyarta ta shigo cikin mata, ko Najeeba na so ko bata so sai sun zauna sun yi magana!
Ya kara wasu mintunnan sun kai talatin kafin a shiga fadin" *GYARA KIMTSI, GYARA KIMTSI, A GYARA ZAMA A NUTSU, MAI DAMAGARAM ZAI SHIGO, DAN SARKI JIKAN SARKI, SARKI MAI WUKAR YANKA, SARAUTA GADO CE, DAN MUN GADA BA DAN HAYE BA, GYARA KIMTSI GA GURNANIN ZAKI TAFE, GYARA KIMTSI GA FARI MAI FARAR ZUCIYA FARAR ANIYA NAN TAFE, JINNI NA BAREBARI DA SHUWA ARAB, KAI DAYA MUKE DA KAI TALLL TAMKAR GOMA*
Irin abubuwan da aka ringa fada kafin ya sanyo kansa ya shigo cikin nutsuwa
A shigowarsa ne baki daya du wani turare ya risina,
Du irin kamshin amaren sai nasa ya doke su domin an masa wankan turare ne kamar ba gobe
Tun da ya shigo du suka sada dubansu
Cike da takun kasaitar da du takunsa daya sai zuciyoyin matansa sun amsa har ya kai ga kujerar da ta fi kowace alfarmar ya yi bismillah sannan ya samu ya zauna
Sai da ya ringa bin wajen da kallo daya bayan daya, da hannunsa ya yi umarnin dogaran su juya
Suka juya a tatare sannan ya ja numfashi a hankali ya furta" *ASALAMU ALAIKUM*
Wannan salama tasa , itace sanadiyar da ta saka du wata halita a wajen dago kanta
A daidai wannan lokacin ne idannuwa suka ringa garwaya da junna, da yawa sun dauko amsa salamar ta katse daidaiku ne suka kaita har karshe kafin idannuwan matan nan uku su sarke da junna
Kamar hadin baki, koda yake idan abu ya dakeku haka ne, a tatare suka zabura a wajen da bai dace su zabu tsayen ba, kowace cike da tsoro da mamakin abinda idannuwanta ke ganni a zaune
A rikice ZINARIA ta nuna yatsarta kan NAJEEBA wace hular alkyabarta ta fadi kan kafadunta itama kamar sauran bakinta na rawa ta ce *KE?*
Najeeba ta kalleta na second biyu ta juyi wajen Nadia cike da matsanancin mamaki ta nunata da yar yatsarta itama ta ce *NADIA?*
Nadia kam gaba daya mikewar da ta yi na tsoro ne, domin bata san zasu ga junna a nan kusa ba hakan ya saka ta tsorata da ido hudun da suka yi da Najeeba bakinta na rawa sosai ta budi baki ta ce"
Morning peopleπ
[31/03 Γ 19:24] Sadjida: π§π»π§π»π§π»π§π»π§π»π§π»π§π»π§π»π§π»π§π»
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
π§π»π§π»π§π»π§π»π§π»π§π»π§π»π§π»π§π»π§π»
*Na*
*SAJIDA*
π«β¨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*π
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_π€
β *[ T.M.N.A]* β πποΈ
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
38
A rikice Nadia ta ce" NAJEEBA, dan girman Allah ki saurare ni na maki bayani."
Auntynta ta ja hannunta da karfi
Warce hannun nata ta yi ta ce" aa, kin ga, ki bari na fad'a mata, walahi tallahi da na san mijinta ne zan aura da ban yarda na yi wannan gangancin ba."
Irin yanda take bayannin hankalinta tashe , sannan har ta fara takowa zata k'arasa kusan Najeebar da saurinta.
A wajen kusan kowa hankalinsa na kanta banda Zinaria da mahaifiyarta da suka gama mutuwar tsaye a lokacin da suka gama fahimtar a yau wata bak'ar fatar, daya daga cikin cousins din Mai Damagaram, y'ayan Mutalab , wace suka fi takun sak'a da ita ta zama mata a wajen mai Damagaram, ZINARIA ta juya wajen mamanta, a fili cike da kidima ta ce" ashe wannan ce ya aura? Ya rasa wace zai had'ani kishi sai wannan marar kunyar yarinyar yar wulakanci? Ya rasa wa zai d'auko min sai wannan bak'ar yar mai idanuwa kamar na mujiya?" Kuka ta fashe da shi a fili wanda da sauri yayarta ta kamata ta aniya mayar da ita saman kujerar
A rikice mahaifiyarta ma ta kamata kasa kasa take fadin" ki min shiru, ki bari mu fita walahi ba zai yiwu ba!"
