Showing 135001 words to 138000 words out of 281103 words

Chapter 46 - ZAGON KASA Book Complete Document by Khadeeja Candy .txt

28 Dec 2024

61263

ya gasheta da Ummi kamar yadda ya saba. Sai ta amsa masa murmushi tana faɗin.


“Mu duk mun ɗauka jirgi zaka biyo fa”


“Wallahi haka kawai naji ina buƙatar driving da kai na”


“Amman ka biyo haka babu kp ƴan rakiya Abdallah abinda Mai Martaba yayi ta maka magana akai kenan, kana da maƙiya fa ya kamata kana bawa kan ka tsoro mana”


Murmushi yayi ya lanƙama Ummi suka shiga falon tana faɗin.


“Abinda Allah ya bututa babu mahani”


Amira bata jidaɗin yadda ya wuce ta ba, sai yayi kamar be ganta ba. Ba kuma dan be ganta ba ɗin sai dai rashin kular da yake nuna mata, dan shi sam bata burge shi.


Saman kujera ya zauna tare da Mahaifiyarsa yana dariyar yadda take masa faɗan ya take masa na zuwan da yayi ba tare da bodyguards ɗinsa ba.


“Haba ummi bodygrsd zasu tsare ni ko Allah?”


“Ni ba wani wa'azi na ce ka min ba”


Ya ɗaga hannayensa sama yana dariya. Kallonsa kawai Amira take cike da shauƙi, bata zaci yana dariya haka ba.


Ruwan sanyi Amal ta kawo masa tare da kofi, ya sha ruwan sosai ya jiƙa maƙoshinsa. Sannan ya tashi ya fice daga part ɗin ya nufi part ɗinsa. Tuɓewa yai ya ɗaura tawul ya shiga banɗaki yai wanka tare da alwala, sannan ya fito ya shirya cikin ƙananan tufafin daman sune tufafin daya fi so inda a gida yake. Sai da ya feshe jikinsa da turare sannan ya fito. Ya nufi masallacin gidansu yai salla azahar, bayan ya gama ya gaisa da wasu mutanen unguwar tare da sojojin da suke gadin gidan. Be fita da komai a aljihunsa ba shi kuma mutum ne mai alheri baya jindaɗin ya ganka be baka komai ba, sai dai kam akwai zuciya dan baya ɗaukar raini. Tsayar da mutanen yayi ya dawo cikin gida ya ɗauki kuɗi masu ɗan yawa ya miƙawa wani soja yace ya raba masu. Aiko har da waɗanda ba su yi salla a masallacin ba sai sheƙowa suke suna samun nasu rabo.


Sai da ya tabbatar kowa ya samu sannan ya juyo ya dawo cikin gida. Part ɗin Ummi ya nufa dan cin abincinsa na rana.
Duka ƙanensa suna dinning har Ummi suna cin abinci, Amira ma ta maida hankalinta sai cin abincin take kamar bata ga shigowarsa ba, Amal ce kawai ta kawarda kai tana yamutsa fuska kamar mai ƙyanƙyami.


Kujerarsa yaja ya zauna yana naɗe hannun T-shirt ɗinsa yana rabon ido, dan be san wane abinci zai fara ci ba.


“Dude don't..!”


Amal ta faɗa tana yarfar da hannu.


“Why?”


“All these things wannan yarinyar ce ta girka”


Ta faɗa tana nuna Amira. Daga Ummi har Abdool ɗin da kansa be jidaɗin abinda Amal tayi ba. Ɗan murmushi Amira ta yi, irin murmushin na rashin jidaɗi ta tashi daga cin abincin da take ta nufi ɗakin Amal ɗin wanda yanzu ya zame mata kamar ɗakinta a yanzu.


Sai ta ta shige sannan Ummi ta kalli Amal cikin xafin rai tace


“Dan ta girki abinci kike cewa karya ci ita ba mutum bace? Bata taimake ku ba? Bata fiye muku wannan inyamurar da take girka muku abinci ba? Miyasa kika ɗauki rayuwa da zafi ne Amal, ke dai baki rayu da babanki ba, balle na ce shine ya koya miki, wannan sam sam ba ɗabi'ar ƙwarai ba ce, ɗan 'adam ba abun wulaƙamtawa be ne”


Fashewa Amal.tayi da kuka ta tashi da gudu ta shiga ɗakin Meesha. Abdool ya zuba abinci ya soma ci yana faɗin


“Ummi you shouldn't talk to her that way marainiya ce”


