Showing 75001 words to 78000 words out of 281103 words
Chapter 26 - ZAGON KASA Book Complete Document by Khadeeja Candy .txt
ga takardun results ɗin ko kuma jinin daya ɗiba tun da yace mata be kai, amman bata ga komai ba. Har ta gaji ta dawo dakinta .
Duk da tasan yau ba a ɗakinta Doc take ba, hakan be hanata chaɓa ado ba, dan ta ɗauki hankalinsa. Daman ya saba duk wacce yake ba girkinta ba yakan shiga yayi mata sai da safe, sannan ya wuce ɗakin da zai kwana.
Tun kamin ya shigo ɗakin, ta haɗa masa tea da lemun tsami dan tasan yana son haka, ta kuma saka masa zuma a maimakon sugar, sai ta ɗauko maganin dake jakarta ta buɗe ta kaɗa masa cikin tea ɗin har kusan guda biyar.
Tana mayarda jakar ta aje yana turo ƙofar ɗakin ya shigo, gabanta ya faɗi, abun ka da wanda bata saba ba, sai dai ta wayance taje ta rumgume shi.
To her surprise sai ya sauke hannayensa daga saman wuyanta, yana ɗan murmushi. Bata damu da abunda yake mata ba, dan a tunaninta fushin ɗazun ne na dress ɗin ta tayi. Cup ɗin tea biyu ne sai ta ɗauki ɗayan ta miƙa masa.
“Ga tea”
Hannu ya kai ya karɓa ya furta
“Thank you, good night”
Har ya juya, sai kuma ya juyo ya kalleta kamar zai ce wani abu, sai kawai ya sakar mata murmushin irin na fatar faki, ya juya ya fice.
Ɗakin Kalsoom ya nufa, ko da ya shiga ciki be ganta ba, ya duba bathroom bata ciki, sai kawai ya nufi ɗakin su Ezzah dan yasan ba wuce tana can ba.
A tsakiyar gado ya tsame ta tana ta tofawa yaransa addu'o'i, su kuma sai bachi suke tayi abun su. A bakin ƙofa ya tsaya yana kallonta yana murmushi, har ta gama ta taso ta nufo shi.
Hannu ya kai ya laƙƙamo kunkurunta, jikinta ya haɗe da nashi, ita kuma sai haɗiyar yawu take tana kallon kofin dake hannunsa, ƙamshin tea ɗin yana kai ma hancinta ziyara.
Kaɗan ya kurɓa ya kai mata kofin a baki, ɗan tsami tsamin data ji yasa ta jidaɗin tea, ta riƙe kofin da hannu biyu har sai da ta shanye tea ɗin gaba ɗaya.
Tana shanye tea ɗin ta saki kofin tayi masa kwance a jikin, wani irin bachi mai bala'in nauyi yayi gaba da ita.
“Hey...”
Ya faɗa yana girgizata, amman ina, tayi nisa har ƙoƙarin zubewa take a ƙasa, hannayensa yasa ya ɗauke ta cak, ya nufi ɗakinta da ita. Saman gado ya kwanatar da ita ya kwanta gefenta yana shafa fuskarta, zuciyarsa cike da mamakin abunda yake cikin tea ɗin.
Ya kusan minti talatin a gurin kwance, sai yaƙi yake da bachin dake son sace shi, yana unƙurin tashi yaji an turo ƙofar ɗakin, ƙin motsawa yayi sai ya lumshe ido kamar yayi bachi, sai ga Rashida ta ƙaraso har gurin tana leƙen fuskarsa, har da sa hannunta tana masa yawo da shi dan ta inda gasken yayi bachin.
Da sauri ta juya ta fita ta nufi ɗakinsa, keys ɗin motarsa ta ɗauka, ta fito waje ta buɗe motar tana masa bincike, seat ɗinsa na gaba ta buɗe ta fara bincikar takardun da suke gurin. Jikinta ne ya bata ana kallonta, da sauri ta fito daga motar, sai taga Doc tsaye ya rumgume hannayensa yana kallonta.
Kasa motsawa tayi, numfashita mai sai da yayi nisan zango sannan ya dawo, jin tayi kamar ƙasa ta buɗe ta shige ciki, a take mararta ta cika da fitsari.
___________________________________________
One free Page remained 🙌
BEST REGARDS 💖🌺
KHADEEJA CANDY 😘
*🌺🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺🌺*
Website
www.khadeejacandy.com.ng
*PAGE - 35. Last Free Page*
NOT EDITED ⚠️
Bata taɓa sanin gume na da zafi ba, sai a wannan lokacin, wani irin nauyi ta ji kanta yayi kamar an ɗauki duniyar nan an ɗora mata, yau ganin Hilal take ya cika ko ina na duniyar idanunta.
Yau kam ba ranar kuka ba ce, tashin hankalin daya same ta ya fi ƙarfin kuka, hakan yasa hawaye ba kusanci idonta ba, ashe abu mai sauƙi ake ma kuka, ta kasa yarda yau ita ce Hilal ya kama dumu-dumu ba.
“Kin san kina da HIV kike ƙoƙarin ɓoyewa Rashida? Do you know what lokacin dana ɗibi jinin ki result ɗin ba ɓata yayi ba, nace miki haka ne saboda ban yarda da abunda idona ya gani ba, na dawo na ɗibi jininki da na yarana da na Kalsoom nawa dan na gwada, so that na tabbatar idan da gaske kina ɗauke da cutar ne, amman ke kin san kina ɗauke da cutar kika bar ni ina kusantar ki?
