Showing 222001 words to 225000 words out of 281103 words
Chapter 75 - ZAGON KASA Book Complete Document by Khadeeja Candy .txt
ƙofar falon, sai mai aikinsa ta buɗe masa ƙofa.
“Sannu da zuwa”
Wani wawan kallo ya jefa mata, ya wuce ciki, ita kuma ta koma kitchen ta cigaba da abun da take.
TEEMA POV.
Yau da wuri ta gama girkinta saboda yau da fara amfani da abubuwan da ta karɓo gurin bokanta. Zoɓo ta haɗa masa ta zuba abun a ciki sannan ta saka wani a miyar giɗa, kana ta bi gidan ta turare ko'ina.
Sai da ta gama sannan ta shiga ta sake wanka, ta chaɓa ado, ta buɗe durowarta ta ɗauko wani rubutu ta zuba a hannunta ta yaye zanen gadonta ta watsa shi, sannan ta shafa wani a ɗayan hannunta, tana jiran ya dawo ta samu sa'ar shafa masa a jiki.
Tana jin tsayawar motarsa ta koma bayan ƙofa ta laɓe, a zatonta shine zai shigo ashe direba ya aiko ya kawo su Ezza da Ulfa. Sai duk suka watsar da jakunkunansu saman kujerarta. Ganin shiru-shiru ba a shigo ba yasa ta fito ta nufo falo.
“Kan Uban nan, uban wa zaku jefarwa da jaka nan? Ku kwashe su da sauri ku kai su ɗakin ku, kuma kar a sake zama min saman kujera, wannan ai rashin tarbiya ne manya su zauna a kujera ku ku zauna ni ba zan ɗauki wannan ba”
Ulfa ce uwar tsoro da sauri ta nufi jakarta ta ɗauka ta nufi ɗakinsu. Ezzah kan banza ta yi kuma ta ƙi sauka daga saman kujerar.
“Ke dan Ubanki ba da nake ba”
Sai a sannan ta ɗago kai ta kalleta.
“Mu a saman kujera muka saba zama”
Ta faɗa tana sauka ƙasa, badan hannun Teema da ke da rubutun ba da babu abunda zai hana ta dake ta.
“Wallahi kuka kuskura min rashin kunya zaki wahala a gidan nan”
Sai kawai ta miƙe tsaye ta nufi ɗakinsu, Ulfah dake tsaye bakin ƙofar ɗakin tana leƙo ta shige da sauri.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *79*
Su Maryam na wucewa Zinatu ta rufa musu baya ita ma tana murmushi. Hajiya Barau kuma ta koma part ɗinta, bedroom ɗinta ta shige ta ɗauki wayarta ta kira Uzair. Bugu biyu ya ɗauka, saman-sama ya gaisa da ita saboda shi ma be cikin daɗin rai, sannan ta labarta masa Namra ta dawo, he was shocked and surprise, sai ya ji maganar kamar daga sama.
“Da gaske kike yi?”
“Wallahi da ido na na gani, yanzun nan Alhaji ya dawo tare da ita, kasan na labarta maka ai Sarkin Katsina ya aiko ƴana nemansa ni na ɗauka ko wani abu ta yi, sai gashi kuma na ga sun dawo da ita”
“Aurenta ya mutu ne?”
“Bari naje gurin Alhaji na ji”
“Okay ki sanar da ni duk abunda kika ji”
“Tau”
Tana kashe wayar ta nufi part ɗin Abbah. Ko da ta shiga yana banɗaki, har ta zauna sai kuma ta yi saurin tashi ta koma part ɗinta, fruit ta yankawa Abbah ta saka madara, ta ɗauka ta nufi koma part ɗinsa. Wannan karon zaune ya same shi saman gado yana waya, sai ta zauna kusa da shi tana riƙe da fruits, sai da ya gama wayar sannan ya kalleta da murmushi a fuskarsa yace.
“Hajiya fatar dai lafiya”
“Lafiya ƙalau bana da ikon da zan zo na ga miji na ne? Ga ɗan abunda na haɗa maka, abinci na kan wuta ban ƙarasa ba”
“Ai bama na ma jin yunwa kamin na taso sai da muka ci abinci”
“A can gidan Namra?”
