Showing 183001 words to 186000 words out of 281103 words
Chapter 62 - ZAGON KASA Book Complete Document by Khadeeja Candy .txt
da take ya isheta, kuma ya hanata sukuni.
Kasa komawa bachi ta yi daman duk ranar da ta yi irin wannan mafarkin bata iya komawa bachi, idonta biyu har aka kira sallah asuba, amaimakon ta bari sai ta yi sallah sannan ta kwanta sai kawai ta buge da bachinta, ba ita ta farka ba sai sha ɗaya na safe, ƙirƙiri ta yi sallah azuba babu ko kunya, ko da yake abun ya samo asali ne daga gurin mahaifiyarta da bata tsawata mata.
Tana sallame sallar wayar Asim ta shigo mata, da sauri ta ɗauka tana kwabar da tasbihin da take.
“Hello”
“Good morning Mardiya ya kika tashi?”
“Lafiya ƙalau na yi missing ɗin ka”
“Nima Haka har na so na ɗauke ke ki muje yawo dan akwai maganar da nake son mu yi mai muhimmanci”
“Wace magana ce?”
“A'a ba za tayi a waya ba, kamata yayi sai mun zauna”
“Okay yaushe zaka shigo?”
“Idan na samu time zan kira ki, sai na zo na ɗauke ki”
“Okay ina jiran ka”
Daga haka ya kashe wayarsa, ita kuma ta miƙe tsaye cike da jindaɗi ta nufi waje dan ɗibar neman mai siyo mata indomie.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *69*
Be ji zai iya kwana a yau ba,ba tare da yaje gurin Namra ba, daman yasan duk daɗin bakin da yake yi ma Ummi ba wani barinsa zata yi ya daɗe ba, kuma idan har ta bar shi Mai Martaba ba zai bar shi ba, and what's on his mind nowa ya ji labarin yarinyar duk da bashi da tabbacin ko zata yarda ta saurareshi ma.
Miƙewa yayi tsaye yana duba shaddar da ke jikinsa.
“I really need to do this, ko zan samu peace of mind”
Closet ɗinsa ya buɗe ya fiɗo wata kafirar shadda golden color, ya buɗe ɗayar wardrobe ya ɗauko hular ƙobe ya aje saman shaddar, sannan ya shiga Bathroom ya watsa ruwa.
Bayan ya tsane jikinsa da tawul ya shafa mai, sannan ya saka body spray, ya saka short da white singlet, sannan ya shafa wani turare, ya ɗauki shaddar ya saka.
Wani mai ya ɗauka ya shafa ma fuskarsa, sannan ɗora da turare. Ya ɗan soma jin babu daɗi lokacin daya tuna gidansu Lamido zai je, yasan he has zero reasons to hate Lamido, but he still hate him.
“Maybe he's bad person”
Ya faɗa yana murza wani turaren a wuyansa, kamin ya ɗauki hular ya saka a kansa. Agogon hannunsa ya kalla, yaga tara da kwata, hakan yasa shi ɗan hanzarin ɗaukar wayarsa ya fice.
Sadauki na ganinsa ya tashi, sai Abdool ya ɗaga masa hannu.
“Ni kaɗai zan je”
“Allah ya tsare ya kiyaye hanya, Allah ya kare ka daga dukan ni abun ƙi, Allah yaja kwanan ka”
Abdool be kula shi ba, balle ya amsa addu'ar da yake masa, sai da ya kawo gurin motocin da suke harabar gidan sannan ya ƙwalama Sadauki kira, sai ga shi ya fito da sauri.
“Key wacan motar na ke so”
Ya nuna masa wata baƙar mota mai baƙin gilashi, wanda ke aje can gefe. Da Sauri Sadauki ya koma ciki ya ɗauko masa key ɗin motar ya miƙa masa, sai da ya sake duba agogon hannunsa sannan ya nufi motar ya shiga, gabansa sai faɗuwa yake.
Sai da ya hau titi, sannan ya ciro wayarsa ya dannawa Ummi kira. Sai da yayi mata one missed call sannan a na biyu ta ɗauka.
“Assalamu alaikum”
“Wa'alaikissalam. Ummi ki min addu'ah zanje wani guri neman abu a yanzu, kuma babu tabbas zan yi nasara, idan kuma har na ƙyale abun hankali ba zai kwanta ba”
“Abdool mi zaka aikata? Thought baka aiki yanzu ka ce sun baka hutu?”
