Showing 237001 words to 240000 words out of 281103 words

Chapter 80 - ZAGON KASA Book Complete Document by Khadeeja Candy .txt

28 Dec 2024

61238

ƙafarsa ɗaya kan ɗaya yana kallon tv, sam ta manta ma bata kunna masa tv ba. Ta dire turen gabansa tana faɗin.


“Na manta ban kunna maka kallon ba”


“Ai na kunna ni ba baƙo ba ne”


Yayi maganar cikin wata kalar murya.


“Ka zo unexpected, ba a shirya maka komai ba”


Ta faɗa tana ɗora fruit salad ɗin da Drink a saman wani ƙaramin tebur da ta janyo ta aje gabansa.


“Tea or coffee?”


Ya daɗe yana kallon gashin kanta da ya buɗe kamar ba zai ce komai ba.


“Da rana”


“Ban san abunda zan kawo maka ba ne... Wai ka ɗan ci kamin na girka maka abinci”


Ta faɗa kamar wacce ta ji kunya.


“Ban zo dan ki girka min komai ba, i just come to see you, kuma na gan ki hankalina ya kwanta”


Ya koma saman kujera ta zauna tana murmushi. Ya sauko da ƙafafunsa ya ɗauki fruit salad ɗin ya fara sha, still idonsa na kan ta yace.


“Ba ni labari”


“Kamar na me...?”


“Komai da komai”


“Nothing new”


“Seriously! What bought Lamido here?”


“Oh... He's my new driver”


“Driver...?”


“Yep Abbah ya kawo min shi ɗazu, zan fara zuwa scul Monday shine Abbah ya samo min sabon direba”


“Nice”


Ya faɗa kamar ba komai. Wayarsa ya fiddo ya kashe flash camera sannan ya shiga ɗaukarta hoto ba tare da ta sani ba, dan yasan idan har yace zai ɗauke hoto ba zata bari ba, kuma sisters nasa da Ummi sun dame shi akan suna son ganinta.
Haka suka ɗauki dogon lokaci a falon ita da shi babu wanda ya iya sake cewa ɗan'uwansa wani abu, kowa da abunda yake tunani, Namra gaba ɗaya hankalinta ya tafi akan halin da Uzair yake ciki, shi kuma hankalinsa ya tafi gurin Lamido dan yana ganin kamar zai masa zagon ƙasa ne, taya zai zauna ya zuba mata ido shi ya riƙa driving ɗinta scul ya sace zuciyarsa shi ya bar shi a nan.


“Zamu iya gaisawa da Abbah?”


“Yeah Yeah yes, bari na kira shi”


Ya miƙe tsaye tana taɓa kanta dan gaba ɗaya hankalinta ya tafi gurin wacan tunanin nata.


Ƙofar da zata sadata da ɗayan falon Abbah ta nufa, tana tura ƙofar falon ta jiyo muryar Abbah sai ruwan bala'i yake, shesshekar kuka na tashi, cike da faɗuwa gaba ta shiga ɗakin Abbah, sai ta samu Anty Amarya da Hajiya Barau zaune ƙasan carpet ko wannensu na kuka. Hajiya Barau ta rashi tana kuka ta fice daga falon, Anty Amarya ta kama ƙafafun Abbah ta riƙe tana kuka.


“Dan Allah karka aikata abunda zaka dawo kana nadama a lokacin da bata da amfani, dukanninmu ƴan'adam ne kuma ajizai masu yawan laifi da kuskure”


“Idan baki daina saka min baki a lamarin gidana ba, ke ma zaki haɗu da ɓacin rai na...”


Juyawa Namra ta yi ta koma jikinta a sanyaye, ba tare da ta kalleshi ba tace.


“Maybe idan ka sake dawowa zaku gaisa”


“Why...?”


“Abbah is not in the mood now”


Hawayen dake idonsa ya zubo muryarta kuma ya soma rawa alamar kuka yana tare da ita. Da sauri Abdool ya taso ya nufo inda take tsaye.


“Faɗa min Abnam, minene? You can't hide the truth”


“Mutumen da na taɓa baka labarin yace ƴana so na kuma ɗan luwaɗi ne, yanzu haka yana asibiti cikin mawuyancin hali, kuma ɗazu ya tara mu ya faɗi gaskiyar duk abunda yayi, ciki har da asirin da ya haɗa kai da Aminiyata Amira yayi min akan na gudu na bar gida, sai gashi asirin be kama ni sai ya kama Amirar Amiyar tawa ita ta gudu ta bar gidansu bata dawo ba sai ranar da na dawo garin nan...”


