Showing 195001 words to 198000 words out of 281103 words

Chapter 66 - ZAGON KASA Book Complete Document by Khadeeja Candy .txt

28 Dec 2024

61284

da kuma number wayarki da wanda za a kaiwa saƙon”


“Zan dai baka number na, amman ban da number wanda za'a kaiwa saƙon, shiyasa na rubuta maka addireshin sa, dan Allah ka taimaka min ka kai masa har gida”


“Okay ba matsala, amman gaskiya ko baki yo ba sai kin bada dubu uku, dan za a kai masa har gida ne, kuma kin ga yanayin da ake ciki ba mu cika son karɓar saƙo ba ma”


“Ina zuwa”


Haleema ta faɗa, sai ta juya ta nufi gurin motarta, bata ɗauki lokaci ba ta dawo ta miƙa masa dubu uku ƴan ɗari biyar biyar.


“Gashi amman dan Allah ka tabbatar saƙon ya isa, ki bashi number wayarki so that idan ya kai sai ya kira ya faɗa miki”


Ta ƙarasa tana kallon Amira. Ba musu Amira ta karɓi number wayarsa ta saka a wayarta, sai ta masa flashing number ta ta fito, sai da ta tabbatar yayi saving sannan ta juyo ita da Haleema suka nufi gurin da suka faka motar su.
Haleema ce ta fara shiga sannan Amira, har suka isa gida babu wanda yace da wani uffan, Haleema na wani tunanin na dabam, Amira ma haka har suka isa gida.
Tun kamin su faka motarsu Haleema ta gane yayanta ya dawo, ganin yadda sojojin suka koma cikin natsuwarsu sosai.


“Big bro ya dawo kenan!”


Ta faɗa tana zare key ɗin motar, Amira dai bata ce komai ba, har suka fita motar suka nufi ƙofar shiga falon.
Gabanta ya faɗi sosai lokacin data saka ƙafarta cikin falo, ta yi ido biyu da Abdool.
Abinci yake aunawa a cikinsa yana zubawa Ummi satti, yanayin fuskarsa kawai zaka kalla ka fahimci baya cikin damuwa, dan annuri ne shimfiɗe a fuskarsa.


Cikin sanyin jiki Haleema ta ƙarasa kusa da Ummi dana wasar haƙura, dan tasan laifinta na fita bata faɗawa Ummi ba.


“Daga ina kike?”


Ummi ta tambaya fuskarta babu alamun dariya. Ta ɗan sosa kai tana tunanin irin ƙaryar da zata yi ma Ummi dan bata jin zata iya faɗa mata gaskiya.


“Ya Abdool an sauka lafiya”


Amira da ke can gefe Haleema ta miƙawa Abdool gaisuwa. Ba tare daya ɗago ya kalleta ba ya amsa.


“Lafiya ƙalau”


Sai ya miƙe tsaye yana yi ma Haleema wani kallo.


“Daga Ina kuke?”


“Pizza na ce ta raka ni na siyo kuma ban samu ba”


Ta faɗa tana pretending like she's serious.


“Amman idan zaku je siyen Pizza sai kawai ki kama hanya ku fita without permission?”


“I'm sorry Ummi i promise ba zan sake ba”


“You're very stupid, haka kawai zaki saka kafa ki fita ba tare da kin faɗa ba? Baki san rayuwarku tana cikin haɗari ba? Ba ni kaɗai za a riƙa farauta ba har da ku”


Abdool ya faɗa yana kallonta har handkercheif ɗin dake hannunsa ya faɗi.


“Haba Big Bros Wallahi ba zan ƙara ba, dan Allah ku yi haƙuri”


Ta faɗa kamar mai shirin yin kuka. Amira kan idonta na kan Abdool, annurin fuskarsa kawai take kallo, a ɗayan ɓangaren kuma tana Allah-Allah ya manta da handkercheif ɗinsa ta ɗauke, ta yadda zata fi jin daɗin tuna sa idan tana tare da shi.


“Miya hana ki zuwa makaranta?”


Ya tambaya yayinda ya risina ɗaukar handkercheif ɗin.


“Yau ba mu da lacca sai four”


Be sake ce mata komai ba, ya kalli Ummi.


“Zan je gurin Mai Martaba”


“Mu zaka ku? Tun da ka sauka naga ka kira shi fa, akwai abunda kuke shiryawa ko?”


“Kedai Ummi kawai ki sa ido ki yi kallo, wannan tsakanin ɗa da uba ne”


“Idan tayi tsami ma ji, miye sunan in-law ɗin tawa?”


“Da saura Ummi, bata kama hanyar zama in-law ba tukuna, sai mun yi settling abubuwa. Her name is NAMRA...!”


