Showing 87001 words to 90000 words out of 281103 words

Chapter 30 - ZAGON KASA Book Complete Document by Khadeeja Candy .txt

28 Dec 2024

61250

ki har Allah yasa na haɗu da Kalsoom na aure, amman ko d mafarki ban taɓa tunanin aikata zina ba.


Tsakanin jiya zuwa shekaran jiya tausayinki nake, ina tunanin halin da zaki shiga idan babu a rayuwarki, amman yanzu nayi tunani baki buƙata na, sam ni da ke ba mu dace ba, nayi baƙinciki nayi nadamar da kika zama uwar ƴaƴana, faɗa min wanene wannan mutumen?”


Tun da yake maganar, bata balle shi balle tace wani abu, hawaye kawai take, irin hawayen nan da wani ke bin wani. Ya matsa kusa da ita ya ciro takardar take aljihunsa ya aje mata.


“Aure na da ni da ke yau ya ƙare, na sauwaƙe miki kije ki auri wanda kike ganin ya fi ni, ki dauwama ke da shi a duniyar da kuke son kasancewa”


Ɗagowa ta yi tmda sauri ta kalleshi, irin kallon nan da bata san tana masa ba, yau ta rasa gane duniyar da take, sama take ƙasa take, mafarki take ko gaskiya ne? Da gaske Hilal ne ko waninsa? Taya zata rayu ba da Hilal ba? Gidan ta da ƴaƴanta a yau sun zama mallakin kalsoom ba ita ba.


A saman gadon ta matsa can nesa ya rumgune kanta tana zubar ido kamar mai ganin aljanu. Ko kaɗan tausayinta a yanzu kam be ziyarci zuciyarsa ba, dan yasan ta cancanci fiye da haka, sai kawai ya juya ya fice daga ɗakin, cikin wani irin zafin rai da baƙinciki.






NAMRA POV.


Bata jin ko ta faɗama Anty Amarya sun yi wata, zat yarda dan ganin take kamar cewa zatayi shi ma haɗi ne, kuma bata iya tambayarta wani kuɗin, sai kawai ta kira ta da wayar Asim tace mata be bari ba yace ta bari har yaji sauƙi sai su zo tare, Anty Amarya bata jidaɗin hakan ba, sai dai babu yadda ta iya tun da mijinta ne.


Da dare Namra kasa, bachi tayi har sai da taje wani BQ dake maƙota ka d nasu ta nemi ƴar fulanin data zo ta taya ta kwana. Duk da haka har safe ba yi bachin kirki ba dan hankalinta be kwanta da gurin ba.
Da safe sai ta aika yarinyar ta siya musu ice su ɗora girki, a abun da bata taɓa ba a rayuwarta yau gashi zata yi. Kamin yarinyar ta dawo, sai taje waje ta ɗauko duwatsu ta haɗa murhu, kamin yarinyar ta dawo sai ta zauna saman bolcony tana kallon gidan.


Tunani take na ranakun baya, lokacin da Anty Amarya take saka ta girki da gas ko electric amman ta ƙi yi ta riƙa faɗin wahala, yau gashi zayi da abund bata ma taɓa gwada kunna wutar da shi ba, yau ga ta a ɗakin da babu katifa balle gado, duk wani abu mai muhimmanci a rayuwart i zuwa yanzu ta rasa shi.
Hawaye ne suka silalo mata sai tayi saurin gogewa, ganin ƴar fulanin ta doso inda take ɗauke d icen.


Sai kusan 12 ta gama girkin abun ka d wacce bata saba ba, sai ta zuba ma yarinyar ta zuba ma su Mama na su sannan ta zuba sauran a kula, sai ta janyo ruwa a rijiya, ta shiga banɗakin BQ ɗin tayi wanka, sannan ta fito ta shirya cikin atamfar jiya ta saka Hijabi ta ɗauki kular ta fito, yau kam a bakin gate ma ta samu Napep, tayi sa'ah an sauke wata ne, sai kawai ta shiga ya ɗauki hanyar asibiti da ita.
Suna kaiwa Babban titi, aka riƙa musu hannu akan su tsaya, amman ta hana mai Napep ɗin tsayawa, har sai da suka isa bakin asibitin. ta fito tana miƙawa mai Napep ɗin kuɗinsa, ta tsaya jiran ya bata canji, sai ta motar ta faka kusa da ita. Abdool ya fito ya nufo ta jiki na rawa. Kamin ya ƙaraso har Mai Napep ɗin ya bata canjinta ta kunna kai cikin asibiti, shi kuma sai sauri yake ya ci gabanta.