“Eh ba aikin office ba ne, wannan aikin nawa ne na sa kai”
“Abdallah karka aikata abunda zai sa rayuwarka cikin haɗari, ka dawo gida gobe”
“O my god”
Ya dafa kansa.
“Allah Ummi ba wani abun ba ne, kawai i need your prayers”
“Ka dawo gida gobe na faɗa maka, kasan dai kullum rayuwarka tana cikin haɗari ko? Karka kuskura ka wuce gobe, umarni na ke baka”
Ta kashe wayarta cike da fushi, dan ta san idan ba haka ta masa ba, ba zai ji ba, gashi duk ya tsorata ta, da wannan maganar na shi daman ita ba son take yana tafiya nesa da ita ba.
Iskar bakinsa ya busar yana cigaba da tuƙinsa a hankali.
“Daga neman sa'ah sai kuma abu ya zama ɗan zane, ban san salon da ya kai ni faɗa mata ba, Allah ka taimake ni”
Unguwar bata da kyau sosai, amman haka ya riƙa kunno kai cikinta yana kallon ƙananan gidajen da suke unguwar har ya isa bakin ƙofar gidan. Wani tunanin ne ya zo masa, sai kawai ya ƙara gaban da gida sannan ya faka motar, ya buɗe ya fito.
Ya samu minti salati tsaye a gurin sannan ya kira wani almajiri da ke bara ya nuna masa gidan su Lamido.
“Je can gidan ka ce ana sallama da baƙuwa”
Sai da almajirin ya kama hanya, sai kuma Abdool ya kira shi ya dawo.
“Ba haka zaka ce ba, ka ce Abdallahi daga Katsina ya na sallama da Namra, Namra ko? Yes Namra zaka ce”
“To”
Almajirin ya nufi gidan da sauri. Faɗuwan gabansa ya ƙaru lokacin daya fara tunanin irin amsar da almajirin zai dawo masa da ita.
NAMRA POV.
Ba laifi yau ta dan sake bisa da jiya, ko dan yau sun ɗan tausasa ta ne kuma ta wuni a tsakar gidan ansha fira da ita. Sai dai bata janye maganar tafiyarta ba, ta yarda ta bari har sai nan gaba, idan ta ƙara jin sauƙi abubuwa sun ɗan dai-dai.
Yau ba iya Maltina da madara kawai Lamido ya bada aka siyo mata ba, har da gasasshen nama, sai dai bata ci ba kasancewar komai bata jindaɗinsa a yanzu.
Sai da aka yi sallama magariba sannan ya bada aka siyo mata tea, yadda yake damuwa ta ci abinci shi kansa be damu da ya ci abincin ba, sam mantawa yake da nasa ciwon wata ƙila ko dan be jimu sosai ba, yake dauriya irin ta maza, ko kuma dan hankalinsa ya ɗauko gurin Namra ne. Shi kansa yana mamakin yadda yake damuwa da Namra, sai dai yana fi karkata hakan da tausayinta da yake, su kansu su Neina suna kula da halin kuwalar da Lamido yake bawa Namra, duk da sun san halinsa na karancin amman wannan kamar yana ƙoƙarin wuce guri, dan ko magana ake Namra ta saka baki zasu ga ya tattara hankalinta ya miƙa mata ya natsu sosai yana saurarenta.
Yau Neina taja Namra da fira sosai musamman bayan Sallah isha'in nan, abinci na fula take labarta masa da kuma al'adansu na fulani, a nan take taɓo labarin Baban su Lamido da kuma ƙuruciyar Lamido, dariya sosai Namra take idan ana faɗin labarin halin ƙiriniyar da Lamido ya yi. Shi kam iya karsa murmushi idan Neina ta faɗi wani abun.
“Salamu alaikum, wai Abdullahi daga Katsina ya ce yana kiran Namra”
Dam dam dam, gabanta ya tsinke ya faɗi, duk wani farinciki da yake zuciyarta sai ya ta neme shi ta rasa, a take murmushin fuskarta ya disashe. Da sauri ta kalli almajirin dake tsaye can jikin ƙofar gidan yana jiran amsa.
Bata san ko waye ba, amman jikinta ya bata wani yanayi na daban, ga shi kuma anxe daga Katsina, kuma an faɗi sunanta, lallai ko wanene ya santa. Sai dai ya akayi ya san inda take zaune? Miyasa be zo da rana ba sai da dare? Shin waye Abdallah ma? Ko dai Asim ne ya canja suna? Amman taya Asim zai san inda take?