Wani irin faɗuwa gaban Amira yayi har sai da kanta ya tsara.


‘Namra’


Ta maimaita sunan a ranta tana, tuna wacan Namra wacce take ganin ita ce silar shiga ta wannan halin rayuwar. Kamin ta kalli Abdool da ya kai hannu ya ɗauki apple ya fice yana wasa da shi. Ummi kuma ta tashi ta nufi Kitchen, sai ya rage daga Amira sai Haleema ne a falon. Amira ta matsa kusa da Haleema ta dafa kaɗatar.


“Haleema zan shiga ciki, idan Ummi fa faɗi abunda za a girka da ranar nan kya sanar da ni please”


“Okay Sleep well”


Cikin sanyin jiki ta juya ta nufi ɗakin Amal da ya zame mata kamar ɗakinta.




ABDOOL POV.


Cike da zumuɗi ya isa faɗar Mai Martaba, kai tsaye ya wuce part ɗinsa da yake zama. A babban falonsa ya same shi, Hajiya Shafa na haɗa masa abun karyawa, yana ganin ɗansa ya washe haƙura, wanda hakan sam be yi ma uwaegidan Mai Martaba daɗi ba.


Cikin girmamawa Abdool ya gaishe ta, ta amsa masa kamar babu komai sannan ya gaishe da Mai Martaba yana masa kirari.


“Ba wani daɗin baki da zaka min sai da ka fara gaishe ta sannan zaka miƙa min gaisuwa”


Dariya yayi shi da Hajiya Shafa, sannan ya ce


“Ayi haƙuri Mai Martaba, zafi zafina na zo dan labarta maka komai”


“Muma nan ai mun aje maka labari har da ɗuminsa”


Hajiya Shafa ta faɗa. Abdool ya ce


“Tau a fara bani na sha”


“Wannan albishir kuma Mahaifinka zai maka shi”


Ta tashi ta fice tana dariya. Mar Martaba ya miƙa ma Abdool tea da aka haɗa masa shi kuma Abdool ya aje tea a gefe ya shiga haɗa ma Mai Martaba wani yana labarta masa labarin Namra.


Sai kusan Sha ɗaya da rabi suka gama karyawa tare da Mai Martaba yadda Abdool ya zage yana cin abincin ba zaka ce ya ci abinci gurin Ummi ba.
Mai Martaba ya jinjina lamarin Namra sosai kuma ya tausaya mata duk da be ganta, bama abunda ya fi taɓa shi kamar yadda ya ji tana raɓe a gidan wasu bayan kuma uwarta da ubanta suna raye.


“Amman Ina ka haɗu da ita?”


Abdool ya yi shiru yana tunanin faɗawa Mai Martaba gaskiyas lamari.


“Ranka ya daɗe ina binka bashin albishir fa”


“Albishir ɗin ka, zan faɗa maka idan ka samu natsuwa kun kai ƙarshen wannan matsalar”


“Yanzu ya kake ganin za a ɓullowa lamarin?”


Mai Martaba ya gyara zamansa.


“Abunda za mu yi, zan sa a rubuta masa wasiƙa daga nan Masarautar zuwa can inda yake, ai kana da addireshinsa ko?”


“Eh ina da shi, dan nasa an min bincike akan sa”


“Okay zamu saka a aika ma Sarkin Musulmi na sokoto shi kuma zai aika wani ya kai masa wasiƙar”


“Amman Mai Martaba me zai hana ka aika masa kai tsaye?”


“Ai mu sarakuna bama haka, dole ne sai sarkin gari ya san da abunda wani sarkin yake so a garinsa. Musamman babban sarki kamar shi”


“Okay zuwa yaushe za a aika?”


“Yau zamu aika, ina tunanin gobe zata isa gare shi”


Abdool ya ji daɗin haɗin kan da Mai Martaba ya bashi sosai da sosai. Daman ya tsammaci haka, dan ƴasan yana samun goyon bayansa a dukan abunda zai yi.




KALSOOM POV.


*Bayan wata biyu*


Tun da aka soma shigo da kayan har aka aje,be ji motsinta a falon ba hakan ya tabbatar masa da tana kitchen, kai tsaye ya nufi kitchen ɗin, fuskarsa ɗauke da murmushi. Ta baya ya yi hugging ɗinta ya aika mata da kiss a gefen fuska.


“Me kike girkawa?”


Wuƙar dake hannunta ta aje ta juyo tana dariya.


“Hancin ka zan girka”


“An ya zaki iya cin hancin na?”