Mama na gurin zamanta ta sinƙayo yadda Abdool ya biyo Namra har cikin ward yana ƙoƙarin cin gabanta, sai ta tashi tsaye, ta matsa can baya tana leƙen su, ta tattara hankalinta gaba ɗaya ta mayar gurin.


*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*

_Written by_
*Khadeeja Candy*


*PAGE - 40*


NOT EDITED ⚠


“Haba baiwar Allah, Wannan wane irin jan'aji ne? Dan Girman Allah ki tsaya ki saurare ni”


Abdool ya faɗa yana haɗe hannayensa, alamar yana roƙonta. Girman Allah daya haɗa ta dashi ne yasa ta tsaya har ta ɗaga kai ta kalle shi.


“Malam ni Matar aure ce”


“Matar aure mai igiya uku ko kuma matar aure kalar aure”


“Matar aure mai igiya uku, dan haka kar ka sake bina”


Wani irin faɗuwa gabansa yayi, a take gumi ya fara zubo masa, a take launin idanuwansa suka canja.


“Inshaallah ba zan sake ba, dan Allah ki yi haƙuri ban san kina da aure ba”


Sai a sannan ya janye ya bata hanya, ta raɓa gefensa ta wuce, shi kuma ya juya jiki a sanyaye ya nufi hanyar fita, kallonsa ake tayi a gurin saboda wasu sun san Namra tana da aure, wasu kuma suna masa kallon sani tun da akan nunasa a tv akan matsalar tsaro, kuma sun san ɗan sarki ne, tun da ga fuskar Mai-matarba nan a fuskarsa.
Sam be ji maganar da wani likita ke masa ba har sai da likitan ya cira ƙafa ya cin masa ya dafa shi.


“Manjor ina magana fa”


Ya ɗan kalleshi yana murmushin ƙarfin hali


“Doc Husaini ya aiki?”


“Lafiya ƙalau, ka zo ganin wani ne?”


“No... Eh.. Oh.. Yeah.. Yeah.. Naga wani Cousin na mu ne”


“Allah sarki, tau ya aiki ya kwana biyu? Kun yi kuɗi kun ɓoya”


“Kai ina wani kuɗi aiki ya samu gaba ba sauƙi”


Haka suka jera suna tafiya, suna ɗan taɓa fira har Abdool ya isa gurin motarsa. Jikin sashin kuzari ya buɗe motar ya shiga yana yima Doc Sallama.


“Tau ni kan zan wuce”


“Yanzu kan ganin ka sai manya, tun da baka ma zama garin”


“To ya muka iya, aikin ne a haka ko ina jefa mu ake”


“Allah ya taimaka, sai mun yi waya”


Daga haka ya rufe motarsa, shi kuma ya juya ya koma cikin asibitin. Ribas yayi ya juya hanyar gidan daya baro.
Tuƙin kawai yake jikinsa ba kuzari, kansa yayi zafi sosai, sai hannu yake sawa yana murza goshinsa, lokaci zuwa lokaci yake sauke ajiyar zuciya har ya isa gida.


Ya daɗe zaune cikin motar, sannan ya buɗe ya fito, yayi yaƙi sosai da ƙafafunsa kamin ya ci galaba akansu har su samu ƙarasawa da shi falon Ummi.
Be damu da farar shaddar dake jikinsa ya zube saman carpet, ya lumshe ido yana sauraren bugun zuciyarsa. Ya samu minti ashirin zuwa ashirin da biyar a haka, sannan Ummi ta fito cikin wata bugaggar shada ya nufo inda yake hankalinta a tashe.


Saman carpet ɗin itama ta zauna kusa da shi ta kai hannu ta riƙa kansa.


“Son tell me what happen? Larai tace min ba lafiya ba, talk to your Mom please”


Sai a lokacin ya buɗe manyan golden eyes nasa ya kalleta.


