Showing 39001 words to 42000 words out of 281103 words
Chapter 14 - ZAGON KASA Book Complete Document by Khadeeja Candy .txt
biyu har da wani abu.
Bayan sun yi sallama ta samu Anty Amarya a ɗakinta ta faɗa mata yadda suka yi da Asim, akan ƙin amincewar da yayi na zama garin, sai ta nuna mata wai har ƙanen Babansa ya bashi gida a can, kuma sana'ar da yake acan mai ƙarfi ce wai a ƙarƙashin kamfanin Dangote ya samu suka ɗauke shi.
Bayan Allah ya kyauta babu abunda Anty Amarya tace mata, sai ta taso jiki ba ƙwari ta dawo ɗakinta, zuciyarta a cunkushe, tunaninta a kulle, ya rasa abunda yake mata daɗi har wani jiri take jin yana ɗaukarta.
_____________________________________
WHO CAN'T WAIT FOR THE NEXT CHAPTER?
COMMENT LINE BY LINE!
LOVE YOU ALL FISABILLIAH 💖💖💖
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/03/zagon-asa19.html
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
_Wattpad @_
*KHADEEJA CANDY*
Click www.khadeejacandy.com.ng for your updated
NOT EDITED ⚠️
*PAGE - 19*
Baki har kunne Asim ya isa gida da kuɗin, tun daga yanayin sallamarsa Mama ta gani yana cikin farinciki. A ƙuryar ɗaki ya same ta tana zaune saman sallaya ya zauna kusa da ita yana murmushi.
Wani kallo tayi masa ta ɗauke kai, dan ita yanzu wani haushi ma yake bata ji take kamar tayi ta dukansa. Takardar kuɗin dake aljihunsa ya ciro ya aje mata gaban sallaya tare da zinarin da Namra ta bashi.
Ba a ɓoye zinari yake ba, ko yanzu ka tashi daga bachi aka nuna maka shi zaka iya gane shi, musamman irin wannan na Namra da aka siya daga Dubai. Gabanta ya faɗi, sai ta kalli sarƙar ta kalleshi kusan sau huɗu sannan ta ce
“Ina ka samo wannan sarƙar Ibrahim?”
Da dariya ya amsa mata
“Nawa ne”
“Na ka? Sata ka fara ne? Kamar fa zinari nake gani”
“Ba kama bace zinari ne, wannan kuma takardar kuɗi ce na miliyan biyu da dubu ɗari uku”
Ta daki ƙirji ta da ƙarfi.
“Miliyan biyu Ibrahim? Ina ka samo wannan kuɗi?”
Yanayin yadda tayi masa tambayar da ƙarfi, yasa ƙanensa shigowa ɗakin da gudu suna tambayar miya faru.
“Kuɗi na samo mana miliyan biyu da dubu ɗari uku, ga kuma sarƙar zinari”
Ƙanensa ya zauna kusa da shi da mugun mamaki.
“Ya Asim taya ka ɗauko?”
“Ba ɗaukowa nayi ba, Namra ta bani tace nayi hidima da su”
Duk tsalle suka saka suna murnar Yayansu ya samo kuɗi, sai Mama tayi saurin riƙe so
“Dan Allah ku rufa mana asiri, kar aji a dirar mana cikin daren nan”
Sai da suka natsu sannan ta kalli Asim
“Da gaske ita ta baka Ibrahim?”
“Wallahi ita ta bani yanzu nan, sai da ma nayi kamar ba zan karɓa ba, sannan na karɓa kuma tace ba zata faɗawa kowa ba”
Hannu Mama ta ɗaga sama.
“Al-hamdulillah Allah mun gode maka”
Ƙanensa yayi dariya yana faɗin
“Mama ke da baki son ta”
“Ai suma ba dan Allah zasu aura masa ita ba, kai kana ganin masu kuɗi kamar Alhaji Usman zai yarda Ƴarsa tayi aure irin gidan nan idan ba da wani dalilin ba”
Asim ya sauke ajiyar zuciya kana yace
“Wallahi haka kowa ke faɗa, ni kwata-kwata ma ta fitar min a rai, kawai dai zan aure ta saboda na fita kunyar masu ganin kamar ɓa zata iya auren mutun iri na ba”
Mama ta mere baki
“Wallahi ko rantsuwa nayi ba zan yi kaffara ba, da abun nan be faru ba ba zasu taɓa yarda kmsu barta ta aure ka ba, Amman wannan shi ake cewa gobarar ti-ti ko ba komai dole dai a kira ka da surukin Alhaji Usman kuma ko yaƙi ko ya so dole ne ya samo maka wata hanyar, kuma Allah kaɗai yasan ribar da zaka ci akan wannan auren”
“Haka abokaina ke faɗa, wai wata hanyar ce Allah yayi min”
“Sosai tun dai baka ci amanarta ita ta nemi ta ci taka ai dole Allah ya saka maka”
“Yanzu wannan kuɗin tace min aje a haɗa lefe dasu kuma da su zan kama gidan hayan da zamu zauna a katsina”
“Amman Ibrahim zaman ka a nan be fi ba? Karatun ka fa?”