Ta ƙarasa cikin kuka.


‘Amira...’


Ya maimaita sunan a zuciyarsa, yana kallon zubar hawayen gimbiyarsa.


“Wannan ba abun kuka ba ne abun dariya ne da murna, amman komai daren daɗewa sai gaskiya ta bayyana kuma mai haƙuri mawadaci”


“Aminiyata ce fa, ace ta min irin wannan aikin ai dole na yi kuka, babu yadda ƴan'uwana ba su yi ba akan na rabu da ita amman na ƙi”


“Kin share hawayen ki, shiga ciki ki canja kamin na dawo, zan nuna miki wani abu”


“A'a Abbah ba zai bari ba”


“Zai bari just go”


Be jira amsarta ba, ya juya ya fice yana danna wayarsa.












MANAGE IT PLEASE 🙏
[7/18, 8:14 PM] Khadeeja Candy♥: *83*


Cikin nishaɗi da walwalah ta isa gida, tana faka Motarta Hajiya Sadiya ta fito hankalinta a tashe ta nufi inda take tsaye ta riƙa ta.


“Daga ina kike Nabila?”


“Mun ɗan fita ne da Asim, Lafiya”


“Na kira wayarki a kashe, ina kika je ne?”


“Munje cin abinci ne”


“Me kuka ci? Talk to me”


Ta riƙa fuskarta tana girgizawa. Itakam mamaki duk ya cika ta tashin hankalin da ta gani a fuskar Mahaifiyarta ta ruɗa ta.


“Miyasa kika tambaya?”


Hannunta ta riƙa ta jata suka nufi cikin falon sannan ta zaunar da ita saman kujera itama ta zauna fuskarta da damuwa ta ce.


“Ina tsoron kar ya baki wani abun ne, kin san mutane ba abun yarda ba ne”


“Hmmm Momi Asim ba irin mutanen da kike tunani ba ne, yana da kirki sosai”


“Ba daga nan take ba, Nabila ina fatar be baki Apple kin ci ba?”


“Ya bani apple kam kuma shi ma ya ci”


Ta dafa kanta ta sauko ƙasa ta riƙa hannayen Nably tana kuka.


“Wane irin apple ya ba ki? Na shiga uku na lalace, ya kai ki ya baro Nabila shi kenan, tawa ta ƙare”


“Momi me ke damunki ne?”


Kuka ta yi sosai har hankalin Nably ta tashi sannan ta labarta mata abunda ta shekara da shekaru tana aikatawa. Kuka Nabila ta saka zuciyarta ta cika da baƙinciki.


“Asim yayi daidai idan har da gaske ya bani apple ɗin na ci, na cancanci mutuwa a yanzu, ke ba uwa ba ce Momi, kin shirya kashe wata saboda tsiratar da ƴarki, kin shirya aikata komai saboda duniyarki”


Ta tashi da gudu ta nufi ɗaki tana kuka, saman gado ta zauna tana kunna wayarta, saƙon da ya shigo mata be bata mamaki ba saboda momi ta faɗa mata komai tun kamin Asim yayi mata wannan saƙon.


_Apple ɗin da kika ci Mahaifiyarki ce ta ba ni tace na kaiwa tsohuwar mamata, bayan kuma ta san na mutuwa ne, mahaifiyata ta ci ta mutu dan haka na yi ɗaukar fansa da ke_


_Ba ka yi kuskure ba Asim, Mahaifiyarta ta cancanci fiye da abunda ka yi mata, ni kuma na yi kuskuren yarda da kai, amman har gobe ina son ka_


Shine amsar da ta mayar masa, ta share hawayenta ta kwanta saman gado tana kallon window. Yayinda Hajiya Sadiya take tsaye a falo tana ta buge-bugen waya akan a taimaka mata kar ƴarta ta mutu, idan ta kira wannan tana kuka ta kira wannan duk ta bi ta haukace sai kuka take kamar zata tashi gidan. jin kamar ƴarta na tari yasa ta bar falon a guje ta nufi ɗakin tana kiran sunanta, amman ina Nably ta yi nisa har bata iya magana, duk ta ɓata gadon da aman jini kamar wacce ta amaye hanjin cikinta. Hannayenta biyu tasa tallafo kanta tana shafata.


“Nabila karki ta fi ki bar ni ke kaɗai kika rage min, na shiga uku na saka kai na a halaka, wannan baƙar ƙungiya bata min rana ba”


Kallonta kawai Nabila ke yi a wahalce tana numfashi da ker, hawaye na bin fuskarta har ta amsa kiran mahallicinta.