“Ko mijin ki ne?”
Tambayar da Lamido yayi mata ne ya dawo da ita daga duniyar tunanin da ta tafi. Kai ta girgiza.
“A'a ba haka ne sunansa ba”
“Ɗan'uwan ki ne?”
Shiru ta yi tana tunanin irin amsar da zata bashi, idan har ta ce ɗan'uwanta ne zata sanu damar fita ta ga ko waye ne, to idan kuma ya kasance Asim ne ya canja suna fa?
Idan ma shi ɗin ne ai babu yadda zai yi da ni, dan yanzu babu aurensa a kai na, idan kuma har aurensa ya zo maidawa to yayi satti, dan na cika idda tun da na yi ɓari!
“Eh ɗan uwana ne”
Sai a sannan hankalinsu ya ɗan kwanta, Neiɓa ta ce da almajirin.
“Je ka ce tana zuwa”
Sai da almajirin ya juya sannan ta kalli Namra ta ce.
“Ɗauki fitila ki je”
Miƙewa tayi tsaye sai Lamido ya ce.
“Ya aka yi ya san gidan nan?”
“Ni na kwatanta masa, a waya”
Kai tsaye ta bashi amsar ta nufi fitilar ta ɗauka ta nufi ƙofar fita gabanta sai faɗuwa yake. Sam Lamido be so ta fita ba, haka kawai ya samu kansa da rashin jindaɗin kiran da aka mata duk da be san me kiran ba. Neina kuma ta kawo wani zargi a ranta, dan tana ganin kamar Namra ta ɓoye musu wani abu ne.
Zuciyarta cike da tsoro ta fita daga gidan, da tunani biyu, Asim ne ko kuma wani nasa yake mata sallamar. Bata ga kowa a ƙofar gidan ba, hakan yasa ta ɗan ɗaga fitilar tana yade, hangota da ya yi yasa ya tako ya ƙaraso kusa da ita.
“Assalamu alaikum”
Ya furta nata cikin murya mai taushi, da sanyaya zuciyar mai sauraro.
“Amin wa'alaikassalam”
Ta amsa masa ba tare data wayence shi ba. Ya ɗan yi gyaran murya.
“Na san baki gane ni ba”
Ya fido wayarsa ya kunna fitar wayar ya haska fuskarsa. Wannan karon ba faɗuwar gaba kawai Namra ta ji ba, har da tsoro, ja tayi da baya yana nuna shi da yatsa, sai maganar ta naƙale ta ki fitowa.
“Nasan zaki yi mamakin gani na, amman ina son ki ba ni aron lokacin ki kuma ki saurari abunda zan faɗa miki”
“Ba kai ba ne ɗan sarki daya kaɗe Lamido?”
“Ni ne, kuma na san ba a nan kika san ni ba, a Katsina ko?”
Kai ta ɗaga masa duk da bata da tabbacin zai ga hakan kasancewar akwai duhu a gurin.
“Miyasa kake bibiyata?”
“Ba saboda ke na zo garin Kaduna ba, ke ma kuma ina da tabbacin ba dan ni kika zo ba, amman zuciyata ta kasa natsuwa da hakan, direba ne ya kaɗe yaron gidan sai kuma na gan ki a gidan shine abun yake bani mamaki, bayan nasan a Katsina na san ki”
“Ba wasu kalamai na ce ka min ba, amman bari na gargaɗe ka, karka sake zuwa ƙofar gidan nan da sunan gurina ka zo”
Ɗan murmushin takaici da mamaki yayi.
“Babu mace da ta taɓa ɗaga hannu ta mare ni sai ke, babu mace da nake gani na bibiya sai ke, babu mace da ta taɓa faɗa min irin wannan maganar sai ke. Zan bar ƙofar gidan nan amman ina son ki faɗa min tsakanin ki da Allah kina da aure? Kuma ina son ki faɗa min tsakanin ki da Allah waye Mahaifinki, kuma miye alaƙarki da mutanen gidan nan?”
Wani haushi ne ya cika mata zuciya, har take jin kamar ba zata iya amsa masa tambayoyinsa ba, amman Allah daya haɗa ta da shi ne take jin ba zata ɗaga daga gurin ba har sai ta ba amsa.
