Showing 174001 words to 177000 words out of 281103 words

Chapter 59 - ZAGON KASA Book Complete Document by Khadeeja Candy .txt

28 Dec 2024

61301

ɗauka ya ɗauki kansa hoto, sannan ya baro gaban madubin baya ya feshe jikinsa da turare mai mugun tsada da ƙamshi.
Already ya saka agogo hannunsa da zabban azurfa.

Yana doso sitting room mafarkinsa ya faɗo masa a rai. Wani irin faɗuwa gabansa ya yi har sai da ya rumtse ido ya murƙushe bakinsa.


“Wai miyasa yarinyar ta tsaya min arai ne? Ko dai akwai wani abun ne? Yeah na ga kare yana binta, ta faɗa rame? Me wannan yake nufi ne?”


“Allah ya taimaki Yarima, ba mu da masaniya akan abunda kake magana a kai, Allah yaja kwanan ka”


Kallon mamaki yayi musu yana juyar da kai, dan shi be san ya iso sitting room ba ma sai yanzu, ashe a fili yake maganar.
Iskar bakinsa ya furzar ya kalli tsadadden agogon hannunsa. Ƙarfe biyu saura minti goma ya gani, ya san ɗaurin auren ƙarfe biyu ne.


“Allah ya taimaki Yarima, tuni Mai martaba, ya kira kana bachi har ya bada umarnin tashin ka”


Hannayensa ya zuba cikin aljihu.


“Yanzu dole sai an naɗa min rawani?”


“Allah ya taimaki Yarima, haka Mai Martaba ya ce, har alkibar da zaka saka mun zo da ita”
Haka ya zauna suka naɗa masa rawani akai, ya fito fes Sarki, ba ma ɗan Sarki ba.
Miƙewa yayi tsaye suka saka masa baƙar alkyabar mai ratsin zaiba, sannan suka fiddo takalmin alkyabar suka aje masa ƙasa. A ƙoƙarinsa na saka takalmin ya kalli Sadauki ya ce.


“Idan ka yi mafarki kare yana bin ka me hakan yake nufi?”


“Allah ya taimaki Yarima, Maƙiyi ne.”


Ya ɗan yi shiru na wasu mintuna, kamin ya sake furta.


“Idan kuma ka faɗa a rame fa? Sai kuma ka miƙo min hannu kana son kamo ni?”


“Wannan Makaru ne, Allah yaja kwanan ka, idan kuma ina miƙa masa hannu to ina neman taimakon ka ne”


Sai da Sadauki ya gama amsa masa duka tambayoyinsa sannan ya saka takarmin, zai soma tafiya Sadauki ya ciro wani turare zai fasa masa.


“Allah yaja kwanan ka Mai Martaba ya ce afesa maka wannan”


“Na saka turare bana da buƙata”


“Allah ya taimaki Yarima, wannan na gidan sarautar ne, na Masarautar Katsina ne, ƙamshinsa ne zai sanar da isowar ka, kuma wannan turaren na gidane da ake haɗawa tun gadon gadon”


Ba dan yana so ba, ya tsaya suka fesa masa turaren sannan suka shiga gaba, wasu kuma a baya, shi kuma sai wata tafiya yake kaɗan-kaɗan, mai cike da tsantsar kasaita, da nuna isa, bayan kuma shi hankalinsa yana can wani gurin dabam.


[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *66 NOT EDITED ⚠️*




AMIRA POV.


Ta san yau zai dawo, amma hakan be hana ta kiwarsa ba, duk sai taji gidan ya mata girma kamar ita kaɗai ce a ciki. Tana son aika masa da saƙon tana tuna gargaɗin da yayi mata akan ta daina.
Bata san hawaye sun zubo mata ba, har sai da ta ji ɗuminsu a kumatunta, ɗan murmushi ta yi ta kai hannu ta share hawayen tana magana da kanta.