Kamar wa'inda suka samu TV dubansu ya dawo wajen NADIA da ta karaso kusa da Najeeba.
Hannunta na rawa ta kamo hannun Najeeba, auntynta kuwa kamar zata k'urma ihu dan takaici.
A birkice ta ce" ke kin san na san cewar bakya son kishiya, ke kin san nima haka ne, kuma ke kin san ke kika min alk'awarin rabani da kishiya ko da na auri miji mai ita, Najeeba, kin san ba zan taba auren mijinki kaina sane ba, koda maye nake da sani ba zai taba faruwa ba, ni ba maciya amana bace."
Najeeba ta lumshe idanuwanta tana jin yanda suka yi mata wani irin nauyi.
A hankali ta ringa satar kallon mutane
Kyam idannuwansa a kansu. Du abinda ke faruwa da ido kawai yake bi tamkar baya wajen.
Haka su Anmy har baki Anmy take saki tana bin ikon Allah
Zinaria kuwa sai danarta ake kamar zata hau bori.
Idannuwanta ta maida wajen Nadia
Sai da ta lumshe su sukai wani luuu sannan ta bud'e su.
A hankali ta ce" ke, daina irin haka mana, meye a ciki dan kin auri miji? Na ce maki na damu ne? Bayan kema ya d'auko Barira, ina taya ki murnar malakar abinda kika jima kina marari, ke kin san ba nawa ra'ayin kennan ba dan haka kar ki bani kunya kin saka ana kalona!"
Maganarta a fili ta yi ta, cikin kwonciyar hankalin da ya zama jikinta, duda daga kasa wani irin jimkar hannun Nadia ne ta yi wanda ya saka Nadiar shiga wani rud'un
Ta ce babu komai, irin magangannunta sun bayana karara ita auren kansa baya gabanta, aman kuma irin rikon ta mata ta tabata akoy wata a kasa.
Hannun nata ta saki ta koma ta zauna tana mai gyara alkyabarta da kyau kafin ta kuma dago dubanta ta sauke kan Nadia dake tsaye kanta
*Zaki ci ubanki!* shine abinda zuciyar Najeeba ke ayannawa
Na tsaye shi, baya gabana, aurensa baya gabana, aman ko kashin da na yar ya haramta gareki domin aminci ba karya bane! Ta kuma furtawa zuciyarta
Ji take baki daya ta gama muzanta a idannuwan mutanen dake wajen, du wanda ya santa, to fa ya san Nadia
Anmy da baki daya jikinta ya yi sanyi ta kai dubanta wajen Sultan
Irin kallon da yake ramkar kallon jin dadi, irin yanda ya maida hankali a kallon dramar da ta wakana, ko take kan wakana kamar wanda abin ya masa dadi
A hankali ta sada kanta
Ba'a taba hayaniya mai yawa haka a gabansa ba, baka isa ka yita haka a gabansa ba tare da ya maka abinda zai firgitaka ba, aman sai gashi ya yi shiru ya kyale har Najeeba ta fadi maganar da bata so ta fadeta a gaban kishiyoyinta ba, kwarai karara ta nuna bata yi auren da zata yiwa kishi ba!
Me ya sa Shaheed? Me ya sa ka auro aminiyarta? Shin amsa min ka yi dan baka da yanda zaka yi da ni ne ko me? Ni kiwa zan nuna maka ba sarauta ba,, ko me ke kanka ni na haife ka!
Ummu kam da kallo take bin kowa, har lokacin da auntyn Nadia ta karasa ta kama hannunta ta ja ta ta mayar da uta wajenta tana jin inama idan ta wanke fuskar Nadia da mari ba abinda zai faru? To da yau sai ta fafale fuskarta da mari sannan ta yi tirr da ita, bata taba bata kunya ta sakata jin ashe Nadia sakarai ce bata taba sani ba irin na yau, lalle Nadia sakarai irinta babu
Ashe yarinyar da take haukan tsoron ita batama damu da mijin ba? Ga alamu karar sun nuna kamar auren dole ne akai mata?