“A'a a gidan Mai Martaba Ahmad Mai-doki Sarkin Katsina, dake Kaduna”
“Ban gane ba, baka labarta min zaka dawo da Namra ba, duk lokacin da na tambaye ka sai ka ce min wani babu wata matsala dai, ya akayi ka dawo da ita bayan kace ba zaka karɓe ta ba?”
Wani kallo Abbah yayi mata.
“Ya kike magana kamar wacece bata ji daɗin dawowar Namra ba? Komai ta yi min aduniyar nan she still my daughter, ko lalacewa ta yi dole za'ace ƴar gidan nan ce, ballantana ina son ta, kawai dai ta ɓata min rai ne kuma ta gane kuskurenta”
“Ta gane kuskurenta kamar ya? Alhaji yanzu baka tunanin mutane zasu zarge ka akan ka yi magana kuma ka zauna? Wannan ai talalace ka yi mata yarinya ta yi laifi kuma yanzu da miji ya wulaƙanta sai kace kayafe mata haka ake yi?”
Abbah yayi murmushi, yana gyara zamansa.
“Baki gane abun ba ne Hajiya wato da muka sauka Katsina...”
Ya kwashe labarin abunda ya faru ya faɗa mata, daman can Anty Amarya ce ta hana a faɗawa kowa wai tana son kawai su ganta ne. Mire baki Hajiya Barau ta yi ta miƙe tsaye.
“Yanzu Alhaji im ban da su mai da wani iri sai da Asim ya gama wulaƙanta ta ya sake ta sannan yanzu su haɗa baki da uwarta su nemo wani a kai ga Sarki, wannan ma ai rainin wayo ne, yarinyar ta yi wasa da hankalinka, yanzu kuma kai har ka yarda ta gane kuskurenta haba Alhaji wannan ai ka bata damar ƙara aikata abunda ta aikata ne kawai”
Wani wawan kallo Abbah ya watsa mata.
“Na bata damar, ko yanzu Namra ta kawo min wanda take so zan aura mata, daman na lura da ke ba son yarinyar nan kike ba, mi ko duk wanda be son Namra bana son shi, dan Namra jinina ce, ƴata ce, ina kula da yadda kika ɗauki matar nan ita ba haka ta ɗauke ki ba, baki son ta ita da yaran ta, ana gobe za mu bar garin nan nan cikin falon nan nawa kika saki wata magana wai Allah yasa Namra bata yi mana jaye-jaye ba, a gaban uwarta amman ta miki kawaici ta tashi ta bar miki falon bata ce komai ba, shiyasa na zaɓi zuwa da ita na ƙi na tafi da ke, iya haƙuri matar nan ta nayi yinsa da ke amman ke baki ga, ina kula da abun nan da Namra ta yi kamar daɗi yayi miki, ba zan ɗauka ba kar bakin ki ya sake furta mummun kalma akan ƴaƴana!”
Ta riƙe baki.
“Alhaji kai kake faɗa min wannan maganar akan Namra? Daga na faɗa maka gaskiya har kace wai bana son ta ita da uwarta? Kuma ka ce baka da so na saboda ƴarka? Anya banza matar nan ta barka Alhaji”
“Ba banza ta bar ni ba, ta kula da ni fiye da yadda kike tsammani, dan tana son ki ke da ƴaƴanki, ba kamar yadda kike nuna mata ba, kuma daga yau sai yau, kar wani munafurci da wata magana marar daɗi ta sake fitowa bakinki akan Ƴaƴa ko wannan matar tau a bakin auren ki! Kar wacce ta aake tadarmin fitina yadda na ga dama haka zan yi a gidana”
Mutuwar tsaye Hajiya Barau ta yi a gurin, tana mamakin Abbah ta ya juye kamar ba shi ba, wai yau shi yake faɗa mata wannan maganar, har yake cewa bakin aurenta. Uffan bata yarda ta sake cewa ba, ta nufi ƙofa cike da nauyin jiki fice sun-sun-sun, hannayenta a baya tana jin kamar an ɗora mata dutse saman kai.
NAMRA POV.
Cikin falo suka riƙa hugging ɗin juna ita da ƴan'uwanta, suna jin kamar su haɗe juna ita da su, sai faman kuka suke. Anty Amarya ta fito daga bedroom ɗinta fuskarta da dariya ta ce
“To ko haɗe ta zaku yi?”
“Anty Faɗa mana yadda aka yi ta yarda ta biyo ku kuma har Abbah ya amince”
Aisha ta faɗa tana laƙƙame da wuyan Namra.