“Idan na ce zan yaƙi zuciya akan ka, zan cuce kai na, ban cancanci komai ba sai kyakkyawan sakamako, zan iya barin komai a kan ka, zan jure haƙurin rasa komai akan ka amman ba zan iya raka ka ba, ni nafi dacewa da kai Abdool, ba zan jure ganin wata ta raɓe ka ba, ba a hallinta maka wata matar aure ba, face Amira.
Wallahi ina son ka Abdool fiye da irin son da uwa take yi ma ɗan ta, kai mafarki, kuma kai kaɗai ne cikar burina, idan har na rasa ka Abdool to sai dai ko wace mace ta rasa ka”


Cige bakinta ta yi tana karɓar kukan da ya zo mata gadan-gadan. Mulmulawa ta yi ta mulmulo saman gado tana jin abu marar daɗi yana ratsa zuciyarta. Hoton da Abdool ya yi da Amal tafi tsurawa ido, tana masa wani kallo kamar wacce bata san shi ba.


“Kin yi sa'ar ɗan'uwa ni kuma zan yi sa'ar miji, ina son ka da iyalan ka Abdool”


Bata ankaro da ɗauki lokaci tana kukan ba, har sai da ta ji abu na ƙoƙarin rufe mata ido, alamar idon ya kumbura kenan.
Muryar Ummi da ta ji ne yasa ta sauri sauka saman gadon ta shiga bathroom ta wanke fuskarta, ta fito ta nufo falo.
A tsaye ta samu Ummi tana rataye da jakarta, mayafinta a hannu, Amal ma na tsaye a bayanta sai kumburi take, ita ala dole ga auta.


Tun da Amira ta soma saukowa downstairs Ummi take kalle da yanayinta, ga kuma kumburin da idonta da ƴa yi, fuskarta har ya soma ja abun ka da farar mace.


“Ba ki da lafiya ne?”


“A'a... Eh... Kai na ne yake ɗan ciwo”


Ummi ma uwace, ta fahimci Amira tana cikin damuwa ne, ko da bata fito a fili ta faɗa mata ba. Hannu ta kai ta shafa kan Amira zuwa wuyanta.


“Ki yi haƙuri kin ji, komai mai wuce wa ne, kin ji? Rayuwa bata tabbata haka amman dai ki yi tunani kin ji? Mu zamu fita, Haleema da Meesha ma sun fita Fauza ce kawai take bachi”


“Okay to sai kun dawo, me za'a girka?”


“No no kije kawai ki kwanta Shukura za ta yi komai, kije kawai ki yi ma kan ki karatun ta natsu”


Daga haka Ummi ta fice Amal na binta a baya, tana waigo Amira da harara dan ita har yanzu haushinta take ji, wai ta maida mata ɗaki kamar nata, daman can Amal ba son mutane take ba.
Maganar Ummi ta tsaya a mata a rai, me take nufi da ta yi ma kanta karatun ta natsu? Me hakan yake nufi? Juyawa ta yi ta nufi upstairs zuciyarta da tunani kala-kala.


RASHIDA POV.

Tana kewar ɗan ta sosai, wata ƙila dan kasancewarsa shi kaɗai ne ɗa namiji a gareta, ko kuma dan ita silar mutuwarsa.


“Na rasa abubuwa da dama, na rasa mijina, ɗa na, na rasa lafiya ta, yanzu kuma ina ƙoƙarin rasa iyayena, ni ka ɗai ce mai Aure da nake aikata zina? Ba suna nan da yawa ba? Miyasa ni bana da sa'a?”


Miƙewa ta yi tsaye daga saman prayer mat da take ta cire hijabinta ta nufi window.


“Idan har na bar gidan nan kowa zai tambayi dalili, kuma dole wasu za su gane abunda yake faruwa, idan kuma na zauna zan fuskancin tsagwama da takurawa, miye mafita?”


Hannu ta kai ta riƙa window, wannan karon sai ta koma zancen zuci.


‘Hakan yana nufin na rasa aure kenan har a bada? Idan kuwa gaka ne, to ba ni kaɗai zan shiga matsala ba, har Asmee tana ciki, kamar yadda nima ta jefa ni, kuma mijinta ma yana ciki, dan asirina ba zai tonu su na su ya rufu ba, bayan su ne silar komai, idan har na rasa Hilal ba zan rasa Alh Bashir ba’


Juyowa tayi ta jingina da window, yana motsa bakinta.