Zaunar da ita akai
Sai a lokacin ya dauke idannuwansa daga kanta
Kwarai da farko, wani murmushi ne ya subuce masa a lokacin da ya hangi dukan da gannin Nadia ya yi mata, irin yanda su duka biyun suka rikice da ganninta a gabansu kuwa ya bashi mamaki duda ya san Zinaria basa shiri aman bai taba tsamanin kawar tata tsoronta take ba, aman a kan me take tsoronta? A hankalo kallonsa ya koma na son karantar ainahin abinda take ciki maimakun wanda yake fitowa daga bakinta
Murmushi ya kuma saki irin na yake din nan a lokacin da sak kunnayensa suka jiyo masa irin yanda ta yi magana da nuna bata damu da gannin kawarta aminiyarta a matsayin kishiyarta ba, wace suke raba mafarkin kasancewa su kwalin kwal a gidan miji
Dubansa ya maida kan Zinaria, kanta sade yake, sosai an janyo alkyabarta an rufa mata dan kar a ga fuskarta
Tausayinta ne ya ji har cikin ransa, irin magangannun da ta yi kwarai sun bashi mamaki, meye ilar bak'ar fata ne? Bai san me ya sa idan hankalinta ya tashi take barin bakinta ya ringa fadin du abinda ya zo zuciyarta ba
Ya tabata da ba dan mamanta ta rufe mata baki ba, da zata dora wata kalmar mai zafi ne a kan kalamanta, menene a kishiya ne da mata ke tashin hankali dan za'a yi masu? (Han, baka yi rayuwar neman aure da wani bane, a wajen da kake soyaya ranka shi dade)
Kuma kai dubansa ya yi wajen da aka zaunar da Nadia, tsuru Najeeba take kallo hakan har ya so ya bashi mamaki, ta yaya mace zaki yi sake har a ga rauninki haka? Kansa ya girgiza sai kawai idannuwansu suka sarke da na Anmy
Irin kallon da ta masa ya saka shi sada nasa idannuwan wanda hakan ke nufin yana tausarta ne
Matar sarkin agadez ta tsakiya ce ta duka sosai ta kama hular alkyabar nan ta dora saman kan Najeeba,
Kanta kasa ta zagayo ta kama hannayenta, hannunta dayan suka kama ya kasance tana tsakiya
Anmy na kallonsu, sarai ta san abinda zasu yi, ita dai Najeeba bata musa masu ba , binsu ta yi a hankali suka nufi wajen da yake zaune
Sunna zuwa da hannayensu suka kaita kasa ya kasance ta duka a gaban kujerarsa
A sanyaye Zahrau ta ce" Allah ya huci zuciyar Sultan, Allah ya huci zuciyar mai damagaram, Gimbiya Najeeba na neman afuwar daga murya a gaban uban gidanta
A hankali da mamaki fal ramta ta dago ta hangi fuskar Zahrau, iyeah, yaushe ta koyi irin abubuwan nan?
Kishiyarta ce ta budi baki itama cikin kara sada kai kamar yanda suka tsugunar da Najeebar ta ce" Allah ya huci zuciyar mai wukar yanka, Allah ya saka sasauci a hukunci takawa, sannu da karin hakurin halayan mata , Allah ya kara maka lafia Gimbiya Najeeba na neman afuwar mikewa a lokacin da baka bada izini ba
Idannuwansa kawai ya lumshe masu bai ce komai ba suka mike a hankali suka koma
Sunna zama su Zinariama suka mike da ita suka nufi wajensa
Baki dayansu suka zube suma, cike da kwarewa a lamarin bada hakuri da kirari mahaifiyarta ta taushi zuciyar sarki da neman afuwa
Idannuwansa a kan Zinaria
A hankali ya budi bakinsa kasa kasa ya furta" Allah ya sanyaya zuciyar uwar gidan SHAHEED
Idannuwanta ta lumshe jin dadadar muryarsa a kanta, mahaifiyarta kuwa har sai da ta kara jinjina ta kara daga murya tana fadin" Zuciya ta sanyaya Gurnanin zaki, Allah ya kara girma, uwar gidanka ta amsa ta gode rarashi
Da biyu ta yi hakan, wa'inda take so su jin kuwa sun ji, a haka suka koma
