Showing 78001 words to 81000 words out of 281103 words
Chapter 27 - ZAGON KASA Book Complete Document by Khadeeja Candy .txt
ta kama ruwa.
RASHIDA POV.
Data isa tasha, shatar motar ta ɗauka ita kaɗai, ya kai ta ƙauyen. Bata sha wahala ba gurin gane gidan, tambaya ɗaya suka yi aka nuna musu gurin, gidan ne mai kyau kamar ba ƙauye ba. Sun tarar da layin mata sosai a gurin haka ta samu guri ta tsaya har aka kai gareta. Sannan ta shiga.
Ƙaton ɗaki ne mai cike da kayan alatu, ba dan rawanin da taga ni a kansa ba, da zata iya rantsuwa da Allah tace wani attajiri ne ba malami ba, sai dai hakan be bata mamaki ba, dan tasan duk mutumen dake aiki da manyan yan siyasa dole ne ya tara komai.
Kallo ɗaya yayi mata ya soma gyara ƙasar dake gabansa yana faɗin ta cire niƙabin ta, ba musu ta cire niƙab ɗin tana gaishe shi. Be amsa ba har sai da ya gama bugun ƙasar sa, sannan ya kalleta yace.
“Kin zo nan ne dan a haɗa ki da wani yayi miki wani aiki”
“Haka ne ni ƙawar Asmee ce, tace zata kira ka”
Sai da ta ciro dubu hansin ta aje masa a gabansa, sannan ta koro masa da bayani. Sai da ta gama sai yayi murmushi yace
“Zan haɗa ki da wani, saboda kawai Asma'u ce ta turo ki, amman ba dan haka ba, babu abunda zai sa na haɗa ki da shi, saboda shegen mutum ne, ni kaɗai zan iya sashi abu yayi nan take”
“Na gode Malam, idan har aiki yayi kyau, kai ma zaka jidaɗi inshallah”
Wayarsa ya ɗauka ya kira, yayi tsowon minti ashiri yana lalasar mutumen sannan yaba Rashida waya suka yi magana ya faɗa mata inda zata same shi.
Bayan sun gama malamin ya kalleta yace
“Idan buƙatata da biya ki dawo ina son ganin ki, dan gaskiya akwai matsala a tare da ke, kuma akwai abunda yake shirin faruwa da ke, dole ne sai kin nemi taimako”
“Inshallah, zan dawo”
Da tsoro tayi masa sallama, tana ta tunanin wane irin matsala ne, zuciyarta nata raya mata lallai wannan malamin yana aiki kam.
Tafiyar mintuna arba'in suka yi, suka dawo cikin gari, kai tsaye tace direban ya nufi American Unique Estates da ita, a dai-dai inda ya kwatanta mata ta tsaya, ta kira number da Malamin ya bata ta mutumen tace masa tana gurin, sannan ta sallami direba fiye da yadda suka yi jingar.
Tsaye kawai take a gurin amman babu natsuwa a tare da ita, ji take kamar wani zai zo ya ganta. Bayan kamar mintuna asirin da biyar wata ƙafirar mota ta faka gabanta.
Wani Namiji ne mai shigar mutunci ya fito cikin motar tare da Amira.
“Ke ce Rashida wacca Malam ya aiko?”
Namijin ya tambaya.
“Eh nice”
Amira ta buɗe mata Motar.
“Shiga muje”
Da tsoro ta shiga motar, zuciyarta duk bata natsu da su ba.
___________________________________________
Assalamu alaikum as i said yau na kai Page 35, that's means na gama free pages kenan. Dan haka duk mai son ƙarashin wannan labari zai iya turo ₦200 zuwa wannan account 0314795884 Abubakar Hadiza GT Bank.
Sai ku turo da shaidar biyan kudin wato screenshot ta wannan number 08036126660.
Zan saka ku group inda zan riƙa updated littafi kullum inshallah.