‘Idan kuma har na tona musu asiri na tonawa kai na, na matso da mutuwa ta kusa bayan kuma tana nesa da ni.
Amman kuma ba zai yarda ya tonawa kansa asiri ba, dan ba zai yarda ya rasa martabarsa da aikinsa ba, ni kuma ba zan rasa mijin aure ba, kuma hakan ba ƙaramin ƙona zuciyar Hilal da Asmee zai yi ba, su ma ya kamata su ɗanɗana yadda zafin baƙin ciki yake. I will never gave up, i will fight for my happiness, i deserve happiness again’


‘Idan kuma har Hilal ya rasa ni, be cancanci sake farin ciki ba, ya kamata ya ɗanɗana zafin rabuwa da ni, yasan akwai banbanci tsakanina da ita, Idan har ban more Hilal ba the love of my life be kamata wata ta more shi ba’


Komawa ta yi saman gado ta zauna ta ɗauki wayarta ta soma kiran Teema.




HILAL POV.


A gidan Hajiyarsa ya zauna har dare, sai da kowa ya watse sannan ya shiga sallama da Hajiya zai mata sai da safe.
Wani kallo uku saura kwata ta yi masa iron kallon Namijin da be san ciwon kansa ba, ƙasan carpet ya zauna kansa a ƙasa yana mai nuna mata tsantsar ladabinsa.


“Ban yarda ku kwana daki ɗaya da matar nan ba, kai dai ba jahili ba ne tun da kasan babu aure a tsakanin ku a yanzu”


Ba tare da ya ɗago kai ba ya ce


“Amman musulumci ya yarda da zaman idda, Hajiya zan bi duk wani umarni na ki, amman dan Allah karki gina katanga tsakanina da matana wallahi ina son ta”


“Kai wawaye Hilal, baka iya son mata ba, kana zurfafawa har ya zama baka iya ganin laifinta, ba zan gina katanga tsakanin ka da matar ka ba, dan ni ba irin surukar nan ba ne, amman zan nisanta ka da ita har sai ta gane kuskurenta ta yadda gaba ko ance ta aikata ba zata aikata ba, kuma ya zama dole ka ƙara aure!”


Ajiyar zuciya ya sauke still be ɗago ya kalleta ba, sai dai ransa be masa daɗi ba akan kalamanta.


“Zan yi duk yadda kika ce Hajiya, ke na fara sani kamin na san kowa a duniyar nan, ba zan zaɓi wata akan ki ba”


“Allah ya yi maka albarka, zan nema maka matar da zaka aura da kaina inshallah mai mutunci”


“Consider it done Hajiya, mu kwana lafiya”


Miƙewa ya yi tsaye idonsa sun rine sun yi ja sosai, irin ran maza ya ba ce sosai.






KALSOOM POV.


Tun da kowa ya watsa aka barta ita kaɗai sai duk ta ji babu daɗi ga kuma danuwar data saka ta gaba, tana ji a jikinta Hajiya ba zata barta ta zauna da Hilal ba. Haka ta zauna ta ci kukanta tun tafiyarsu har dare bata aikin komai sai kuka.


Tana jin tsayawar motar Hilal gabanta yayi dakan uku-uku. Ji take kamar ya zo mata da wani sabon abu, jin take kamar wata maganar zai faɗa mata wacce kunnuwanta ba zasu iya ɗauka ba.
Bata ƙarasa tsorata ba, har sai da ta ga ya ɗauki tsawon lokaci be shigo cikin gidan ba, hakan yasa ta unƙura cikin rashin kuzari ta miƙe tsaye, ta fito falo. Zaune ta same shi saman kujera ya haɗa kan sa da gwuiwa.


Ta ji babu daɗi sosai, sam bata jin damuwarta, ta sa damuwar take ji, bata san me Hajiya tace masa ba, amman a yanayin yadda taga mijinta ta karanci damuwarsa, duk abunda Hajiya zata ce mata ba zai wuce akan zamanta gidan ba, ko kuma wani abun daya shafe ta.
Juyawa ta yi zata koma ciki, sai kawai ta ji muryarsa ta daki dodon kunnenta.


“Ɗauko mayafin ki zamu je gida mu yi na su Momi bayani”


Bata juyo ba, ba kuma amsa masa ba, sai kawai ta cigaba da tafiyarta, hawayen na bin fuskarta.
Hijabinta yana kusa da gadonta, amman tsabar hankalinta baya jikinta haka ta bi tufafinta ɗaya bayan ɗaya bata ga Hijabin ba, sai kawai ta bude wardrobe ta ɗauko wani, Sannan ta ɗauki wayarta, ta handbang ɗin ta ta fito hawaye na cigaba da bin fuskarta.