“Can ɗin zai fi Mama, kin ga zan samu sana'ah mai ƙwari, kuma ƴan'uwanta basa zasu sa mana ido a zamantakewar mu ba, idan muna da shi aci idan babu a haƙura, babu wanda yasan mun ci ko ba mu ci ba”
“Haka ne, sana'ah ma yafi, kuma nan kan sai sun sa maka ido har dai wata yarinya na nan marar mutunci kai yarinyar nan bata da kunya kaga yadda ta riga min fitsara sai da ta tara min jama'ah a gida kamar nayi sata! A nan ma saurin kashe auren zasu yi”
“Ai Maryam bata da mutunci ni kaina ina haƙe da ita Wallahi”
Ƙanwarsa ta risino.
“Amman Ya zaka gyara mana gidan nan ko?”
“Gyara gida ai dole ne yanzu kan, bari dai na ciro kuɗin kawai komai ma za'ayi da yardar Allah”
Duk tsalle suka hau yi. Mama na musu dariya zuciyarta ta cike da farinciki.
*** *** ***
Shi da kansa yasa ta faɗawa Abbah cewar ƴan'uwan babansa zasu zo su kawo sadaki da aka yanka tare da lefe.
Sai da Abbah ya sake sa musu rana sannan Anty Amarya ta faɗaata ita kuma ta faɗa masa.
Da daren ranar ne Aisha take faɗawa Anty Amarya irin maganganun da ake tayi a makarantar ta islamiya.
Namra na zaune parlour tana jinsu, har suka yi maganganunsu suka gama bata ce uffan ba, shiru kawai take tana saurarensu ƙwaƙwalwarta na juyawa.
“Amman gaskiya Anty Namra karki bar karatun ki, idan har ba zai iya bari ki ƙare makarantar ba kawai ya haƙura da auren ki, ai ba akanki aka fara cin amanar ba, kuma wallahi duk mai maka son gaskiya dole ne yaso cigaban ka, amman gani nake kamar cin amanarki kawai zai yi”
Maganar Hindatu ce ta ɗago da hankalin Namra har tasa ta kalleta, sai dai bata iya tace musu komai ba ban da ruwan hawaye daya fito daga idonta.
Maryam ta tsire baki
“Ke dai kika sani, tun da baki da ra'ayin kan ki sai na Miji, kuma wallahi kina daf da yin nadama dan duk mace da bata da ra'ayin kanta wahala tana tare da ita, ina tunanin wani abu ne ya ƙire kuma sauran kaɗan ya faɗa miki, ko kuma a ɗaga auren har sai kin ƙarasa karatun ki”
Hannu Namra tasa ta share hawayenta ta tashi jiki ba ƙwari ta nufi ɗakinta tana wata tafiya kamar marar lakka.
Sai a lokacin Anty Amarya ta kalli Maryam tace
“Kar na sake jin kun mata wata magana akan auren nan, kuyi mata fatar alheri kawai, wannan maganganun ba zai haifar mata da komai ba sai baƙinciki, idan kuna mata wannan maganar damuwa zata mata yawa.
Gani nake yi abun kamar zai taɓa ƙwaƙwalwarta, dan Allah karku sake mata magana nan, ita kan ta a yanzu bata iya banbance fari da baƙi, bata daɗe da fita lamarin Uzair yanzu kuma ta faɗo wannan, ko wane ɗan'adam baya wuce ƙaddararsa, no matter how you try baka iya tsallake ƙaddararka,
Kuma ba musan alherin da yake cikin wannan auren ba”
Maryam ta tsire baki.