“Ba na da aure, kuma babu wata alaƙa tsakani na da mutanen gidan nan, sunan Mahaifina Manjo Usman Zamau”
Bata tsaya jiran Abunda zai ce ba ta juya ta shige ciki gidan. Shi har tsoro ta bashi cox the way da take bashi amsar kamar tana masa faɗa.
“Wow”
Ya faɗa yana shafa fuskarsa, kamin ya zuba hannayensa aljihu ya nufi motarsa.
Sorry for the short chapter 🙏🙏🙏
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *70*
‘Manjo Usman Zamau, Manjo Usman Zamau’
Sunan yake ta maimaitawa, tana tunanin kamar ya san mai sunan amman ya kwanta masa, sai dai jin Manjo ma ya tattabatar masa da soja ne.
Murmushi ya samu kansa da yi lokacin daya tuna wasu kalamai da Namra ta yi masa.
“She's so Unique”
Rage gudun da yake, ya fido wayarsa ya nemo number Sadiq ya aika masa kira. Ringing ta yi sai da ta kusa katsewa sannan aka ɗaga.
“Shegen gari baka kira sai ta samu”
Ƙyalƙyalewa ya yi da dariya.
“Chief Sadiq Northwest”
“Au yau Chief na samu kuma? Kai dai faɗa min abunda yasa ka kira ni”
“Kiran ka kawai na yi na gaishe ka, ko kuskure ne kiran manya kuma?”
“Na ji, ya gida ya hutu, ku ai kun samu hutu”
“Gaskiya ba laifi, amman ba wani mai yawa ba ne, ina Madam”
“Madam na nan ƙalau go straight to the point miyasa ka kira ni?”
Dariya sosai Abdool ya yi kamar ba shi ba, sam ba zaka za ci akwai mutumen da Abdool yake sakewa da shi ba, bayan mutanen gidansu.
“Kasan waye Manjo Usman Zamau?”
“Aha ni nasan akwai wata a ƙasa, ai baka kiran mutum hakan nan kawai”
“Ni dai amsa min kawai, ban ce ka min surutu ba”
“Na san shi, kai ma ai kasan shi, amman yanzu ya yi ritaya ai”
“Nima ina jin kamar na san shi amman sunan ya kwanta min”
“Ai mun yi zama barrack da shi ai, a Yola, shine mahaifin su Salwee and Abdulraman na manta sauran ɗiyansa dai, yanzu ina jin yana sokoto zaune, ance ya zama babban ɗan siyasa ma”
Abdool ya bugu sitiyari motarsa da ƙarfi.
“Yes I knew it!”
“Easy Man what happened to him?”
“Ba komai, kawai wani ɗan bincike na ke ne”
“Okay abokin su ekwieu ne tare suka yi aiki, suna shiri sosai”
“Amman kana da addireshinsa?”
“Kai Malam, tun da ba shi na ke wa aiki ba, haka kawai zan aje addireshinsa”
“Okay okay bye”
Sai kawai ya katse kiran zuciyarsa cike da farinciki. Wata number ya sake lalubowa ya aika mata kira.
“Salim a bincika min addireshin Manjo Usman Zamau mai ritiya, kuma a bincika min a cikin ƴaƴansa akwai Namra, aɗan min bincike akan ta”
Be jira abunda Salim ɗin zai bashi amsa ba ya katse wayar, dai-dai loƙacin daya faka a harabar gidan. A yanayin yadda ya shigo cikin gidan ba zaka ce shine ɗazu ya fita a haka ba, yadda ka san wanda aka yi bushara da aljanna haka ya dawo fuskarsa a sake, zuciyarsa fari ƙal.
Yana shigowa falo ya zauna saman cushion yana kallo falon kamar wani baƙo. Kallo ɗaya zaka masa ka fahimci yana ciki nishaɗi, dan hankalinsa ma baya gurin da yake kallo. Wayar hannunsa ya kallo kamar mai son magana da wayar, sai kuma ya watsa yatsunsa saman screen ɗin ya danna number Sadauki, bugu ɗa ya ya ɗauƙa.
“Sadauki ga ni a falo ina jiran ka”
Be jira abunda Sadauki zai ce ba, ya katse kiran fuskarsa shinfide da murmushi. Ba ayi minti biyu ba sai ga Sadauki cikin falon da rawar jikinsa.
“Allah ya taimaki Yarima, Allah yaja kwanan ka, Allah ya baka abunda kake so”
Abdool ya kallesa fuskarsa da Murmushi.