Kamar mai koyan tafiya haka ta fito daga ɗakinta zuwa falo, shi kuma har lokacin yana nan zaune a yadda ta bar shi. Zuwa tayi ta tsaya bayansa tana hawaye.
Be yarda ya haɗa ido da ita ba, sai kawai ya miƙe tsaye ya nufi ƙofa ba tare da ya ce da ita komai ba.
Sai da ya yi ma motar key sannan ta fito daga falon ta shiga gidan baya, ja fisgi motar da ƙarfi, mai gadi na buɗe masa gate ya fara gudu kamar zai tashi sama. Shesshekar kukanta ne yasa ya rage gudun da yake ya faka gefen titi. Ya juyo ya kalleta.


“Try and cry so that i can tell you not to cry, Na fi ki shiga damuwa Kalsoom, ga damuwa na ga na ki ga na Hajiya ga na ƴaƴana ga na rashin yaro na duk ni kaɗai. Ba ki san waye Hilal ba shiyasa kike damuwar kan ki, yanzu haka za muje gida kina ciki damuwa da kuka? Kuka ba komai yake ƙara min sai karya min gwuiwa”


Be jira abunda zata ce ba, ya hau ttiti ya cigaba da tuƙa motar a hankali, har suka isa estate ɗin su. Gabanta ya faɗi sosai lokacin da ya danna horn a ƙofar gidansu.
An ɗan daɗe kamin a buɗe musu gate ɗin kasancewar a lokacin goma da ɗan gota, daman can a al'adar gidan da tara ta yi suke rufe gate.
Sai da mai gadin ya fara buɗe gate ɗin ya leƙo su ya ga su ne sannan ya koma ciki ya buɗe musu gate ɗin. Nesa da motocin gidan ya faka motarsa sannan ya jingina kansa jikin sitarin motar yana karanto irin bayanin da zai ma Daddy har ya fahimta.


“Ni ce zan faɗa musu komai?”


Dagowa ya yi ba tare da ya juyo ba ya ce


“Ta wace fuska?”


“Ta fuskar da za su fahimta, ka jira ni a nan”


Gefen hijabinta ta saka ta ƙara goge fuskarta sannan ta buɗe motar ta fita. Ita kanta tana fargaba yadda zata faɗa musu tun da ba magana ba ce mai daɗi, sai dai basa buƙatar a ɓoye musu komai. Ta daɗe tsaye jikin ƙofar falon tana tunani kamin ta tura ƙofar ta shiga.


Sallama tayi can ƙasan maƙoshinta, muryarta a dakishe alamar kuka ya kamata, babu kowa falon kuma kayan kallo a kashe, hakan ya tabbatar mata da sun shiga bachi ko kuma ƙannenta suna can suna karatu. Sai kawai ta juya ta fita daga falon ta nufi falon Dady.
Tun daga bakin ƙofar falon ta jiyo muryar tv, da alama yana kallon labarai ne.


“Assalamu alaikum”


Ta faɗa a daƙishe, haɗa baki suka yi gurin amsa mata. Duk da mamaki suka kalleta Momy ta aje plate ɗin abincin dake hannunta.


“Kalsoom shigo mana kika tsaya jikin ƙofa kamar baƙuwa”


Shigowa ta yi tana kuka, ta zauna kasa tana duƙunƙune fuskarka. Kallon natsuwa Dady yayi mata kana yayi gyaran murya ya ce


“Idan kin jin wani abu ne ya shiiga tsakanin ki da mijinki kuma ke ce mai laifi kar ma ki soma ba mu labari”


Cikin muryar kuka ta ɗago kai ta kalle shi


“Ba ni ce mai laifi ba, kuma Hilal ba shi da laifi, mahaifiyarsa ce ta saka ya sake ni”


Momi ta dafa ƙirjinta.


“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”


Dady kuma ya rumtse ido yana sauraren yadda maganar ta daki dodon kunnensa.


“Me kika mata?”


Momi ta sake tambaya.


“Wallahi ban mata komai ba, saboda mutuwar Rafiq ne”


A nan ta kwashe labarin duk abunda ya faru ta faɗa musu, sai da ta kai aya, sannan Dady ya kalleta ya ce


“Je ki shigo da shi”


Ba musu ta tashi tana kuka kamar ta shure ta fita. Hilal na tsaye jikin mota ta fito, yadda ya hango ta zuciyarsa ta nasalta masa bata faɗa musu gaskiyar abunda ya faru ba.