Sai da Aunty ta kamata ta mikar da ita, ita kanta kafafuwanta rawa suke, sai wata datijuwar daje gefenta suka saka Nadia a tsakiya suka nufi wajen baki dayansu a tsorace domin basu taba kusanci irin haka da sarki ba, sannan basu san al'adun gidan sarautar ba
Sai da suka karasa suma suka tsuguna
Hannayensu du suka hade kamar sunna adu'a kafin su shiga hadin baki wajen maimaita abinda suka ji ana fada masa
Murmushi ya yi kafin ya gyada masu kansa
Auntyn Nadia ta ringa sauke ajiyar zuciya, a ranta kuwa fadi take" Allah ka sa mu tashi da wuri lafia daga wajen nan,
Gannin basu mike ba ya saka ua rage muryarsa sosai ya furta" ku koma mazaunin ku
Sunna komawa suka zazauna tadar gaba wace a cikinta ne ake fadawa junna magana ta hanyar firgitatun kyaututukan da matayen zasu yiwa junnansu
Wannan tada, zinaria ta san da ita, kuma ta shiryawa hakan, sai dai a yanzu a wajen mahaifiyarta ta kara ninka kyautar dan tana son ta fara kai mari da firgitatun kyaututukan da zata gabatar ba dan komai ba sai dan ta nunawa y'ayayn talakawan nan kudin kansa hawa hawa ne, sannan sarauta fa gado ce!
Yayar ZINARIA ce ta fito cikin shirin wata mahaukaciyar shada ruwan pink, an cancada mata mak'up tana baza kamshi sosai
Da alkyabarta baka mai shara shara wace ta fitar da tsarin gashinta karara
Cike da yanga dauke da jaka ta karasa Tsakiya
Jakar nan ta buda ta duka kadan ta ciro wata katuwar sarka ta zinaria kafin ta hada da chek mai dauke da kimanin kudi cefa millipn biyar biyar ya zama sarka biyu da million goma
Sai da ta dadaga ta nununa sannan ta buda bakinta da hausar buzayen da bata zauna ba ta ce" *Alhamdulilah, ZINARIA na yiwa Amare barka da sauka da fatan sun shigo lafia, Zinaria ta sauki Amare da ruwa sansanya da wajen zama harma da kyauta a ja jari*
Karin chek din shine karin da suka yi, sai maganar a ja jari da suka d'ora wace sarai magana ce cikin hikima.
Murmushi Anmy ta yi kafin yayar Zinaria ta dauka ta je gaban Anmy ta tsuguna ta ajiye sak'on ta k'ara gaishe da Anmy din sannan ta koma mazauninta.
Dubansa ya kai wajen su Nadia,
Sai kici kici Aunty take da jaka ita batama san inda ta zuba chek din da ya bada Jakadiya ta kawo masu ba, sarai ya san a wannan wajen za'a so nuna hali na wulakanci shi ya sa ya bada chek biyu wanda ya tabata wannan uwar handamar ba zata taba iya ciro kudi irin haka ba.
A lokacin da ta fitar da takardun sai da ya lumshe idannuwansa sannan ya ci gaba da kallo
Sai a lokacin ta kalli takardar, sai da ta zaro ido tsabar kad'uwa har da yan yatsunta ta kara irga ziro din dan tabatarwa.
Ajiyar zuciya ta sauke ta nufi wajen itama
Tana inda inda ta ce" NADIA na godiya, sannan ta bada kyauta a baiwa kishiyoyinta kamar haka, million muraran million har million ashirin ashirin... *su ja jari* (kar ku manta ita ba sannin me ake fad'a ta yi ba, kokari ta yi ta kamanta)
Itama ta nufi wajen su Anmy, sai da ta duk'a da hannu biyu ta mik'a masu sannan ta mik'e ta nufi wajen Nadia da baki d'aya ta zaro idanuwanta da mamakin kud'in, kan ubancen kaya sa, wani abin sai manya, wani abin sai kishi, yo ita uban wa zai bata wannan kud'in ta yi wasa da su? Ko hauka take, ba dai dan ta birge kishiya ba walahi, kai, inama inama daga ita sai Zinaria ne suka shigo? Inama inama hakan ne?
Kwarai gwuiwar Zahrau ta yi sanyi a lokacin da ta tuna kudaden da suka zo da su kwata