“Kwarai kuwa ta yadda Amaryar nan da taga baka da hanci zata ce ta fasa auren”


Ƙyalƙyalewa yayi da dariya, ya zageye kunkurunta da duka hannayensa.


“Shikenan sai ki kashe min kasuwa ko?”


“Eh mana ai ƙara ni kaɗai zan riƙa ganin kyan ka”


Ya riƙa hannunta yana dariya.


“Zo ki ga wani abu”


Gabanta yayi mugun faɗuwa, haka kawai ta annayana a ranta ba abun alheri ba ne, cire hannunta ta yi cikin na shi.


“Bari na juya miya sai na zo”


Be mata musu ba, ya juya ya fice. Ta ɗauki minti goma a kitchen ɗin tana ta fargabar fita, duk da bata san abunda zai nuna mata ba, tana ji a ranta kamar ba alheri ba ne. Ba ƙaramin dauriya ta yi ba kamin ta wanke hannayenta ya juya miyar sannan ta nufo ƙofar falo.
Tana ganin akwatuna jere a tsakiyar falonta, bugun gabanta ya ƙaru, idonta kuma ya cika da hawaye. Ga invitation card da kwalayin minti da cinka a saman akwatunan mai yawa ana ɗora. Jikinta yayi sanyi sosai, hawayen dake maƙalle a idonta ya gangaro zuwa kumatun ta.


“Ashe haka Rashida ta ji lokacin da za a auro ni ko?”


Ta faɗa muryarta na rawa. Ɗagowa Hilal yayi ya kalleta, sai ya miƙa mata hannu alamar ta zo, sannu ta fara takowa har ta kawo inda yake ta miƙa masa nata hannun. Sai ya zaunar da ita ƙasan kujerar ya ɗora mata hannayensa saman kafaɗunta, kasancewar shi yana saman cushion zaune ne.


“Ki duba ki ga idan akwai abunda babu zan ƙaro”


Kai ta girgiza ta miƙe tsaye.


“A'a ni nabar mata kayan duka ka kai mata, ina da kayana”


Shima.ya miƙe tsaye.


“Na sani ai, ba tsirara na auro ki ba”


Sai ta yi ƙasa da kanta tana hawaye. Hannunsa ya saka cikin nata yaja zuwa ƙirjinsa, sai kawai ta rushe da wani irin kuka mai ban tausayi.


“Sorry dear, zan canja miki komai idan kina buƙata, just be strong”


Kuka tayi sosai har sai da ta ɓata mishi gaban riga da majina, sannan ta sake shi ta nufi toilet ɗin falo saboda amai da taji ya cika mata baki.




ASIM POV.


Tun safe ya tashi ko da goma tayi yana cikin garin sokoto, A hotel ɗin Shukura ya kama ɗaki, sai da ya ɗan huta sannan ya kira Ubangidansa ya sanar masa da ya iso. Ya bashi tabbacin sai dare zasu gana, da alama can zai kwana inda yake, dan ya faɗa inda zai same shi a gidansa da ke Sama road.
Fitowa yayi ya biya kuɗin wuni ɗaya, sannan ya ɗauki hanyar gidansu, zuciyarsa cike da nishani, yana mai jin kansa lallai shi a yanzu wani ne.


Ko da ya isa unguwarsu ƙarfe ɗayan rana yayi, dan haka irin mazan nan masu zaman kashe wando duk basa nan sai da yamma suke zama, kasancewar unguwar minannata, haka suke da yamma ta yi, amman hakan be hana wasu ganinsa ba, dan tabbatar da shi ɗin ne yasa wasu gayu zuwa su bashi hannu shi hannu su gaisa suna masa yaushe gamu.


“Kai ke da wannan?”


Ɗaƴan ya faɗa yana nuna motar dake kusa da su.


“Eh Wallahi sai a taya mu addu'ah”


“Toh Allah ya taimaka ya tsare. Kace kai ma ka shigo gari, ko da yake kana sirikin Manjo Usman ai dole ka hau wannan motar”


Ɗan murmushi yayi.


“Babu ɗigon dukiyarsa nan”


Duk dariya suka yi, ba dan sun yarda ba, sai suka ƙara gaba suna nasu zancen.


Da farinciki ya shiga gida, yana doka sallama kamar wani baƙo. Da gudu Mama ta fito dan tabbatar da muryar ɗan na ta ne ko bashi ba, ganinsa yasa ta daki ƙirji tana ƙare masa kallo


“Ibrahim kai ne? Allahu akbar”


Ta shiga shafa kayan jikinsa tana kuka, shi kam sai dariya yake yana kallon ƙanensa dake sanye da uniforn ɗin makaranta suna kallonsa. Da alama suma basu gama tabbatar da shi ɗin ba ne.