Wani uban ihu Hajiya Sadiya ta saki ta fita a ɗakin a guje, tana kaiwa harabar gidan ta zame ta faɗi ƙasa ba sumammiya.




UZAIR POV.


Wasa-wasa yau kusan talatin da ɗaya ana abu ɗaya babu sauƙi, sau biyu ana fita da shu waje amman babu abunda yake canjawa kuma ko ina aka je abu ɗaya ake faɗa cewar ba zai sake tafiya ba.
Tun ranar da ya aika Tahir be gane kan maganarshi ba, sai yawo yake ta masa da hankali, kullum da kalar abinda zai faɗa masa, kuma duk tsowon lokaci Yasmin bata taɓa taka asibitin da sunan ta zo ganin Uzair ba, abunda ya bawa kowa mamaki ciki har da Abbah. Ranar wata Lahadi duka ƴan'uwa suka saka ta gaba ana mata faɗa da tambayar dalilin ƙin zuwa ganin mijinta, amman ta kasa furta musu komai sai kuka take, a dole tasa suka ƙyaleta suka saka mata ido.


Ana sauran kwana biyu Abbah ya sake fitar da shi india, Tahir ya zo dubasa daman duk bayan kwana biyu yake zuwa ya gansa.
Yau ya fi bashi tausayi fiye da ko yaushe, ya rame sosai kamar ba abokinsa ba, wai yau Uzair ne kwance a nan baya iya komai, lallai duniya abun tsoro ce. Hawayen da ya gani a idon Uzair ya tashi hankalinsa sosai hakan yasa yau ya yanke shawara faɗa masa gaskiya, da kuma ba shi shawarar abunda yake tunanin zai zame masa mafita.


Ajiyar zuciya Tahir ya sauke yana kallon Uzair ya ce.


“Na yi ta maka wasa da hankali akan maganar Malamin nan, magana ta gaskiya Uzair mutumen baya raye, lokacin da naje gidansa na samu ranar ake sadakan bakwai nasa, na ɓoye maka ne saboda karka tashi hankalinka”


Wasu zafafan hawaye ne suka zubowa Uzair, ya haɗe yawun bakinsa cike da tausayin kansa ya ce.


“Tawa ta ƙare kenan! Haka ƙarshe na zai zo ni kuma? Ina ma ace mutuwa na yi na huta...”


Tahir ya dafa ƙafaɗarsa ya matsa kaɗan.


“ina tunanin abunda ya fi, ka samu Namra da iyayenta ka yi musu bayanin komai, kuma na nemu yafiyarsu, wata ƙila abunda ka aikata ne haƙƙi yake biye da kai, idan kuma har ba haka bane, to Amira ce ta yi maka asiri, idan zaka fallasa komai ka fallasa tare da Amira idan tana gurin, hakan zaisa guiwarta ta yi sanyi ta je ta kare abunda ta yi maka”


“Zan aikata Tahir indai har wannan zai sa na samu lafiyata, amman ya za'ayi Amira ta zo nan? Da wane ido zan kalli Abbah na ce ina son magana da Namra?”


“Zan kawo maka Amira, Namra kuma ka faɗawa Abbah kana son ganinta tare da Abbah”


Ya jinjina kai, shi dai ya shirya yin komai akan lafiyarsa, dan bai jin zai jure zama a irin wannan rayuwar. Bayan Tahir ya fita Mahaifiyarsa ta dawo ɗakin daman yanzu ita ce take jinyarsa ita da wani ƙanensa da kuma ƙanwarsa.


“Umma ina son ganin Abbah da Namra”


Ta kalleshi cike da mamaki.


“Ta maka me? Yarinyar da tun da ka kamu da rashin lafiyarnan bata taɓa cewa tana gaisheka ba balle ta zo duba ka ita zaka nemi gani yanzu?”


“Zan yi wata magana da ita mai muhimmanci, dan Allah ki taimaka min itace kawai mafitar wannan ciwon da nake yi, da ta zo zan samu sauƙi”


“Ban gane ba? Kamar ya itace mafitar ciwonka? Kana magana kamar wanda baya cikin hayyacinsa, Uzairu cuta fa ba mutuwa ba ce”


“Ki taimaka min ki kawo min ita mu yi magana zan faɗa muku komai,ciki har da dalilin daya sa Yasmin ta ƙi ta tako asibitin nan”


Da farko Umma ta ɗauka zafi ciwo ne yasa shi wannan maganar, daga baya kuma sai ta fahimci yana cikin hankalin kansa, sai dai maganganun da yake sun ɗaure mata kai.