“Amin Sadauki, addu'ah tana tasiri sosai, kaga Allah ya fara ba ni nasara. Yariman ka ya kusa samun gimbiya”
Sadauki ya riƙe baki tare ta washe da dariya
“Mashallah, babban goro sai magogin ƙarfi, Allah ya taimaki Yarima, Mai Martaba zai fi kowa jin farincikin wannan labari”
Abdool ya ɗan risino daga zaunen da yake
“Ya kake auna farincikin Mai Martaba idan ya samu labarin na samu matar aure?”
“Allah ya taimake ka kamar mutum ne, da yake cikin tsamman nin ƴanci, yake cikin baƙin ciki da damuwa, ga yunwa da ƙishin ruwa ya dame sa, masaukinsa kuma babu daɗin zama, me kake tsammani idan aka aka basa sabon masauki mai cike da ƙuramon wanka, ga kuma abinci da abun sha, bayan kuma an ƴanta shi?”
Komawa Abdool ya yi dai-dai saman cushion ɗin ya ɗora hannayensa saman kushin ɗin yana kallon silin.
“Zai kasance mai tsananin farinciki, har zai ji kamar ya haɗe zuciya ya mutu saboda jindaɗi”
“Toh haka zuciyar Mai Martaba zata kasance matuƙar ya samu labarin Yarimansa ya samu Gimbiya”
Murmushi mai ƙayatarwa Abdool ya yi, ba tare da ya kalli Sadauki ba ya ce
“Bana Sadauki da kai za'aje Umara”
Faɗuwa Sadauki ya yi yima Abdool godiya, yana zuba masa kirari, da yabo. Hannu Abdool ya ɗaga masa alamar ya tashi ya bashi guri, haka ya tashi ya fice baki har kunne tsabar murna da farinciki.
Sai da Sadauki ya fice sannan Abdool ya maida dubansa gurin wayar yana lalubo number Mai Martaba. A handsfree ya saka wayar ya ɗorata saman center center tebur ya nufi freezer ya bude ya ɗauko power horse, ya kai bakinsa.
Daga inda yake tsaye yana jiyo muryar Mai Martaba da yayi picking wayar tare da sallama.
“Allah ya taimaki Mai Martaba, i have a good news for you”
“I have good news for you too Son”
“Amman nawa ya fi na ka daɗi, dan nawa idan ka ji ma sai ka bani goro”
“Nima ai sai ka bani goro ba kuma ɗan ƙarami ba ma”
“Me zaka ba ni idan nayi maka albishir da abunda ka daɗe kana jira”
“Zan baka yankin Bakori da kewaye, kuma za a naɗa ka motar Mai Martaba kai fa wace kyauta zaka min?”
Zauna Abdool yayi saman kujera yana dariya har da buga ƙafa, ko ba komai Sarautar da Mai Martaba ya ce zai bashi ta sashi dariya balle kuma yau yana cikin nishaɗi.
“Ni kuma bana da gumi na zaka je Ummara gaida Ubangiji”
“Lallai yau Ɗan Sarki yana ciki farinciki, ɗan tsakura min kaɗan daga cikin labarin ka mana”
“ Ina ai ba tsakure, sai ga ni ga ka, gobe zan sauka sokoto cikin rahamar ubangiji, kuma ba zan kwana ba, har sai na labarta maka abunda zan labartawa Ummi”
“Allah ya kai mu, ya dawo da kai lafiya”
“Amin ya Rabbi. Na gode Mai Martaba, mu kwana lafiya”
Daga haka suka yi sallama, sai Abdool ya ɗauki wayarsa ya nufi bedroom yana kalle kallen gidan kamar yau ya fara shigo shi.
Bayan ya rage tufafin jikinsa ya aika ma wani yaronsa saƙo. Akan ya nema masa jirgin da zaije Katsina gobe.
Bayan kamar minti goma sha biyar yaron yayi masa reply da akwai wanda zai tashi da safe zuwa Katsina.
Daga nan Abdool ya aikama Sadauki da text na maganar tafiyarsu gobe gida, akan yayi duk abunda ya kamata cikin lokaci, duk da be so hakan ba, sai dan Ummi da ranta ya ɓaci.
NAMRA POV.
Da tunanin abunda zata faɗa ma su Neina ta shiga gida, a ɗayan ɓangaren kuma tana tunanin bibiyar da Abdool yake mata. Babu abunda ya fi tsaya mata a rai kamar tambayoyin da ya yi mata.
“Har ya tafi?”
Tambayar da Neina