“Ai daman kai kake buɗe mata ƙofar yin abinda duk take so, babu dama ayi ama Amal faɗa a gidan nan, duk abinda take yi hundred percent kai kake supporting ɗinta”


“Ummi ba haka bane, Amal itace ƙarama a cikin mu, kuma yarinyar nan ko da ta yashi bata san mahaifinta ba, ya kamata ace tana jin sanyi wani gurin”


Ummi tayi shiru tana cigaba da cin abinci. Tasna abinda Abdool yake faɗa gaskiya ne da acw mahaifin su an nan da ko hararsu Ummi bata isa tayi ba, dan game da yaransa ba shi da kyau babu mai taɓa masa komai kusancinsa da kai, musamman Amal da yake jin ta kamar ransa. Sai dan tana marainiya ba zai bata damar wulaƙanta kowa ba, Ummi bata da wannan halin daman can halin mahaifinsu baya burgeta, Amal ce ta kwashe halin gaba ɗaya, sai kuma Meesha dake ko-in-kula da mutane.


“Amman shi kenan, dan tana marainiya sai ta riƙa irin wannan halin? Dubi ka ga yarinyar nan wai har warin mutane take ji haba wannan iskanci ai har yayi yawa”


Abdool ya yi dariya


“Ƙurciya ne zata daina nan gaba kaɗan”


“Allah yasa”


“Amin”


Yaja tissue ya goge bakinsa, sannan yaja kujerar ta yi baya, ya miƙe tsaye ya nufi ɗakin da Amira take.


Kife ya tarar da ita saman gadon tana kuka. Sai ya zauna a kujerar dake ɗakin yana ƙarema ɗakin kallo kamar baƙonsa.


“Funny you indai akan Amal zaki riƙa kuka zaki ƙarar da hawayen ki ne kawai baki gama kukan ba, the more Amal knowing you are crying for her the more she will do something to insult you, haka rayuwarta take akwai ƙuruciya a cikin ta sosai”


Daga lokacin da kalaman Abdool suka fara shiga kunnenta sai ta ji duka kukanta ya yanke, sautin muryarsa da take ji sai tsigar jikinta ta tashi. Tashi tayi zaune ta share hawayenta, ɗaga kanta da zatayi caraf cikin idanuwansa. Eyeball to eyeball suke kallon juna ita da shi, kowa da irin abunda yake tsaƙawa a zuciyarsa. Ita ta riga kawar da nata idon saboda kwarjinin da yayi mata, sai ta kawarda fuskarta gefe. Tana murmushi a zuci.


“Sorri for what Amal did to you”


“Never mind”


Miƙewa yayi tsaye ya fice ɗaga ɗakin ya nufi ɗakin Meesha inda Amal take. Ita ma lallaɓata yayi har tayi shiru sannan ya fito ya koma part ɗinsa ya canja kaya ya nufi gurin Mai Martaba.


Ba shi ya dawo ba sai da dare ya raba, daman duk yaje gurin Mai Martaba ko da rana ne sai ya daɗe balle ya je late. A falo ya sami Ummi Amal na saman ƙafafunta tana bachi, murmushi yayi ya zauna kusa da su yana kallon Amal ɗin.


“Har kun shirya”


“Ta ya za'ayi uwa da ƴa, ita ta kawo kanta tace min ta daina”


“Hmmm Amal kenan wannan ɗabi'ace kawai ta ɗan adam, amman idan kin lura har ƴan'uwanta bata bari ba”


“Jiya ma haka suka yai ita da Haleema akan Amirar nan”


“Ai tana gama wannan makararar ƙasar waje zan kai ta tayi karatu a can a huta”


“Ta dai ƙara lalacewa”


Dariya yayi ya miƙe tsaye.


“Ummi good night”


“Aha night, Abdallah yaushe zaka koma?”


“Jibi, akwai aiki a gaban mu abuja”


“Ai kai Allah be raba ka da aiki ba, ni dai kamin ka koma ina son kaje gidan nan na Haleema ka duba mana shi, yadda gyaran zai kasance sai ka kira yaron nan Isma'il ka faɗa masa, dan kasan gidan marayune ƙara a gyara idan ma wasu ƴan hayar za a zuba sai”


“Okay zaje gobe inshallah dan gobe babu inda zan je, a ina ne gidan ya ke? Tun da akayi gobarar nan ma ban je na duba shi ba”


“Yana nan Nasarawa na can wajen gidan action kuɗi ƙasa, kasan irin abubuwan nan sai maza, ni mace wano abu sai dai na ɗaga ƙafa”


“Inshallah gobe zanje”


“Allah ya kai mu”


“Sai da safe”


Yana hamma ya fice daga part ɗin dan duk ya gaji sosai.