“Ji yadda kuka tsaya kallo na”


Sannan suka yi dariya suka rugo a guje suka rumgume shi, suna murna. Sai da suka gama zumuɗinsu sannan Mama ta ɗauko tabarta ta shimfiɗa masa tsakar gida, ko zama be yi ba sai ga maƙota sun soma shigowa ƴan ganin gwan, kar ayi ba su, dan kace kwabo har labari ya fara zaga unguwar.


Ya sha gaisawa da mutane sosai, dan sai a lokacin wasu ke masa ya jiki. Sai kusan La'asar ya samu keɓewa da Mama suna tattauna lamuran duniaya.


“Amman wannan matar Allah yayi mata tausayi, irin wannan hidima haka? Ko dai auren ka zata yi? Allah dai yasa taimakon Allah ne take maka”


“A'a ai matar babbar macece, kuma ta san ina da mata, Allah yayi mata tausayi ne kawai”


“Ai har gobe na Allah basa ƙarewa, Allah saka mata da alheri, ba irin waɗannan lalataccin mutanen ba, ai na so ka zo da Namra ta yadda zaka je kaita su ga irin buɗin da Ubangiji ya yi maka”


Ya ɗan yi shiru kamin ya ɗora da.


“Ai na saki Namra...”


Mama ta daki ƙirji tana buɗe baki tare da gwalo ido.


“Kai ɗan nan? Yaushe?”


“Yanzu an kusa sati biyu gaskiya, bata zo nan ba?”


“A'a wallahi ai da tazo da sai mun samu labari”


“Daman na yi tunanin ba zata zo nan ba, amman nasan duk inda taje dole zata dawo”


“Hmmm ai ƙara ma daka sake ta, sai mutane gane ba dukiyar ubanta bace,dan nasan yanzu duk wasu haka zasu ɗauka, kai lokacin ma da baka da lafiya har da masu cewa wai ubanta ne ya ɗauki nauyin komai, ko zaka maida ita sai nan gaba”


“Wallahi Mama ina sakinta sai abubuwa suka buɗe min komai yanzu ba ni da matsalarsa, yanzu haka zuwan da na yi na zo ne na faɗa muku na samu matar aure kuma zan siya muku gida mai kyau na miliyan biyu haka sai ku zauna”


Tashi Mama ta yi tana rawa, kamar wata bayarabiya sannan ta ɗire tana ma Allah godiya tare da sujada.


“Kai ɗan nan Allah ya zuba maka albarka, da mahaifinka na nan da rai da ya gode maka”


Dariya yayi yana mai jin kansa sosai da sosai. Sun deɗe suna fira kamin ya cire kuɗi mai yawa ya bata wai ta siyo kayan abincin, gida kuma ta sa abincika mata idan an samu ayi masa magana. Sai da magariba ta yi. sannan ya yi wanka ya canja kayan daya zo da su, ya gyara jikinsa ya bar gidan sai ƙamshin turare ya ke.




RASHIDA POV.

Juyi kawai take saman katifar da saboda wani mugun ciwo da zuciyarta ke mata, tea ma daker ta iya tashi ta haɗa ta sha.
Bata yi mamakin ganin irin kiran da take ta samu daga ƙawayenta ba, ciki har da Asmee, sai dai bata damu da ɗauka ba dan a tunaninta ko zasu tambayeta dalilin barin gidan iyayenta ne, taji zafi sosai da taga har da ƙawayen da take nesa da su ne cikin masu kiranta, babu shakka labarin barin gidan iyayenta ya same su kenan.


Wannan tunanin yasa ta ƙara jin wani irin zafi ya rufe mata zuciya, yana ɗaya daga cikin dalilin daya sa ta ƙaurawace whatsapp saboda yawan tambayar gaskiyar mutuwar aurenta da ƙawayenta ke yi, wasu kuma suna jajanta mata akan mutuwar Rafiq.
Yanzu ma wayarta ce take ringing, wannan karon Momi ce dan haka ita kam ba zata ƙi ɗaukar wayarta ba, cikin hali na kamar marar lafiya ta ɗauki wayar ta kara a kunnenta.


“Hello Momi”


“Ke Rashida kin san abunda ya ke faruwa kuwa?”


Ta tashi zaune da sauri cikin rashin gane zancen da Momi take mata.


“Miya faru?”


“Kina da labarin Hilal zai ƙara aure?”


“Eh na taɓa ji amman ban tabbatar ba”


“Kin san Teema ce matar da zai aura”


Haka maganar ta riƙa yi ma Rashida yawo cikin kai har tana jin kamar ɗakin ya juya mata.