“To ku sake ta taje ta yi wanka ta shirya zan baku labarin komai”
Aisha da Hindatu ne suka saketa yayinda Maryam ta laƙƙame hannunta suka nufi bedroom tare. Bayan sun tashi Zinatu ma ta tashi ta nufi part ɗin Mahaifiyarta. A sannan ne Anty take tambayarsu yaushe Zinatu ta zo.
“Tun ranar da kuka tafi, wai faɗa tayi da mijinta ya ce taje gida, shi ne wai ta baro masa yaransa”
“Subhallahi, miya haɗa su haka?”
“Wallahi bata faɗa ba, ai kin san Hajiya ba zata bari ta faɗi gaskiya ba, dan ita Hajiya ma ce mana ta yi bikin Maryam ta zo”
“Tau Allah ya sauwaƙe yayi mata mafita, ku tashi ku girka mana abinci dan ni dai ba zan ci taliya ba”
Hindatu ta mike tsaye tana dariya.
“Komai kuke so za a muku, sai ku ba mu labarin abunda ya faru”
A ɗaki da suka shiga Namra take labartawa Maryam irin abunda Asim yayi mata, da yadda ta yi rayuwa gidansu Lamido da kuma haɗuwarta da Abdool ya yadda ya haɗa ta da su Anty.
“Ke ni wallahi na jidaɗin da auren ya mutu kuma cikin ya zube, dan zai iya cewa ya maida ki ko dan ɗansa ko kuma ya ce zai maida ki kamin ki cika idda amman yanzu ba ciki ba goyo dole ya ƙyale ki dan ubansa, tsinan nen banza”
“Ba laifinsa ba ne Maryam, laifina ne a gareni ya ga wannan damar kuma ni na zaɓe shi sama da iyayena. Amman yanzu Alhamdulillahi tun da Abbah ya ƙarɓe ni”
“Gaskiya nima na jidadin hakan ciwon Anty zai warke, kuma za'ayi biki da ke, amman dai wannan yaron son ki yake ko?”
“A'a ba so a tsakanin mu, bikin wa za'ayi?”
“Bikina mana ni da Hindatu sati mai zuwa za'a ɗaura aure, Wednesday za'a fara biki”
“Amman shinw ba a faɗa min ba?”
“To ba kin zaɓi wasu family sama da mu ba”
“Haba Maryam, ai komai na zama ni ƴar'uwarku ce jininku, be kamata ku min haka ba”
Maryam ta laƙƙamo kafaɗarta tana dariya.
“Ai yanzu kin dawo ma hanya, komai da ke za'ayi Maman su Babanmu”
Ɗan Murmushi Namra ta yi ta miƙe ta shiga wanka. A wunin ranar haka suka riƙa treat ɗin Namra kamar wata sarauniya, sai faman dare-dare suke suna rumgume ta. Suna cikin haka sai kawai ta fashe musu da kuka da kuma dariya lokaci ɗaya.
“Ban taɓa tunanin rayuwa zata dawo haka ba, i miss my family a lot”
Hannu Aisha tasa ta share mata hawayenta, sannan ta miƙa mata wayarta da ke ringing.
Namra na karɓa ta zaro ido.
“Asim ne”
“Asim”
Maryam ta amsa da ƙarfi, kana ta ce.
“Ba ni shi”
Anty ta ɗaga mata hannu
“No barta ta yi picking mu ji me zai ce”
Sai da ta yi ajiyar zuciya sannan ta danna picking ta kara a kunne.
“Hajiya Namra kenan! Ina kika shiga na yi nemanki cikin garin Katsina da kewaye baki ciki”
“Ina kake tsammanin zan kasance bayan gidan Ubana”
“bakya giɗan ubanki kam dan na bincika aka ce min baki can, faɗa min inda kike je? Karki damu da tambayar da nake miki ina son naji lafiyar Baby na ne”
“Bka da wani Baby Asim saboda ka zaɓi rabuwa da ni ne saboda shi”
“Yanzu kuma ina son abuna sai yaya?”
“Amman babu kaskantacce wulaƙantacce wawa kamar ka Asim, yanzu da baka da kunya zaka kira ni ka ce min wai lafiyar cikin ka zaka ji?”