*HILAL POV*


Lokacin daya isa asibitin be wuce ɗakin da Rafiq yake ba sai da ya biya ya karɓo hoton da akayi ma Rafiq ɗazun. Sai dai ba iya ya buɗe hoton ba har ya koma office saboda fargaba, sai yanzu ya gane irin abunda majinya suke ji idan wani nasu aka ce yana da wani ciwon ko kuma za ayi masa aiki.


Zamansa kenan a office, sai ga Alhaji Bashir ya shigo cikin mayan tufafin na shadda, tun kamin Hilal yayi masa uwarnin zama ya zauna yana nuna alhininsa akan abinda ya faru.


“Ɗazu nake jin labari babu daɗi ban samu na shigo ba sai yanzu”


Ya faɗa yana miƙawa Hilal hannu su gaisa. Hilal ya maiyarda Hoton gefe ya aje yana sosa kansa yace


“Ƙaddarori ne”


“Wallahi shiyasa kaga bana son ƙara auren nan dan rigima ce kawai ko wacce da kalar matsalar da take zuwa da ita, yanzu miye abin na sawa yaro guba”


“Babu tabbacin ita tasa Bashir, amman dai ita kaɗai ce a gidan”


“To ai shi ya nuna ita ɗin ce, kuma kasan fa ita ta fitar da Rashida a gidan yanzu kuma tana son ganin bayan ƴaƴanta, gaskiya abun be yi daɗi ba, ai ota Rashida tace ba zata ƙyale ba, dan Asma'u ta ce har ta aika mata sammaci ko? Amman dai ban jidaɗi ba gaskiya”


Hilal ya jingina da kujerarsa yana lilo.


“Ni ne na saki Rashida da kaina san ganin damana, maganar kotu kuma taje duk inda zata je ta kai Kalsoom i will surely depend her”


Alh. Bashir ya masa kallon mamaki.


“Doc kasan abinda kake faɗa kuwa? Ɗan ka ne fa ɗan ka ta nemi kashewa”


“Kana da hujjar ita ɗin ce ta kashe shi? Amanarta na karɓo a gurin iyayenta yanzu haka tana ƙarƙashin kulawa ta ne, dole na yi abunda zan kare ta”


“Kana nufin za ka ci gaba da zama da ita kenan?”


“What do you expect?”


Ya ɗaga kafaɗunsa.


“Nothing, ya mai jiki”


“Da sauƙi bachi ya ke”


“Okay Allah ya ƙara lafiya, ni zam koma da safe zan zo na duba shi”


Hilal ya miƙa masa hannu suka sake gaisawa.


“Na gode sosai”


Wani kallon Alh Bashir yayi masa, yana mamakin yadda Hilal ya sauya masa kamar ba shi, duk irin tare da suke a can baya yana aure Kalsoom duk ya watsar ta ɗauke masa hankali. Lallai yanzu ya yarda da maganar da ake cewa magani tayi masa, tun da har Hilal ya furta zai tsaya mata, bayan kuma ɗansa ne tayi ma wannan karen aiki.


Bayan Alh Bashir ya wuce Hilal ya koma saman kujear ya zauna, yana tunanin maganar sammacin da Alh Bashir yace Rashida ta aika Kalsoom. Duk waɗancan maganganun yayi ne kawai dan ya nuna kamar ya san abinda yake faruwa bayan kuma besan komai, yayi hakan ne dan bayan son ayi Alh Bashir yai insulting ɗin matarsa. Saboda ya tsani haka.


Ajiyar zuciya ya sauke yana tunanin yadda zai ɓullowa lamarin. Sai kuma ya kai hannu ya ɗauki hoton ya buɗe yana dubawa. Abinda ya gani ya tayar masa da hankali, da sauri ya tashi yana ƙara dubawa dan tantance abinda yake ganin ɗin. Da sauri ya bar Office ɗin ya nufi inda zai laƙa hotunan su fito a majigi...




*RASHIDA POV.*


Tana sauke wayar ta ƙara ɓata fuska, zuciyarta ta sosu matuƙa, akan abinda Alh. Bashir ya gama faɗa mata, na cewar Hilal zai tsaya ma Kalsoom, a tunaninta shi da kansa zai saka ta kotu yadda tasan yana jin da ƴaƴansa.


Hawaye suka zubo mata sai tasa hannu ta share. Hankalin ƴan'uwa sai duk ya dawo kanta, daman tun ɗazu maganar da suke kenan har da wata ƙawarta wacce suka yi makaranta a tare.