Na yi haka ne duba da yadda wasu suke ci da gumi na, akwai wanda ya ƙirƙiri grp a whatsapp ana tura masa naira ɗari yana tura littafan marubutan online cikin har da nawa, sannan akwai wanda ya ɗauki littafina na MAIRO ya maida shi application ya ɗora a Google play store, wanda duk yayi downloading ɗin app ɗin sai google sau biya shi, idan kuma suka ɗora talla a app ɗin kuma wannan shima sai sun biya shi, ni da nayi rubutun ban ci ba shi ya ci. Bayan haka an ɗauki littafina na SALEENA an saka a okadabooks, ba tare da izini na ba, wanda idan aka siye kuɗin zasu je ga wanda ya saka littafin ne ba gare ba, idan kukayi searching duk zaku ga abunda nake faɗa muku na Application da okadabooks.
Dan haka ya sa na canja wannan littafin uzuwa na kuɗi, dan nima na ci amfanin abuna, da wani ya ci da gumminka ƙara ka san kai ka ci, ko yayane, dan baka san ta rai ba. 😀
Ina roƙon duk wanda na ɓatawa rai sanadin canjin nan ko kuma littafin nan, dan Allah ku yafe min, nima ban za ci sauyin zai zo ba, sai daga baya, da tun farko na faɗa. Ina roƙon alfarma dan Allah kar wanda ya mai da min da Littafi document.
Na gode da shawarwari da ƙauna, Allah ya sakawa kowa da Alheri. I love you all
BEST REGARDS 💖🌺
KHADEEJA CANDY 😘
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
_Write by_
*Khadeeja Candy*
*PAGE - 36*
NOT EDITED ⚠
Nitsa kai suka yi tayi cikin unguwar, sun yi tafiyar mintina goma zuwa sha uku, sannan suka isa ƙarshen unguwar, a bakin wani makeken gate black color.
Tsoron dake cikin zuciyar Rashida ya kasa ɓoyuwa har sai da ya nuna a jikinta, gani take kamar wani abun zasu mata har ta buɗe baki tayi magana, sai ta tuna da abunda ya kawo ta gurin, kuma ta san bata da wata mafita sai wannan.
Sai kawai tayi shiru da bakinta ta sakar musu na mujiya har suka faka bakin wata babbar ƙofa. Amira ce ta fara fita tana faɗin
“Fito muje”
Buɗewa Rashida tayi ta fito, sai mutun ya ja motar ya nufi wani ɓangare na gidan da ita.
Amira tayi gaba, Rashida ta rufa mata baya sai kalle-kallen gidan take.
Cikin wani ƙaton falo suka shiga, wanda aka ƙawata da kayan alatu, kallon falon tayi sosai ba dan ya birge ta ba, sai dan ɗaukar rahoto ta karanci wane irin gida ne aka a kawo ta.
Kamar daga sama ta ji Amira na mata magana.
“Idan baki yarda da gidan ba, miyasa kika shigo? Ko kina tunanin za mu miki wanin abun ne?”
Kasa cewa komai, tayi har Amira ta gaji da tsayi a gurin, ta isa gaban wata babbar kujera ta zauna tana cire gyalen abayarta.
“Guy Son!”
Ta ƙwala mishi kira, tana nuna ma Rashida kujera.
“Zauna idan zaki iya”
Rashida ta zauna zuciyarta na ɗar-ɗar, wani tunanin ne ya zo mata. What if tafa mutumen data sani? Ko kuma gidan yana tare da Dr Sabo fa?
Fitowarsa yayi dai-dai da sauke ajiyar zuciyar da Rashida ta yi, a yanayin shigarsa da kamalarsa, bata zace shine Guy Son ɗin ba har sai da ya zauna kusa da Amira, jikinsa yana Gugar na Amira.
“Wa kike son ayi miki garkuwa?”
Ya tambaya, fuska babu alamar murmushi balle wasa.
“Wani mutun ne, sunan shi Doc Sabo a asibin Alex yake aiki sashen jini”
“Cire Niƙab ɗin fuskarki kiyi mana bayanin komai”
Tasa hannu ta cire Niƙabin ta gyara zamanta sannan tace
“Mijina ne ya ɗibi jinina dana yara na ya kai masa akan yayi mana gwaji, bana da tabbaci amman ina jin kamar ina ɗauke da cutar hiv kuma ina tunanin mijina da kishiyata basa da shi, na karɓi numbersa gurin abokin aikina na kira mun yi magana akan zai faɗa min idan mijina ya kawo jinin, har na tura masa dubu ɗari, sai gashi ya yaudare ya faɗawa mijina na bashi kuɗi”
Ya kai hannunshi ya riƙa hannun Amira yasa yatsunsa cikin nata.