“Wallahi babu wani alheri a ciki, daga gani ma amanarta zai ci shiyasa yake son yaje can nesa da ita, kuma ya hanata karatun ta tun da shi be san muhimmancin karatun ba”
“Babu alheri a ciki kin san gaibu ne? Idan ma amanarta zai ci ai ita ba yarinya ba ce, idan bata iya karatun duniya ba ai sai duniyar ta karantar da ita, ai kowa ya ƙona rumbunsa, ya san inda toka ke kuɗi”
Daga haka Anty Amarya ta tashi ta nufi ɗakin Namra, zaune ta tararda ita tana aikin kuka. Kusa da ita Anty Amarya ta zauna ta jata jikinta tana rarrashinta.
“Ki riƙa sauraren zuciyarki Namra, Allah yasa wannan auren ya zame miki alheri, kada Allah ya bar ki da kanki Allah ya dafa miki lamarin ki”
Rumgume Anty Amarya Namra tayi sosai tana wani irin kuka mai taɓa zuciya. Anty Amarya bata san lokacin da nata hawayen suka zubo ba.
*** *** ***
Ranar Assabar suka kawo lefen, tarba ta musamman akayi musu, tun daga kan drinks har zuwa abubuwan ciye-ciye, Hajiya Barau ta soya musu kaji da wasu abubuwan. Sai dai wannan karon ba'a tara mutane kamar wacan ba, iya su ƴan gida ne kawai suka tarbi lefen.
Su basu ga wani abun a'zo a gani ba, a lefen tun da abun masu hannu da shuni idan ba an saka tufafin dubu ɗari, ɗari biyu ba su ba ƙimarsa suke gani ba. Sai dai Anty Amarya bata bari sun yi magana a gaban idonta ba, sai dai idan bata nan, a fuska kuma sai tasa suka nuna mata ai yayi ƙoƙari. Ita kanta tasan yaba mata ne kawai suke dan su ƙarfafa mata gwuiwa, amman ba dan sun ga darajar kayan ba.
Tun daga ranar da aka kawo mata lefen Namra tayi sallama da abinci, duk yadda aka tursasata sai tacw bata iya ci, sam bata ma jin sha'awar abincin balle ta ci. Iyakarta abu mai ruwa, ko kuma tea, gashi ta yi baƙi sosai kamar ba farar mace ba, ta rame kamar marar lafiya.
Ita kaɗai tasan abunda yake cin ta a zuciya, tana jin son Asim, wani ɓangaren kuma tana jin kamar ta fasa auren amman babu dama, ta kasa samawa kanta mafita. Haka take wuni a ɗaki kamar wata marainiya, duk wata hidima da ake na zuwa siyen kayan aurenta ba da ita ake yinsa ba.
Da dare Maryam ta samu Namra ɗakinta tana nuna mata pictures ɗin gadaje wato furniture ɗin da za a zuba mata.
“Kin ga wannan miliyan ɗaya da rabi, wannan kuma miliyan ɗaya da ɗari bakwai Abbah yace ki zaɓi wanda kike so”
Kasa zaɓa tayi, ita sam zuciyarta bata mata daɗi.
“Kawai ki zaɓa min wanda duk kika ga yayi miki”
“Amman Anty zaki yi event ko?”
“ Babu abunda zan yi Maryam wanda ya wuce walima”
Kallonta Maryam tayi kamar tace wani abu sai kuma wani tunanin ya zo mata, sai kawai tayi shiru ta shiga nuna mata kujeru.
Sai da suka kai ƙarshe sannan Namra ta riƙa hannunta cikin rashin kuzari tace
“Maryam dan Allah kar ku yi fushi da ni dan na aure Asim, ku yi miki kyakkyawar fahimta dan Allah”
“Babu wanda yake fushi dake, kuma kin yi ma Asim halacci iya halacci Allah yasa kar ya zamo butulu, ya riƙe ki Amana”
“Amin na gode”
Daga haka Maryam ta tashi ta bar mata ɗakin. Ita kuma ta gincira tana sauke ajiyar zuciya.
KALSOOM POV.
Yanzu kam ƙofar farinciki ta buɗe mata dai-dai gwargwado bata da wata matsala a gidan mijinta.