“Ke mai ya faru?”


Khady ta tambaya tana dafa ta.


“Wani abokinsa ne ya kira ni yanzu yana faɗa min wai Hilal yace zai tsayawa Kalsoom”


Ummu Faisak ta daki ƙirji.


“Da gaske? Lallai wannan Kalsoom ɗin ta wanke ta bashi ya sanyen, kan uban nan ayi ma ɗanka abu amman kasa yin komai har kace zaka tsaya mata”


Dukansu jinjina lamarin suke. Zainab ta kada baki tace


“Wannan abun har ƴan Human Rights sai mun saka, ai idan ya san wata be san wata ba, ƙaramin yaro zaka bari a wulaƙanta yama baki ɗan kawai tun da bayan son zuri'arki”


Ummu ta jinjina kai.


“Hmmm Ai wallahi sai na masa rashin mutucin, dan har a tv sai na nuna su, ai daga ganin wannan abin kinsan Hilal ba cikin hankalinsa yake ba. Kuma wallahi tallahi matuƙar ina numfashi sai Kalsoom.ta bar gidan nan, ba ko mallaka ne aikinta wallahi ko a gabanta bokanci ya yake saƙa sai na nuna mata shayi ruwa ne, ai ko baba da babansa”


Rashida tayi saurin rufe mata baki 5ana kuka.


“Dan Allah ki ƙyaleta, ni dai bana iya, ita ta sani can ita da Allah”


“Ai ban ci ki iya ba bada kuɗin ki zan yi ba, amman wallahi tun da ta taɓa ki sai na taɓa ta”


Wani yatsine yake tana tsine ɗankwali irin ita ga ga tantsiriya ɗin nan. Maimunatu ta girgiza kai


“Daman kin yi sake tun farko Rashida Namiji kamar Hilal kinsan duk wace ta shiga gidansa kan ba fita, ni da nice ke Wallahi da wannan abokin nasa zan aura, in yaso ya mutu....”


Ta murguɗa baki. Fashewa Rashida tayi tda kuka tana narke musu kamar wata ta ƙwarai, su kuma sai tausayinsa suke suna bata haƙuri....






INA JINDAƊIN COMMENTS NA KU. THANKS........🙏
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *56*




Idonsa ya cika da hawaye, jikinsa ya mutu sosai har yana ƙoƙarin zamewa ya faɗi kamar ba Namiji ba.
Hannunya kai ya taɓa hancinsa ya lumshe, tana girgiza kai. Abinda yake bashi mamakin results a yanzu ya nuna ba guba bace gas ya nuna kuma har yayi effecting ɗin ƙwaƙwalwar Rafiq, that's mean zai zama wani iri kenan. Wanda abu ne mai wahala ya koma dai-dai, ko da kuwa an ɗora shi akan ganine.


Ya daɗe idonsa a lumshe, _Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un_ Shine abinda yake ta maimatawa a zuciyarsa. Daker ya buɗe idon ya ƙarasa ya ciro hoton ya bar ɗakin yana mai jin kansa kamar marar lafiya.
Be shiga office ɗinsa ba sai kawai ya nufi ɗakin da Rafiq yake kansa na mugun sarawa. Tsaye yai a bakin ƙofa yana kallon Rafiq cike da tausayin Rafiq, ya daɗe jikin ƙofar kamar mai tsoron ƙarasawa. Juyawa yayi ya koma office ɗinsa, ya zauna kaman kujera ya dafe kansa still takardun na riƙe a hannunsa. Babu abunda ya faɗo masa a rai sai ya sake ɗaukar wani hoton ya gani, wata ƙila wannan ƙarya ya nuna masa...
Ɗaga kai yayi ya sake kallon hotunan, yana sauke ajiyar zuciya. Ya ɗauki mintuna talatin yana kallon hotunan sannan ya buɗe wani gurin ya saka su ya ɗauki abubuwan daya shigo dasu office ɗin ya fito, da kansa ya kulle office ɗin sannan ya nufi ɗakin da Rafiq yake. Har lokacin bachi yake abunsa, be farka ba.
Wani ɗan ƙaramin tebur Hilal ya nufa ya ɗora kayan a kai sannan ya ƙarasa gurin da Rafiq yake yaja kujera ya zauna, ya riƙe hannunsa yana hafawa, wani irin tausayin Rafiq ne ya ke shiga zuciyarsa.