“Dady ya ce ka shigo”


Ta faɗa tun kamin ta ƙaraso kusa da shi, sai kawai ta juya, shi kuma ya rufa mata baya, zuciyarsa cike da zullumi.
Jimmm yayi lokacin da ya isa bakin ƙofar falon, sannan ya shiga da sallama yana mai sadda kansa ƙasa. Can jikin ƙofa ya zauna dan baya jin sakewar da zai ƙarasa kusa da su ya zauna.


“Kalsoom ta faɗa mana komai, kuma ba mu ga laifin ka ba, ko nine kwatankwacin abunda zan aikata kenan”


Cewar Dady. Hilal ya ɗan ɗago kaɗan ya ce


“Fushin Hajiya na ɗan wani lokaci ne, nan gaba kaɗan zata sake, shiyasa na ce za tayi zaman idda acen kamin Hajiya ta yarda na mai da ta”


Dady ya gyara zamansa, yana yi ma Hilal kallon hankali da kamala.


“Hilal ina son ka kasance mai haƙuri a duk halin rayuwar da ka tsinci kan ka. Kalsoom zata koma gidan ka amman ba yanzu ba, zata zauna a nan har sai lokacin da Hajiya ta ce ka zo ka tafi da ita, kuma ina mai baka shawara ka nemi matar da mahaifiyarka dake jin hankalinta ya kwanta da ita ka aura”


Da sauri Hilal ya kalli Dady


“Amman Dady bata hana....”


Dady ya ɗaga masa hannu.


“Ni a ɗana na ɗauke ka, kuma ba zan baka shawarar da zata cutar da kai ta cutar ƴata ba. Ka ɗauki shawarata kawai”


Maida kansa ya yi ƙasa.


“Amman Dady ita Kalsoom ta yarda?”


Dady ya kalli Kalsoom da ke kusa da Momi tana aikin kuka ya ce


“Zata yarda, ai tasan mahaifinta ba zai mata abunda zai cutar da ita, ka tashi ka je kar dare ya yi maka, ke kuma ki wuce ɗakin ƴar'uwarki”


Ita ce ta riga tashi ta nufi hanyar da zata sadata da ɗakunan tana kuka. Hilal kuma ya miƙe tsaye jikinsa a sanyaye ya bar falon, zuciyarsa na raya masa Dady yayi fushi ne shiyasa har ya yanke wannan shawarar.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *67*


Rasa ya yi inda zai sa kansa, gaba ɗaya ganin yake gabas da yamma sun haɗe masa, musamman ma daya dawo gida.
Sai tunani ya taru ya yi masa yawa, wanka daya saba yi kamin ya kwanta yau kam be yi ba, ko kayan jikinsa ma be damu ya canja ba haka ya hau gado ya kwanta, bachi ya ƙwauracewa idonsa gaba ɗaya, har safe be rumtsa ba, sai juyi yake kan gado.
Biyar da rabi na safe ya yi sallah asuba, bayan ya gama tasbihinsa ya ɗauko alƙu'ane ya buɗe ya fara karatu.


Ƴar ƙara wayarsa ta yi alamar saƙo ya shigo, sai dai be duba wayar ba, har sai ya gama karatun nasa yayi addu'ah sannan ya maida ƙur'ane mazauninsa ya aje. Kayan dake jikinsa ya cire ya ɗaura tawul ya shiga wanka, ya daɗe zaune a bathroom ɗin sai tunane yake kamin ya samu kuzarin watsa ruwa ya fito. Cikin rashin daɗin rai ya shirya, Farar shadda ya saka, be damu da duba kansa ba a madubi ba, ya saka agogon hannunsa tare da hulla, sannan ya ɗauki wayarsa yana duba ya nufi ƙofa,
Tunawa yayi da be saka turare ba hakan yasa shi ya dawo ya saka turaren sannan ya fice.


_Ka yi blocking ɗin number na, ka raba ni da ƴaƴana, Hilal ka ci amana ta, ina roƙon ka alfarma, dan Allah dan Manzon Allah ka bar ƴaƴa su dawo a gare ni su ne kawai gata na_


Yana karanta saƙon yasan daga inda


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login