Tahir na barin gidan ya nufi gidansu Amira, kamin ya isa sai da ya kira yayanta ya faɗa masa shi baya gida amman Amira tana gida. Harabar gidan ya shiga da motarsa, sannan mai gadin ya shiga ciki yace ana sallama da Amira, bayan ƴan mintuna ya dawo yace wai ance wanene?


“Kace Tahir ne abokin Big Bro”


Sai mai gadin ya koma, ya dawo ya ce wai ance ya shigo ciki. Ba musu ya doshi babbar ƙofar Falon. Da sallama ya shiga Ammy ta amsa masa tare da Amira sannan ya zauna, suka gaisa ya faɗa musu abunda yake tafe da shi. Ba Amira ba har Ammy ta yi mamakin jin Uzair na son ganinta to me zai ce mata? Bayan duk abunda yayi mata, daman tun da suka samu labarin bashi da lafiya Ammy da Abban Amira suke cewa wai amanar Amira ce ta kama shi.


“Yana nemana kamar ya ? Me zai ce mun?”


“Nima ban sani ba, amman yace maganar tana da muhimmanci, sosai”


Ammy ta ce


“To ba zata ita kaɗai ba, tare zamu je, kuma sai Abbah ta ya dawo duk abunda ya ce shi zamu yi”


Tahir ya miƙe tsaye yana faɗin


“Kamin na zo nan sai da na yi magana da Big bro, idan har wani abu ne mai cutar da ke ba zai bari na shigo nan na faɗa miki ba”


“Koma dai minene sai mahaifinta ya dawo”


“To hakan yayi, ni zan wuce”


“A gaida gida”


Ammy ta faɗa sannan ta bishi da kallo har ya fice. Gaɓa ɗaya jikin Amira yayi sanyi, zuciyarta sai yaye-yaye take mata, ta rasa dalilin da zai sa Uzair ya so ganinta, to ko yana zargin tana da hannu a ciwonsa ne? Ko kuma wani abun ne kuma ya faru? Maganar Abbah ce ta dawo da ita daga duniyar tunanin da ta tafi.


“Bari na kira Abbah ki na faɗa masa”


Kai kawai ta iya ɗagawa ta cigaba da tunanin da take.




NAMRA POV.


Bayan an gama bikin Maryam da Hindatu, Abbah ya shiga fafutukar nemawa Namra Admissions a wata makarantar koyarda ilmin computer. Kasancewar duka jami'o'i a yanzu sun gama ɗaukar ɗalibai, gashi kuma bata da komai a yanzu saboda ƙonewar da takardunta suka yi a motarta lokacin da Asim ya taɓa haɗari, ba ƙaramin kuɗi Abbah ya kashe ba wajen fito mata da tsofin takardun da suke makarantar primary da kuma Secondary school. Jami'ah kuma sai next year zata fara, tun da ta riga ta lalata karatunta tun a wacan lokacin.


Sai dai wannan karon kan Alhamdulillah komai ya zo da sauƙi, kasancewar Abbah ya saki ƙuɗi cikin ƙanƙanen lokaci aka yi komai. Aiko murna gurin Anty Amaeya da Namra ba a magana kamar su haɗe Abbah, dan jindaɗi.


Monday mai zuwa Namra zata fara zuwa makaranta, ranar Assabar da Safe Abbah ya kawo mata sabon direba da zai riƙa kai ta makaranta, Namra ta yi murna sosai dan bata tsammaci haka daga gurin Abbah ba.


“Abbah ka yi min abubuwan da ban yi tsammani ba, ka nuna min sosai, Allah ya ba ni ikon saka maka”


Duk suka amsa da Amin har Anty Amarya dake ƙara jin son Abbah har cikin ɓargon ranta. Namra ta ɗauki ɗankwalin abayarta ta yafa ta fita dan ganin sabon direban nata. Tsaye tayi cak a baki ƙofa tana furta


“Lamido”


“Yes Ma'am”


Ya amsa a natse, yayi fari yayi kyau sosai ƙananna kayan da ke jikinsa sun ƙarɓe sa sosai. Ta nunashi da yatsa sai ta kasa magana. Murmushi yayi ya gabatar da kansa.


“My Name is Aliyu Adamu Lamido your new driver”


“How.... How....”


Maganar ta laƙe ta ƙi fitowa sai ta sake nuna shi da yatsa.