“So kina son ayi forcing ɗinsa ya canja result ɗin ko?”
“Haka nake so, matuƙar ya faɗi gaskiya, mijina zai rabu da ni, kuma duniya zata ƙyamace ni, zan ba ku ko nawa kake so, dan Allah ku taimaki rayuwata”
Amira ta ɗan yi murmushi.
“Ba shi kike son ayi a ɗauke miki ba, ƴaƴansa za'ayi kidnapped sai asa shi dole ya faɗi abunda kike so”
“Koma yaya ne ni dai yi min zan biya ko nawa kuke so”
Ta faɗa tana karyar da murya irin tausayin nan. Wayar dake hannu ya karɓa, ya saka wata number ya kira, ana picking yace
“Zo nan ina neman ka”
Be fi mintuna uku da aje wayar ba, sai ga mutumen ya shigo cikin ƙaƙanan tufafi, yazo dai-dai shi ya tsaya, Rashida na kallonsa gabanta ya faɗi saboda jan idonsa.
“Ka bincika min addireshin Doc Sabo yana aiki a Alex hospital sashen jini”
“Okay Boss”
Sai ya juya ya fice. Guy son ya kalli Rashida ya ce
“Bani addireshin ki, kuma karki kuskura ba ni na ƙarya dan zan gano ki”
Gabanta ya faɗi sosai, kuma ta tsorata, bata son bashi na ƙarya tun da har ya gargaɗeta, sai dai kuma idan har ta ba shi adireshin na gaskiya, bata san abunda zai faru ba.
“Sunana Rashida Abdullahi Kardam ina aiki a Stanbic Ibtc Bank, mijina babban likita ne, yana aiki a Kaduna special hospital, muna nan GRA magaji road”
“You can go, zaki ga motar data kawo ki zata maida ke inda kike”
“Thank you”
Ta saka niƙabinta ta saka sannan ta ɗauki jakarta ta fice. Amira ta tashi ta nufi gurin window falon ta tsaya, tana kallon harabar gidan. Tana sinkayar motar har suka fice, sannan ta sauke ajiyar zuciya, ta jingina da gurin ta rufe ido.
Hannunshi yasa cikin jikinta yana murza fatar jikinta, ya fara shinshinar gefen wuyanta. Buɗe idon ta yi ta ture shi da dukan ƙarfinta.
Kallon da zai yi sai hawaye ya gani sun silalo daga idonta. Yarfarda hannu yayi ya cije fuska.
“So nawa zan faɗa miki bana son hawayen nan”
“Ka bar ni nayi kuka na, ai ina da dalilin kuka”
Hannu ya kai ya riƙe fuskarta iya ƙarfinsa ya matse ta.
“Ba dalili bane, idan har kina son iyayen ki dole ne ki koma gare su, amman kin kasa kuma kin ƙi ki faɗa min gaskiya, saboda kin san mugun abun da kika aikata”
Yana kaiwa nan ya wurgar mata da fuska gefe, ya wuce ciki. Da kallo kawai ta bishi idonta na hawaye, wani irin zafi zuciyarta ke mata, ita kaɗai tasan irin abunda take ji.
Bata ganin laifin kowa sai Uzair da Namra, dan sune suka rusa mafarkinta, suka gurɓata duniyarta, suka canja tunaninta, sun salwantar da farincikinta, sune sanadin barin gidan iyayenta, sune suka sa duniya ta zage ta, sun yi nasarar sauyata daga mutum zuwa mutum mutumen da kowa ke kallonta.
Lallai bata da maƙiya kamar su, bata da wani buri illa na ganin bayan su. Har yanzu zuciyarta bata lurar da ita illar abunda ta aikatawa Namra ba, bata ganin asirin ne ya koma mata, gani take kamar da haɗin bakin Namra Uzair ya cuce ta.
Tana son komawa gida amman hakan sai ya gagareta, idan ta tuna yadda ta bar kowa nata, ta watsar da karatun ta, ta dawo nan ta zauna, sai taji kamar ta haɗiye zuciya ta mutu.
Rayuwarta ta zame mata kamar mafarki, yadda sauyin yazo mata, sai yayi mata kamar a shirin fim ko littafi, silar su ne take a cikin halin da take ciki. A yanzu kan bata da mafarki sai na Namra da Uzair bata da buri sai na su.