Tun da safe zata tashi ta haɗa yara breakfast, tayi musu shirin makaranta, sannan ta tashi Doc. Sai dai yanzu kusan wata ɗaya kenan, Rashida babu ruwanta da Kalsoom duk kuwa da kasancewar yaranta ne take yima hidima, da ranar girkinta da ba girkin ta ba duk Kalsoom ce take girki, sai dai da dare ne zaka banbance ba ita ke da girki ba, kasancewar kwana biyu-biyu yake musu.
Doc. Hilal kam ji yake kamar ya ɗauki Kalsoom ya haɗeye, saboda yadda take masa komai daki-daki a gidansa, yana jindaɗin yadda take tashi tun da asuba tayi aiki, daman maza basa son raguwar mace. Gashi tana nunawa yaransa so hakan ba ƙaramin daɗi yake masa ba. Sai dai a ɗayan ɓangaren yadda Rashida taƙi ta sake Kalsoom abun na sosa masa rai, dan duk wahalar da zatayi da yaran Rashida ba zata iya ce nata sannu ba, balle na gode, ko kuma ta nuna mata jindaɗinta a kansu.
Yau ma kamar kullum bayan ta gama sallamar yara, sun karya sai ta raka shi bathroom suka yi wanka tare.
Ita ta shafa mishi mai ta murza masa turare, jaka yazo ya zauna ta saka mishi tufafi ko kunya. Har ta ɗora masa hula akai bakinta yake kallon.
“Perfect everything clear”
Ta faɗa tana ƙara gyara masa girarsa. Bakinsa ya miƙa mata.
“Na siye wannan lips ɗin”
“Yau ba za'a sai da maka ba”
Lumshe mata ido yayi, ya langaɓar da kai
“Haba Ma'am... Pity me”
Sai taja kumatunsa.
“No Toy”
Miƙewa tayi tsaye. Ganin da gaske ba zata masa kiss ɗin ba yasa yayi hanzarin fisgota ya jefar saman gado.
“Idan ban samu kiss ba toh zan nemi abunda ya fi kiss ɗin”
Hannu ta ɗaga masa
“Tsaya Wallahi zan baka, amman kiss kawai”
“Naji kiss kawai aya tashi”
Ya faɗa yana nuna mata bakinshi. Kamin ta miƙe tsaye ya buɗe durowa ya ɗauki sweet candy yasa bakinsa. Riƙe ta yayi gam kamar wanda zata tsire masa sai da ta tsosar masa bakin da kyau da kyau sannan ya sake ta bayan ya mayar mata da sweet ɗin cikin bakinta.
Sai ya zaunar da ita.
“It my turn”
Mai ya ɗauka ya fara shafa mata, sannan ya shafa mata hoda, sai janbaki. Sannan ya ɗauki underwears ya saka mata, ya ɗora mata da gown, haka ya mundula mata ɗankwali saman kai sai dariya yake.
Bayan sun gama, ta rako shi har gurin mota, sai da yayi mata side hug sannan ya shiga motar tana masa addu'ah.
“Allah ya haɗa ka da halak komai ƙanƙantar ta, ya nisanta ka da haram komai yawanta”
“Amin I Love You Dude”
“I love you more”
Bayan ya wuce ta dawo falon ta ƙarasa gyarasa. Guraren goma da rabi Rafiq ya tashi, sai tayi masa wanka ta bashi abincin sannan ta ɗauko shi suka dawo falon suka zauna.
Ƙonƙosa ƙofar data ji anyi ne ya ɗago da ita ɗaga kallon MBC2 da take.
“Waye?”
Daga inda take zaune ta tambaya.
“Nice Amarya”
Jin muryar Asmee yasa ta tashi ta buɗe mata ƙofar fuskarta a sake.
“Amarya gida sai ƙamshi yake”
Ta faɗa bayan ta zauna. Kalsoom tayi dariya
“Daman gidan mace a gidan ƙamshi ne, ya aikin ya kwana biyu?”
“Lafiya ƙalau, kina nan kina fama da rainon yara ko?”
Murmushi Kalsoom tayi.
“Asmee ke nan, ai yara na kowa ne, kuma ƴaƴan Hilal ai ƴaƴana”
Asmee ta wani gyara zama tana tsire baki.
“Ke ni dan Allah raba ni da abun haushi, ke kika zama ni nake miki kishi”
“Asmee kenan nikan na so naga kishiyarki”
Kalsoom ta faɗa tana dariya. Da sauri Asmee ta matsa
“A'a Wallahi mugun abin ki ya biki, ke daman Allah be raba bakin ki da tsaɓo ba, bari ma na bar miki gidan daman wani haki ne na siya nace bari na sam miki”
Ta faɗa tana fiddo wani baƙin abu a ƴar ƙaramar roba.