“Bana da damar hakan ne? Ai Allah ya ɗora min haƙƙin kula da ke har sai kin haihu, kuma dole ne na bincika ko da kina da buƙatar wani abun sai a kawo miki”
“Kai har kana ganin ka yi arzikin da zaka iya ɗaukar nauyin cikin ka, ka daina wahalar da kan ka dan ni yanzu babu ciki a jikina kuma karka sake kirana”
Tana kaiwa nan ta kashe wayarta tana huci. Anty bata muƙatar ta faɗa mata dalilin kiran nasa dan ta fahimci komai. Ko minti biyu ba tayi ba ya aiko mata sako.
_Wallahi duk kika zubar min da ciki sai mun shiga kotu da ke_
Namra na gama karanta ta nunawa Anty.
“Karki sake ɗaga wayarsa karki sake ce masa komai, har sai mun ji abunda Abbah ki zai ce”
Maryam ta yi ƙwafa.
“Wallahi samun family masu haƙuri irin wannan yana da wahala, wlh da wani guri ne da sai an wulaƙanshi kam uban nan...!”
Anty ta nuna ta yatsa.
“Maryam ki cire wannan zafin ran da kike da shi, aure zaki yi kuma mace kike, abunda duk haƙuri be baka ba rashinka be baka shi, duk wanda ya ci amana kin taɓa ganin ya ƙare da kyau, kar dai karka yarda ka ci amanar wani barshi shi ya ci amanar ka, ki zuba masa ido ki gani ba zai ga da kyau ba”
“Amman wani lokacin mutun yana buƙatar gargaɗi kai, da wannan haƙuri kike ta cutar da mu da kan ki, gashi nan a gida kullum mine ba mu da gata, komai na gidan nan Hajiya ce take da iko da shi, da an yi magana sai ki ce ayi hakuri, fisabilliah har na waje kuma sai a riƙa bari suna takamu”
Ta ƙarasa tare da miƙewa tsaye ta nufi bedroom ɗinta.
“Ke kan Maryam Allah ya shiryaki, da wannan rayuwar babu inda zata kai ki, ni ban san inda kika ɗauko wannan baƙin hali ba, ni dai ba haka na ke ba”
Bayan sun yi Sallah magariba, Anty ta shiga part ɗin Abbah da abinci a hannunta ta tsakura masa labarin abunda ya faru.
Washe gari Namra ta daɗe tana bachin safe saboda gajiya da kuma kwanciyar hankalin yau tana gida bata da wata matsala. Maryam ce ta shigo ita da Aisha suka tashe ta wai zasu je siyen wasu kayan kitchen, kuma ta fito da Yasmin a falo tana jiranta. Mulmula ta riƙa yi saman gadon sai da suka fice, sannan ta miƙe tsaye tana miƙa ta shiga bathroom, bakinta ta wanke, a nan take kallon kanta a madubi ita kanta ta san ta chanja kamar ba ita gaba ɗaya ta fita daga kamamninta, ta yi baƙi sosai idonta sun ƙara fitowa.
“Namra ko har yanzu baki tashi ba”
Jin muryar Yasmin yasa ta yi saurin barin gaban madubi ta nufo ƙofar fita tana zumuɗin haɗuwa da Yasmin.
“Anty”
Ta faɗa jikin Yasmin suka rumgume juna.
“Ashe kin ji na dawo”
“Eh Gwaggo ce ta faɗa min komai. Ban jidaɗin abunda ya faru ba Namra sai dai dawowarki ta min daɗi, saboda Uzair, ko da baki zo ni zan je har inda kike”
Gaban Namra ya faɗi ta mata wani kallo mai cike da mamaki.
“Uzair kuma, miya faru?”
Yasmin ta kama hannayen Namra ta riƙe.
“Ina son ki faɗa min tsakani da Allah, da gaske kin taɓa kama Uzair yana luwaɗi?”
“Dan Girman Allah Anty ki rufa in asiri na dawo yanzu cikin family na kuma saki sake tayar min da wannan maganar? Ko so kike Abbah ya sake kora ta ne?”
“Ko kaɗan, Namra kawai ina nema miki justice”
“Justice for what...?”
“For what Uzair did to you, shi ya ɗauke ki ranar da aka ce kin gudu kin je gurin Asim”
Idon Namra ya cika da ƙwalla.
“Waya faɗa miki?”