“Wace Teemar? Ba dai ƙawata ba ko?”


“Ita fa”


“How true it's?”


“Ga Iv nan Ummu Faisak ta zo da shi, ko ba ita bace Fatima Jafar Mai Goro?”


“Ita ce, ta ya hakan zai faru?”


Tayi saurin kashe wayarta ta kira Asmee, bugu ɗaya ta ɗauka.


“Hello na kira baki ɗauka ba, kinji abunda yake faruwa kuwa?”


“Da gaske ne kenan?”


“Ashe kin ji”


Ta katse kiran ta jefar da wayar saman katifa cike da tashin hankali, rasa gane ta yi inda take sama ne ƙasa ne, duniya ne ko lahira, sai juya mata ɗakin ke yi, tana numfashi guda guda.


“It can't be Teema, idan har ta tabbata da gaske ne sai na ci Uwarki...!”


Ta faɗa cikin wani irin zafin rai, a take ta zari mayafinta ta fice.




YASMEEN POV.


Yana jefar da scul bang ɗinsa, yasa hannu yana ƙwaƙwala gurin kashinsa, yana tafiya ararrabe ya nufi kitchen.


“Momee na dawo”


Be same ta a gurin ba, sai Mai mata raino ya samu tana girka mata abinci.


“Ina Momee”


Ya faɗa yana jan rigarta.


“Tana ɗakinta”


Juyawa yayi da fuskar kuka ya nufi ɗakin nata, yana cigaba da ƙwaƙwala gurin kamar mai jim ƙaiƙayi. Da hannu ɗaya ya tura ƙpfar ɗakin ya shiga.


“Momee na dawo, kin ce zaki ba ni chocolate da safe”


Harara ta watsa masa dan ta tsani wannan soshe-soshen da yake yawan yi.


“Ba zaka cire hannunka a nan ba? Zan ci ubanka Adnan idan baka daina saka hannu a gurin ba, kai ƙazami ne ko?”


Ya yi saurin cirewa.


“A'a Momee ciwo ne yake min”


“Bari Dadee ya dawo ya saka maka magani, yana can ɗakinsa”


Ya faɗa, dan hana kowa ya saka masa ganin sai shi kaɗai, hakan yasa ya aje ganin gurinsa shi kaɗai zai riƙa saka masa ganin.


“Zo mu gani”


Ta aje Namra dake hannunta, ta riƙa wandon makarantarsa ta cire, sannan ta sake cire pant ɗinsa.


“Wannan ciwon yaƙi ya warke, ko dai maci ɗan wawa ne, amman kuma shi ai ba nan yake fitowa ba”


Ta ƙara buɗe gurin da kyau tana dubawa.


“Momee da zafi, Dadee yace na daina bari a na buɗewa, kuma ya ce karna faɗawa kowa zai dake ni idan na faɗa”


“Okay sorry ina duba maka ne, ai idan ya ji nice ba zai dake ka ba”


“Ya ce har da ke, kuma ya ce idan na faɗa abunda yake min sai ya yanke kamar yadda ake yanka rago, ya cinye nama na, ya soye”


Dariya ta yi dan bata ɗauki abun gaske ba.


“Wasa yake maka, ba zai maka komai ba”


“Wallahi yayi rantsuwa, kuma ...”


Ya faɗa cikin muryarsa mai kamar kuka. Yasmee ta juyo da shi, ta zaunar.


“Kuma me Adnan..?”


Sai kawai ya soma matsa ƙwallah.


“Talk to your Mom”


“Yace zai ba ni duka da yawa idan na faɗa”


“Minene”


Ganin kamar ya tsorata yasa ta ƙyalƙyale da dariya ta soma masa cakulkuli, sai ta jashi jikinta ta rumgume.


“Zo mu yi sirri da kai, ba zan faɗawa kowa ba”


Cikin dariyar cakulkulin da take masa ya ce.


“Allah zaki faɗa”


“Ba zan faɗa ba i promise”


“To kawo kunnenki”


Ta matso da kunenta bakinsa. Kaɗan-kaɗan ya raɗa mata.


“Dadee yake sa min abun shi nan, a baya”


Ta ɗago da mamaki tana kallonsa.


“Kai Adnan mu yi gaskiya da kai”


Kamin ya ƙara cewa wani abu mai aikinta ta ƙwalo mata kira.


“Anti Ana sallama”


Sakin sa ta yi ta tashi ta nufi falon, Zuciyarta da ɗayan biyu. Mai gadinta ta samu tsaye a falon riƙe da kwali yana shirin miƙa mata.


“Ga saƙo wani ya


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login