Ƙarar buɗe ƙofar gidansu da tayi ta fita ne ya dawo mata sabo, yadda ta kai kanta har tasa ta bar garin sokoto ne ya riƙa mata yawo a ƙwaƙwalwa.
Durƙushewa tayi a gurin ta fashe da wani irin mahaukacin kuka, tana yagar fuskarta. Da sauri Guy son ya fito daga ɗakin daya shiga yazo ya rumgume ta yana rarrashinta.
“Shiiiiiiiiiii, I'm sorry Amira, I'm so sorry”
Ya ɗora kansa saman na ta yana girgizata, alamar lallashi, har cikin kansa yake jin kukanta, son ta na masa yawa a ko ina na gaɓoɓinsa.
RASHIDA POV.
A inda suka ɗauke ta ɗazu, mutumen ya sauke ta, sai ta tari Napep ya kai ta unguwar da iyayenta suke. A nesa da gurin tasa ya sauke ta ta sallame shi, sannan ta taka da ƙafa ta ƙarasa cikin gidan.
Sai da ta buɗe motarta ta saka jakarta sannan ta, ta shiga cikin gidan, bakinta ƙumshe da sallama. Da far'ah Momy ta amsa mata.
“Ma'aikatan kuɗi yau a gidan na mu?”
“Wallahi kuwa, yau kin san babu aiki”
“Yau kuma har da hijabi! Aiko kin ga yadda ya fitar da ke, mashallah”
Zaunawa tayi tana murmushi.
“Momy kenan, shi saka Hijabi har wani abun ne?”
“Wani abun ne mana, shiyasa abokiyar zaman ki take burgeni saboda ta san kanta sosai, duk inda zaka ganta da hijabi zaka ganta, kin ga irin wannan matar? Da wahala wani namiji yayi mata maganar banza, Hijabi ne abu ne mai muhimmanci Rashida tun da har ki ga musulunci ya koyar da mu saka shi ai kinsan yana da kyau”
Ta ɗanyi murmushi, wanda be kai ciki ba murmushin rashin jindaɗin maganar da Momy tayi na Kalsoom.
“Nikan bana burge ki ko Momy?”
“Ba haka nake nufi ba, yadda ɗabi'unta da halayenta yake haka na so naki ya kasance, amman sai ki ari wata rayuwar ta daban kika ratayawa kanki, kika ɗauki wani hali wanda ban san inda kika samo shi ba kika laƙabawa kan ki”
“Uhmm Momy ban yi breakfast, yunwa nake ji sosai”
Ta faɗa da nufin kawar da wacan maganar ta Momy, shiyasa bata cikin son zuwa gidan ba, duk lokacin da tazo sai ance tayi wani abu ba dai-dai ba, yanzu ma abun ya wuce guri har abokiyar zamanta Momy take yabo, ita kam bata taɓa ganin uwar dake yabon kishiyar ɗiyarta ba sai nata uwar.
6ana ɗaya daga cikin dalilin dayasa Kalsoom ta zame mata ƙashin wuya, amman wannan matsalar da take ciki yasa ta ma manta da ita sai yanzu da Momy take tsokaro mata tsatsar ƙiyayyar da tayi mata katutu a zuciya.
A gidan da wuni, duk irin tambayar da Momy tayi mata na barin motar ta da tayi taje wani gurin, ƙin faɗar inda taje tayi, balle ma har ta faɗawa Momy dalilin zuwan nata.
Tasan bayan sallah magariba Hilal baya gida, dan a masallaci yake sallah magariba kuma baya shigowa gida sai anyi isha'i, hakan yasa ta dawo gida a lokacin, dan bata son ta dawo lokacin da yake nan.
Ta jidaɗin rashin ganin ɗaya daga cikin motocinsa hakan ya tabbatar mata da baya ma unguwar kenan, sai da ta cire hijabin ta bar a mota sannan ta fito, ta nufi hanyar falo.
Ɗora ƙafarta da zatayi sai gabanta ya faɗi, maido ƙafar tayi tayi baya-baya tana sauraren bugun zuciyarta.