“Shi ya faɗa min da kansa, kuma yayi rape ɗinsa da kansa Namra, na rasa yadda zan yi abun yana ta ci na a rai, na kasa faɗawa kowa, amman na yi ma kai na alƙawari sai na shigar da ƙarar Uzair kotu da kai na, akan ki sai na nema miki haƙƙinki, saboda ɓacin suna da yayi miki kuma yasa duniya ta zargi kin gudu da saurayinki”
Kai Namra ta girgiza masa.
“Na yafe masa, dan Allah dan Annabi ki taimaka min ki bar wannan maganar”
“Kin tuna lokacin da Amira ta gudu? Shine sila saboda ke aka yi ma maganin sai ya koma kan Amira saboda ta ci amanar ki, Namra you deserve justice”
“Ke da kan ki zaki shiga kotu ki ƙalubalanci mijin ki?”
Cikin kuka Yasmin ta ce
“Yes Goyon bayan ki kawai na ke nema”
Namra ta yi saurin miƙewa tsaye fuskarta da hawaye.
“Zan yi tunani a kai, just go please”
Bata mata musu ba, ta share hawayenta ta mike tsaye ta fice. Tana fitowa falo ta karɓi Little Namra hannun Anty ta fice, ko sallama bata yi ma Anty ba. Anty na ganin hakan ta san ba lafiya dan haka ta tashi ta nufi ɗakinta inda Namra take.
ASIM POV.
Yana fita gidan Hajiya Sadiya, ya kira Matdiya ya faɗa mata ta faɗawa mamanta yau da dare zai zo ya gaishe ta. Haka kuwa aka yi, dare na yi yaje yayi wanka ya shirya cikin tufafi na alfarma, ya shiga motarsa da ya sa aka wanke masa, ya nufi wani boutique ya haɗu mata sabulai da mai da turaruka masu ɗan karen tsaɗa sai da ya kusa ciki bayan motarsa sannan ya shiga ɓangaren kayan ciye-ciye yayi leda uku, bayan ya biya ya kama hanyar gidansu.
Tass ya samu ƙofar gidan yau kam an share ba kamar kullum ba, zamansa yayi cikin mota ya kira ta a waya, ya shaida mata yana nan waje. Yau kan ta fi masa kyau fiye da kullum dan ta chaɓa ado da sari kamar wata amaryar india. Sama-sama suka gaisa yana mata wani kallo mai cike da alamar tambaya, ita kuma sai wani noƙe kai take ita ala dole tana jin kunya. Sannan ta yi masa iso, suka shiga cikin gidan tare. Ya raina gidansu sosai dan shi gani yake yanzu ya wuce irin wannan rayuwar. Bayan ya gama gaisawa da mahaifiyarta ya aje mata dubu hansi, sannan shiga ko wane ɗaki na gidan yana gaisawa da su sannan ya aje musu dubu goma. Su kan sai murna suke suna yabawa Mardiya kan ta yi miji, masu jin zafi suna ji, dan wasu har sun soma maganar ai yadda yayi ma Namra ita sakinta zai yi da ana kwana biyu.
Bayan sun fito yasa yara suka kashe kayan da ke bayan motarta suka shigar ma Mahaifiyar Mardiya da su cikin gida. Ita Mardiya ji tayi kamar ta ɗauke shi ta haɗe saboda ƙaunarsa dake ƙara mamaye mata zuciya, ko a mafarki bata zaci mutum mai kuɗi kamar Asim zai so ta ba, balle ma har ya ce zai aureta. Sun sha fira sosai sai kusan ƙarfe goma sha ɗayan dare sannan suka yi sallama.
A daren da farinciki suka kwana daga ita har Asim, har yana jin ba zai iya bari ta jima sosai ba. Sai dai abunda ya tsaya masa a rai miyasa bata nuna masa dangin ubanta ba? Ko lokacin da ya ce zai turo cewa ta yi bari ta faɗawa Uncle ɗinta.
“Idan ma bata da uba miye ruwana tun da ita nake so ba ubanta ba”
Ya faɗa yana fesa turare a jikinsa. Sannan ya ɗauki glass ya saka ya ɗauki makullin motarsa ya fice. Kai tsaye gidan ƙanen Babansa ya nufa, daman yasan a irin wannan lokacin yana gida kamin yaje gurin da yake aikin ƙira. Har ciki gidan ya shiga, sai qani ƙyaƙƙyami yake da ginin ƙasa, ya gaisa da