“Mom i saw her today”


“Who?”


“The woman i have been dreaming of, i finally saw her in a hospital”


“And...”


“Ummi matar aure ce”


Wani dogon numfashi Ummi taja ta sauke, tana tunanin ta inda zata fara kwantar masa da hankali.


“Abdallah, be patient one day your princess will surely come, miji baya aure sai matarsa, mace ma bata aure sai mijinta”


“I know, but what i don't understand is duk mace da na gani bata kwanta min, sai wannan ita kuma yanzu matar wani ce, zuciyata tana son wahalar da ni”


“Karka damu, komai zai wuce, i will talk to Mai Martaba, zan faɗa masa ya baƙa time, har Allah ya baka wacca kake so, bana son ka auri wace baka so ina son ganin farincikin ka”


“Thank you”


“Anything for you”


Ya ɗan kwanto jikinta, babu abunda yake gani a idonsa sai Namra.


“Allah ka shiga tsakani na da zuciyata, Allah ka min tsari da sherin zuciya”


Be ankaro da fili yayi maganar ba har sai da yaji Ummi ta amsa masa ta Ameen, dan shi duk a tunaninsa a zuci yayi wannan addu'ar.
Ummi tana son ɗan ta sosai, ta kan damu da damu damuwarsa, ta fi kowa son farincikinsa, saboda ta san zafinsa.


Abdallah Ahmad Mai-doki. Ɗa ɗaya namiji gurin Hajiya Zuwaira. Kuma ɗa na uku a jerin ƴaƴanyen Mai Martaba sarkin katsina na uku III, wato Alhaji Ahmad Abdallahi Mai-doki, jiki gurin Isma'il Mai-doki sarkin Katsina na farko.
Shine ya gaji sarautar kakansa, tun bayan da sarautar ta bar gidansu, sanadin rasuwar kakansa. Bayan rasuwar Sarkin Katsina na biyu, sai aka ɗauko sarautar aka bawa mahaifin Abdallah, wato Ahmad Abdallah Mai-doki.


Matan sa biyu a yanzu, bayan fitar Ummi ya auro Hajiya Salamatu, wace ta kasance ita ta biyu a yanzu. Hajiya Zuwaira (Ummi) Ta sha gwargwarmaya da uwar gidansa Hajiya Shafa, dan zame mata tayi muguwar kaza, mai hana shiga akurki. Hajiya Shafa ta haifa masa ƴaƴa bakwai, Mashkur ne na farko, sannan Salwee wace ita ce ta biyu, sannan Ummi ta Haifi Abdallah, wanda mai martaba ya saka masa sunan babansa, hakan yasa bata taɓa faɗar sunansa sai dai ya kira sa da Yarima ko Babana.
Mar martaba yana matuƙar son Ummi ganin ita ce ƴar'uwarsa kuma itace tafi kula da shi sama da Hajiya Shafa, hakan yasa zaman gidan ya gagareta, saboda irin son da yake nuna mata.
Babu inda Hajiya Shafa bata shiga ta fita ba, har sai da taga ta raba aurensu da Mar matarba, ba tare daya sani ba yayi mata saki uku lokaci ɗaya, kuma ya karɓe ɗansa, Abdallah a lokacin yana ɗan shekara biyu da wata uku. Son duniya nan Mai Martaba ya ɗauka ya ɗora masa, saboda son da yake ma uwarsa, sai kuma akayi sa'ah ya zama ɗa na gari gurin iyayensa, duk kuwa da faɗi tashin da yasha kamin ya kawo inda yake yanzu. Mai martaba ya so ya kaishi waje karatu amman Hajiya shafa ta hana, tasa aka kai ɗanta.


Haka tasa aka riƙa tura masa kuɗi da sunan karatu ashe yana can yana holewa da ƴan matansa, har yayi karatun ya gama be dawo gida da kyakkyawan results ba. Abdallah da yayi karatu a Nigeria sai ya fishi ƙoƙari da basira, sosai hakan ya ƙarawa Mai matarba ƙaunarsa, bayan ya gama degree a nan sai ya turawa waje yayi Master's. Hakan yasa Hajiya Uwani ma da tazo daga baya ta ɗauki ƙiyayyah ta ɗora masa, kowa cewa yake Mai Martaba yafi son sa da kowa.