Ta kusan minti biyar a haka, sannan ta kai hannu ta tura ƙofar ta shiga, bata ga alamun motsin kowa a gidan ba, hakan ya tabbatar mata da dukansu basa nan. Sai da ta leƙa ɗakin yaranta, taga babu kowa sannan ta nufi ɗakinta.
Jakarta ta fara ajewa tana sauke gajiya, sannan ta cire tufafin jikinta, ta shiga banɗaki tayi wanka, ta fito.
Dressing mirror ta nufa, ta shafa mai da turare sannan ta zauna tana nazarin duniyarta, idan har ta aikata abunda take da niya, to asirinta ya rufu, sai ɗayan kuma tana tunanin makomarta, akan abunda take ƙoƙarin aikatawa. Wani dogon numfashi taja ta sauke. Sam bata lura da takardun dake saman gadonta ba har sai da ta unƙura zata tashi.
Gabanta ya faɗi, a iya tunaninta bata san ta bar komai a saman gadonta da zata fita ba, sannan yanayin takardar be yi kama da documment ko file ba. Matsawa tayi kusa da gando ta kai hannu cikinn rawar jiki ta ɗauki takardaun.
Tana fara karantawa ta ji kamar an mata shocking, wani abu yazo mata tsam tun daga saman kanta har zuwa cikin ƙafafunta, bata ankaro da duniyar da take ciki ba, har sai da jini ya fara bin ƙafafunta.
NAMRA POV.
Sai da yamma sosai ƴan gidan suka dawo, abun walima ɗaya Inna ta bawa Mardiya tace su raba ita da Namra. A tare suka ci, lemun da yake ciki Namra tacw ba zata sha, ta bar ma Mardiya.
Bayan sallah magariba, ɗaya daga cikin matan gidan ta kawo ma, Namra tuwon masara da miyar ganye, haka Namra tayi ta tura abincin ba dan tana so ba, abun ka da wanda be saba ba.
Kaɗan kawai ta ci ta bar ma ƙannen Mardiya saura, ta wanke hannunta, sai ta koma kusa da Maman Mardiya ta zauna tana labarta mata zasu koma BQ, Inna tayi mata murna sosai, har tana cewa zata ƙara mata da wani abun.
A daren sun sha hira, ita da Inna sai labarin rayuwa take bata, irin gwargwarmayar da ta sha kamin ta kawo yanzu, da kuma labarin ƙurciyarsu ta ƙauye, wani abun na dariya wani na ban haushi, wani kuma na ɗaukar darasi.
Sai kusan goman dare Namra ta kwanta, har kuma lokacin Mardiya bata gidan, kuma sam hankalin Inna be tashi ba, bata ma nuna damuwarta akan rashin sanin inda Ƴarta take ba. Sai kusan shabiyun dare ta dawo gidan, tana ta wani ƙunshen-ƙunshe, suna sun-sun ita da Inna a tunaninsu Namra tayi bachi.
Sai kawai ta warware Mardiya da ta zo da shi. Har suka ci suka cinye Namra bata motsa ba balle ta nuna musu idonta ba, sun tana bachin ƙarya har na gasken yayi gaba da ita.
*WASHE GARI*
Inna ta bada aka siyo musu koko da ƙosai, sai ta siyo ma Namra waina, dan ta lura sam bata son koko, tun farkon kwananta gidan. Sai da ta ci ta ƙoshi, sannan ta nufi akwatin Mardiya dan ɗauko kuɗinta, da zimmar ta siya ma Asim abinci ta kai musu.
Bata ga jakar a inda ta aje ta ba, sai ta sa hannunta tana ta lalabawa, wayan bata ji komai ba, wale akwatin tayi tana duba sama-sama ko zata ganta, amman bata ganta ba.
Zata canye hannunta kenan sai taji abu ya zargi hannunta kamar an soke ta da allura, da sauri ta janye hannun tana raki.
“Waisss Ina jakar nan ta shiga ne”
Sai ta soma ɗaga tufafin ɗaya bayan ɗaya, tana dubata, ganin tayi kamar be dace ta ya mutsa mata kaya ba, saboda neman jaka wata ƙila ma ta ɓoye mata a wani gurin, ƙara kawai ta tambaye ta.
Har zata mai da kayan sai abu ya faɗo daga cikin ɗankwalin atamfar Mardiya, dubawar da