“You...”


Murmushi ya sake yi yana kallon yadda ta canja ta yi kyau kamar ba ita ba, baƙin nan nata sai sheƙi yake ga dogon hancin nan da farraren idonta da suka ƙara fitowa.


‘Black beauty akwai kyau’


A zuciyarsa yayi maganar a fili kuma murmushi yake mata mai ɗaukar hankali. Juyawa ta yi ta koma cikin falon, cike da ruɗani ta kalli Abbah ta ce.


“Abbah da gaske shine sabon direba na?”


“Eh ko be miki ba ne?”


“Me direban yayi”


Anty Amarya ta tambaya. Zaunawa Namra ta yi tana faɗin.


“Anty Lamido ne fa”


“Wane Lamido kin san shi ne?”


“A gidansu na sauka Kaduna, shi ya ɗinga ɗawainiya da ni har kuka zo kuka ɗauke ni, Lamido na gidansu Neina fa”


“Au shine? Ya akayi ya zo nan ne?”


“Nima ban sani ba, abun ya ɗaure min kai ne, Abbah ina ka haɗu da shi?”


“A can ƙamfani ya same ni, wai yana son a ɗauke shi direba idan zai samu, kuma baya son na kamfani na gida yake so, kin san daman ni kuma ina neman direban da zai riƙa kai ki scul yana maido ki, shiyasa na ɗauke shi”


Namra ta girgiza kai.


“Abbah why not ka ɗauke shi aiki a kamfanin ka, yayi degree fa, aikin ne be samu ba”


“Ko zan ɗauke shi ba yanzu ba, sai naga gudun ruwansa, idan dai be miki ba za a iya canja miki wani”


“Oh no yayi min, ba matsala Allah ya saka maka da alheri”


“Amin, yanzu sai ki tashi muje Asibiti, Uzair ya ce min yana son ganinki”


“Ni?”


Ta nuna kanta, ba ita kaɗai ba, har Anty Amarya mamaki ta yi.


“Ya za'ayi Uzair ya cw yana son ganin Namra? Kin yi wata magana da shi ne?”


“Anty ya za'ayi na yi magana da shi, tun da na bar garin nan har na dawo wata kalma bata taɓa shiga tsakani na da shi ba”


“Ɗazu dai Mahaifiyarsa ta kira ni tace min dan Allah na zo da ke, Uzair yace zai yi wata magana da ke mai muhimmanci”


“Ni gaskiya ba zani ba”


“Sai fa kin je, indai har zan baki umarni ki bi, bawan Allah nan ban san abunda ya tare miki ba, daga kawai yace yana son ki, kuma na ga yanzu ko lafiyar jikinsa bata ishe shi ba, ya aikamata ki je ki masa sannu”


“Zan je kawai bisa Umarnin ka”


“To tashi ki saka Hijabin ki”


Ba musu ta tashi ta nufi ɗakinta dan ɗauko Hijabin.


“Wai ko na taso muje har da ni ne?”


Anty Amarya ta faɗa tana kallon Abbah, dan taji me zaice, dan tana cike da son sanin dalilin kiran Namra da Uzair yayi bata son a bata labari.


“Tashi muje komai dai son gulmarki sai kin ba su ɗaki sun yi magana”


Abbah ya faɗa da fuskar zolaya. Anty Amarya ta tashi tana dariya ta nufi ɗakinta.


Cikin ƙanƙanen lokaci suka isa asibitin, gaban Namra sai fat fat fat yake, duk da bata san ta yi wani laifi ba, tana jin tsoron kiran da Uzair yake mata. Bama kamar lokacin da suka shiga ɗakin ta yi ido huɗu da Amira, kallon kallon Akuya kallon Kura suka riƙa yi ita da Amira, ko wannen kuma.ya kasa cewa ɗan'uwansa uffan. Daga su har Ammy da Anty Amarya, Ammy sai faman hararar Anty Amarya take da Namra, Abbah ne kawai ya gaisa da Abban Amira, sannan Big Bro ya gaishe shi, ya kuma gaishe da Anty Amarya sai kuma ya kalli Namra fuskarsa da murmushi ya ce.


“Namra ba gaisuwa, kin san ni fa yayanki ne”


“Ina wuni”


Ta gaisheshi ba tare da tayi murmushi ba, ita hankalinta gaba ɗaya ya tattara ya koma kan Uzair yanayin yadda ta ganshi ya bata mamaki, daman hausawa suka ce abunda duk ya baka tsoro wata rana sai ya baka


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login