“Kin ganshi ɗan matse ne mai kyau Wallahi, sai kin ban labari, nasan ai kayan amarcin ki sun ƙare yanzu ai”
“Wallahi sun ƙare, duk na kyautar da su ni ba son irin abubuwan nan nake ba, nafi son masu zaƙi ko kuma ƴan fruits haka, kin san suma suna gyara jiki”
“Amman gaskiya kiyi amfani da wannan dan Wallahi yana da kyau sosai”
“To na gode zan gwada”
Bata daɗe ba ta tashi ta fita, har gurin gate Kalsoom ta rakata, sannan ta dawo gida.
Tun kamin Asmee ta isa gida ta buga Rashida tana labarta mata cewar saƙonta ya samu isa yadda ake so. Daga ɗayan ɓangare Rashida tayi murmushi tayi mata godiya sannan suka yi sallama.
Tana aje wayar ta tsire baki. Mutumen dake zaune saman wata huge chair ya kalle a ƙasaice yace
“Wacece?”
“Matar ka ce”
Yayi saurin ɗagowa
“Miya kai ta gidan ki? Bayan baki nan?”
“Ai abokiyar zama na nan, gurinta taje”
Ɗan murmushi yayi
“Mata Allah be raba ku da kicihiba”
Dariya tayi ta ɗauki documents ɗin da suke saman teburinsa, ta nufi ƙofa.
“Ki kai min waɗancan documents ɗin a guesthouse”
Ya faɗa yana kallon mazaunanta dake cikin suit.
“Gaskiya yau ba zan samu shiga ba da wuri zan koma gida”
Daf da zata fice ta amsa masa, sannan ta fice.
___________________________________________
Assalamu alaikum Habibaties💖. To all those that are asking about Amira and Uzair labarinsu zai zo nan gaba, so please wait patiently. And masu cewa kaza ya kamata ayi ba kaza ba, blah blah blah, yen yen yen, this and that, na gode duka amman please ku bar tafiyar nan ta tafi a yadda na tsara ta. Ba ku san dalilin da yasa Yasmeen ta fito a Barrister ba, ba ku san miyasa asiri ya koma kam Amira ba instead of Uzair, so please judge less.
Na gode Sosai Jazakallahu Khairan 🌺
I Love You All Fisabilliah 😘
https://www.khadeejacandy.com.ng/2019/03/zagon-asa20.html
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
NOT EDITED ⚠️
*PAGE - 20*
Ba'ayi wasu events ba, bayan salalle da wanki a Amarya, sai Walima da akayi ranar Jumma'ah. Bikin yayi mutane sosai musamman ta ɓangaren Anty, kasancewar Anty Amarya yanzu ne ta fara aurarwa. Har Ƴaƴan Hajiya Barau da suke nesa sai da suka zo.
Kaɗan daga cikin ƙawayen Namra ne suka samu halartar walimar, kasancewar bata yi gayyatar mutane ba, wasu ma ta hanyar Maryam suka ji.
A babban masallacin Jumma'ah akayi ɗauren aurenta, manyan mutane da dama sun tafi ta dalilin Abbah.
Yadda Asim.yake far'ah da nuna jindaɗinsa kamar ya zuba ruwa ƙasa ya sha. Takeaway na Manyan mutane Abbah yasa aka shirya masa ya rabawa abokansa. Asim kan shimkafa da miya yasa aka shirya masa a gidan wani abokinsa, sai ya tare da Abokansa a can bayana ɗaurin auren sukayi liyafar cin abinci.
Namra na zaune ɗakinta tare da wasu cousins ɗinta, Maryam ta shigo da guɗa.
“Ayyyyyyy Yau an ɗaura auren Namra da Asim”
Wani irin faɗuwa gaban Namra yayi, a maimakon tayi murna sai kawai idonta ya cika da ƙwallah. A take ta soma ganin kamar mafarki take. Farinciki da baƙinciki sai suka taru suka mata tsaye a guri ɗaya.
Yadda ƴan'uwan nata suka riƙa zolayarta yasa ta fito da kukan nata a fili, su kuma suka cigaba da zolayarta. Daker wata Gwaggonta ta lallaɓata ta tashi, tayi wanka lalle ta shirya cikin jar