Bayan fitar Ummi a gidan Mai Martaba, sai auri Alhaji Dahiru, mahaifin Haleema da Meesha da Fauza, tana da goyon ƴar autar ta, Amal ya rasu. Tun daga lokacin bata sake aure ba, sai tayi zamanta a gidan da take ita da yaranta, daman ba guri ɗaya suke da abokiyar zamanta ba. Da aka raba musu gado sai ta riƙa juya dukiyar tana business da ita har abun ya bunƙasa.


Abdallah mutum ne mai tsantsan da kai, da kuma taka tsantsan da duniya, duk da irin tarin dukiyar mahaifinsa da ta mahaifiyarsa da kuma sarautar da suke da ita, be taɓa sa yayi unƙurin wulaƙanta kowa akan hakan ba.
Yana yawan samun matsala da Ƴan'uwansa a lokacin da yake gurin mai martaba, ganin irin son da yake masa, da kuma irin rufin asirin da Allah yayi masa, ga kuma aikin da shine sillar ɗaukaka a duniya.
Baya son fitina ko tashin hankali, hakan yasa ya tattara ya dawo gurin Mahaifiyarsa, sai ya warewa kansa part ɗaya a gidan, daman can ya zuba musu securities. Ko kaɗan Mai Martaba be so hakan ba, amman dole ya haƙura ganin hakan shine mafita a garesu gaba ɗaya.
Kuma hakan be rage ƙaunarsa a zuciyar Mai martaba sai ma ƙaruwa da tayi, dan a yanzu ne Abdallah yake nuna masa kulawa da biyayyar fiye da da. Ga kuma zumuncin daya ƙaru tsakanin Mai Martaba da Ummi, kasancewar Kakansu ɗaya, daman can auren gida ne aka yi. Idan har zai cilasta Abdallah yin abu to sai dai ya kira Ummi ya faɗa mata, dan baya tun karar Abdallah kai tsaye da abunda ya san zai iya sosa zuciyarsa.


Ya kan zauna yayi fira da shi kamar abokinsa, shine yafi kowa sanin sirrin Mai martaba, gashi ya karanci mahaifinsa sosai, da ido kaɗai zai oya gane abunda Mai martaba yake so ko ƙi.
A duk lokacin da suke tare baka taɓa ganin danuwa a fuskar Mai matarba, idan ba su yi labarin zamanin baya ba, tun Abdallah zai ɗauko masa firar matsalar tsaro da kuma sauran matsalolin da suke damun ƴan negeriya, ko kuma na siyasa.


Wani lokacin kuma idan ya shiga faɗar Mai martaba, zai zauna a kusa da shi ya riƙa karatun alƙur'ane, Mai martaba na sauraro, hakan kuma ba ƙaramin daɗi yake masa ba. Ga shi kuma Major abunda Mai martaba ya daɗe yana mafarki Allah be ƙaddari zai yi ba, ɗansa yayi.
Major General Abdullah Ahmad Mai-doki, an officer of very high rank in the army. Sunan ma kawai idan an faɗa daɗi yake ma Mai maraba.


*Back to Story*


****
Sai da ya bar cikin asibitin gaba ɗaya sannan Mama ta koma ta zauna, sai taɓe baki take, ita dai bata san ko waye ba amman zuciyarta na nasalta masa babban mutum ne, sai dai alaƙar dake tsakaninsa da Namra ne ya tsaya mata a rai.
Bata jiyo abunda suke cewa ba, amman dai ta ga Namra ta tsaya ta yi magana da shi, rai ta ya sosu tana jin kamar tana taya ɗanta kishi, sai yanzu take jin rashin natsuwa a lamarin Namra ya saukar mata.


‘To idan bata san shi ba, ya za'ayi tayi magana da shi? Miye ma na wani biyota har asibiti? Ko ƙe tsakanin su Allah masa ni’


A baɗini take zancen, a zahiri kuma sai taja tsaki, ta gyara zamanta, tana kalle-kalle kamar baƙuwar asibitin.




NAMRA POV.