Haka ya zauna ya tsare Rafiq da ido yana jin kamar yayi masa kuka, ko da kuskure bachi be doshi idonsa ba.lokaci lokaci yake sauke ajiyar zuciya kana ya haɗe yawu. Rafiq be farka ba sai kusan uku da rabi na dare. Murje-murje ya fara yana kiran ruwa kamin ya buɗe ido. Da sauri Hilal ya tashi ya buɗe jakar da ya shigo da ita ya haɗa masa tea ya ta sheshi zaune ya soma bashi tea ɗin, yana masa sannu kamar wani babba.


Yana gama shan tea ɗin ya langwaɓarda kansa jikin Hilal bakinsa yai gefe kamar zai talalarda yawu.


“Rafiq”


Hilal ya faɗa yana girgiza sa dan zuciyarsa ta katse gaba ɗaya. Ɗagowa Rafiq yayi kaɗan ya kalli Daddynsa sai ya maida kai gurin ƙofa yana kallo kamar mai jiran shigowar wani.
Can kuma ya ɗaga kai yana kallon ɗakin, kamin ya sake kallon Daddynsa.


Rumgumesa Hilal yayi yana hawaye. Daga bisani ya ɗauko wasu magunguna ya bashi, sannan ya maida shi a ƙirjinsa ya kwantar. Haka suka kwana, Rafiq na kwance a ƙirjinsa, Hilal kuma be rumtsa ba, a kan idonsa aka kira salla asuba. A hankali ya kwantar da Rafiq yai alwala a toilet ɗin ɗakin ya nufi masallacin asibitin.


Ya daɗe yana addu'a bayan yai salla, a nan masallacin ma sai da ya gaisa da wasu da suka sanshi har suna masa ya jikinsa ɗansa.
Sai da ya koma ɗakin ya ganshi sannan ya fito harabar Asibitin yana amsa wayar Hajiya dake tambayarsa ya jikinsa. Be faɗa mata a results ɗin da hoton ya bada ba, dan ba labari bane mai daɗin ji.
Ko da ya isa gida 6:30am, dan garin be ƙarasa wayewa ba a lokacin. A mota ya zauna har 30 ɗin ta ƙarasa sannan ya buɗe ya shigo nufi ƙofar shiga gidan. A kulle ya jita hakan yasa ya kai hannu ya ƙwanƙwasa, sai ya kawar da fuskarsa. Bayan kamar minti biyu zuwa uku Kalsoom ta buɗe ƙofar.


“Sannu da zuwa”


Ta faɗa cikin sanyayayyiyar murya. Be amsa ba be kuma kalleta ba sai kawai ya raɓa gefenta ta shiga cikin falon.
Kai tsaye ɗakin su Ulfah ya nufa, shiri ya tarar suna yi na makarantar boko.Dukansu ya shafa kansu yana masa good morning ɗin da suke masa, sannan yaja su jikinsa ya rumgume.


“Gobe za ku koma gurin Hajiya da zama, a can za ku zauna har na gama gyara wannan gidan”


Ezzah ta daka tsalle, tana murna, Ulfah ma Murna ta yi, dan suna son zuwan gidan Hajiya ko dan su yi wasa da ruwaz ga gidan akwai yara da yawa sa'aninsu.


“Daddy har da Anty?”


Ulfah ta tambaya cikin zumuɗi. Shiru Hilal yayi kamin ya amsa mata.


“A'a Anty a nan zata zauna”


Bata wani damu ba dan tana son gidan Hajiya, sai dai ta san zatayi missing Anty kan sosai, a ranta take auna a weekend zata zo ta ganta.Bayan kamar minti biyar ya miƙe tsaye ya nufi ɗakinsa. Yana tura ƙofar ɗakin yana Kalsoom zaune saman gadonsa tana hawaye.


Be kulata ba ya nufi wardrobe ya buɗe yana cire wasu tufafin. Da kallo ta bishi har ya gama cire kayan sannan ta soma magana cikin muryar tausayi.


“Baka buƙatar canjawa yaran ka gida Hilal, ni kake buƙatar canjaw! Ni kaina ban cancanci zama da ƴaƴan da mahaifinsu be yarda da ni ba, ko kaɗan ɓan ga laifin ka ba akan abinda ka aikata, ko ni kwatankwacin haka zan aikata”


Sauka tayi daga saman gadon ta durƙusa ƙasa ta haɗe hannayenta alamar roƙo.


“Ma gafarta min akan abunda na yi maka Hilal, ba zan sake hararar yaran ka ba balle na cutar da su”


Juyowa yai ya kalleta.


“Kin Aikata kenan?”


Kai ta ɗaga alamar eh.


“Na aikata kuma ina neman ka yafe min, dan dajarar iyayenka


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login