Tsaye ta tararda shi jikin window, yana kallon wani ɓangare na asibitin.
Har Sallamarta daya amsa be sa ya juyo ba, jar sai da aje abincin ta ƙarasa inda yake tana murmushi.


“Haka ake so Allah ya ƙara lafiya”


Ya kalleta a karkace, yana mai jindaɗi har cikin ransa, shi kansa ya san yana daf da komawa dai-dai, dan yana jin kuzari a jikinsa sosai, ga kumburin kansa nan duk a cire.
Shi kan sa ya san he has to fight for his life, just to achieve his goal, he needs so many things and many things need him, so there's no point of giving up.


“I'm just trying na ga samu sauki sun sallame mu Next week”


“Inshallah indai har kana takawa haka zasu sallame mu da wuri”


Ta faɗa tana shafa bayansa, daɗi har fal har cikin ranta. Bayan ya ci abincin ta zuba masa ruwa ya sha, sannan ya ɗauko masa zancen gyara gida.


“Har yanzu Mama bata je kasuwa ba”


“Eh wai cewa tayi tun da ga wannan kuɗin Anty ta turo miki, ta ce a bar wacan a siye magani da shi, kin ga daman rantuwa tayi abunda yayi saura sai ta mai da mata”


“Kuɗin da Anty ta tura min har na biya bashin gado da su, sauran zan siye tufafi ne da wasu abubuwan kuma Anty tace na siye waya”


“Amman ai kin ci kin ga zinarin ki? Da kin siyar sai a ƙara ayi lalura, idan Allah yasa na warke sai na siya miki wani, wanda ya fishi ma zan siya miki”


Ta ɓata fuska tana kallonsa.


“Ni gaskiya ba zan siyar da zinari na ba, shi ƙadai ya rage min na kuɗi, kuma ko na siyar sana'ah zanyi da kuɗin, dan ba zan riƙa zuwa ina roƙon kowa komai ba”


Ya taɓe baki yana mata wani kallon.


“Hmmm Namra kenan, kina min kallon talaka ko? Har zan ce ki ranta min zinarin ki yi min complain, an faɗa miki zan dauwama a talauci ne hala? Kina ganin bana da mafitar da zan biya ki ko? Nima zan yi kuɗi Namra, zan yi arxiki irin kuɗin da baki taɓa mafarkin Asim zai yi ba, akwai buƙatar nayi kuɗi ko dan na rama bikin da aka min”


“Idan nayi magana zaka ga laifi na, haba Asim shikenan sai ace kullum nice zan riƙa biyar dangi ina roƙon su abu? Yau da gobe sai Allah, na rasa komai dana mallaka, sauran kuɗin nan daya rage min da shi nake cefane, kuma siyen abinci ba haƙƙina bane, kai Allah ya ɗorawa amman ka ɗauki kuɗin nan ka bawa Mama, idan nayi magana kace rantowa kayi alhalin kuɗinka ne na adashe!”


Dammm ya wulga mata wani kallo da mugun faɗuwar gaba. Ya akayi ta sani? Ina ta ji?Ko dai Mama ce tayi subul da baka ta faɗa mata. Ƙoƙarin kare kansa yake yana naɗe tabarmar kunya da hauka.


“Allah sarki rayuwa, talauci be yi ba, a yau har ni kike tunanin na ɓoye miki wani abu, yau ni kike yi ma gori akan kin siye abinci, ai ban san ba dan Allah kika aure ni ba sai yau, kina ganin kamar ba zan iya rayuwa babu ke ba ko? Kina ganin kamar da arzikin ki nake ci ko? Kina ganin ke kika min magani ko? Da gaskiyar Mama yanzu cewa za ayi duk ni na ƙarar miki da komai na ki, daman haka kike so ace na auro ki na zo na aje ki ina cin amanarki ko? So that ki samu damar fakewa da na yaudare ki, daman na san ba dan Allah kika aure ni ba”


Tun da ya soma kwarara zantukansa kallonsa kawai take tana mamakin kalamansa, wasu zantukan ma bata san inda suka dosa ba. Yau kam ya fara fito mata a kowaye shi, ya bayyana mata abunda zuciyarta ta soma zargi akansa.


“Na bar jindaɗin gidan mu, na zabe ka. Na watsar da karatuna na bika,


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login