Da ba dan wanann cikin ba, da sai mu ɗauki dogon lokaci a tare da dake baki faɗa ba right? What if all of us mun kamu da cutar nan?”
Ƙiri-ƙiri tayi masa da ido, cikin ƙarfin hali ta cira ƙafarta da tayi mata mugun nauyi ta tako ta ƙaraso kusa da shi.
“Kana tabbacin ni ce kaɗai nake ɗauke da cutar? Kasan ta ina cutar ta shige ni? Miyasa idon ka zai rufe har haka?”
“Ke da kan ki kike zargin kan ki, dan me zakiyi ma Doc Sabo transfer 100,000k? Dan me zaki ce idan ya kawo jinin kamin ya auna ya kira ki? You late Rashida ko da kika kira shi na riga na kai jinin amman yaƙi ya faɗa miki saboda ya san ni kamin ya sanni kuma ya san aikinsa, daman nasan ziyarar da kika kawo min ɗazu a office bata banza bace cox na lura dake kwata-kwata hankalinki baya jikin,
Bincike da kika min da tambayoyin da kika min ya tabbatar da akwai wani abu, and now what kin sa abu a tea ki bani nasha so that kiyi iya binciken ki ko? To bari na faɗa miki if something happens to my wife hmmm you're in trouble”
Sai a yanzu hawaye suka samu damar cika idonta har suka silalo zuwa kumatunta.
“Saboda na san idan kasan ina da HIV ba zaka faɗa min ba, idan har ya tabba ina da HIV Hilal to ta hanya ɗaya na same shi, wato sex kuma wani namiji be taɓa kusantana ba sai kai, a lokacin dana bar ka ya kusance ni ban san komai ba, sai a ɗazu nasa an nemo min Doc Sabo saboda na tabbatar idan har da gaske ina cutar ne, do you know who i try to protect? You and your dirty wife, Asmee told me everything about your bride but very soon gaskiya zata yi halinta, kuma ba zan taɓa yafe mu ku ba, aje ayi gwajin”
Tana kai nan ta raɓa gefensa ta wuce cikin falon. Juyowa yayi ya bita da kallo zuciyarsa na raya masa abubuwa da dama.
Kalamanta basu kama zuciyarsa ba, amman suna ƙoƙarin zaunawa akansa, what he believe shi dai yana da protection ɗin da ba kasafai cutar zata yi saurin kama shi ba, ko baya da protection, he's Doctor ya san cutar bata saurin kama namiji kamar mace, dan namiji ɗaya mai hiv zai kwanta da mace goma to dukkan su sun zama patient living with hiv, wato sun shiga sahun masu dauke da HIV acikin al'umma.
Amman mace ɗaya mai HIV zata kwanta da namiji 10 a rana, abu ne mai sauki namiji 2 ko 3 suka mu da wannan ciwon mai karya garkuwar jiki. Namiji zai iya daukan HIV kawai idan yana da wata kafa a gabansa abunda ya shafi kurji, yanka ko tsaga.
“He's lie”
Ya furta a hankali, yana murza saman goshinsa, zuciyarsa ta kasa yarda da zancen ta, duk da yasan Kalsoom take nufi, dan ita daya auna jininta be nuna haka ba, amman yasan result ɗin zai fito kuma dole gaskiya tayi halinta.
Shigowa yayi cikin falon cikin tunani da sarƙaƙiya, a saman babbar kujera ya zauna, ya dafe kansa, ɗaurewar da kansa yayi shi ya hana shi bachi har safe.
Har yayi sallah asuba ya dawo, be ji motsin Kalsoom ba, ita daya san wani lokacin ma takan riga shi tashi, a falon ya zauna yayi addu'o'insa sannan ya shiga ɗakinta, yadda ya tararda ita kwance rigingim har sai da ya tsorata, wani irin ninshari take kamarmacijin nan mesa na bachi, yayi mata girgizar duniyar nan amman ina, in ma ban da ƙara nauyin bachi babu abunda take.
Da sauri ya fita ya shiga ɗakinsa duba keys amman be ganshi ba, sai a lokacin ya tuna da suna guri motarsa da Rashida ta saka su jiya, da sauri ya fita daga ɗakin ya nufi gurin motar, ashe ma buɗe ta kwana, shiga kawai yayi ya kunna ta ya bar gidan.
Rashida na jin tashin motarsa ta duba agogon ɗakinta, 6:55am ya nuna, bata damu da rashin warewar gari ba ta tashi ba tare data tsaya wanka ba, ta canja tufafin jikinta zuwa atamfa ta ɗauki abaya ta ɗora sama, sannan ta ɗauki handbang ɗinta ta fice daga ɗakin.
Cikin sauri ta shiga motarta tayi mata keys gudun kar Hilal ya dawo, dan yanzu kam sam bata son haɗa ido da shi.
Gidan su Asmee ta nufa, cikin ƙanƙanen lokaci ta isa, haka ta riƙa musu horn har sai da mai gadin ya buɗe mata gate, kusan da motar Alhaji Bashir ya faka motarta, daman tasan yana nan dan yanzu be isa fita ba. Ƙofar falon ta riƙa bugawa tana sallama kamar zata tashi gidan.
Alhaji Bashir ne ya buɗe mata ƙofar yana tambayar lafiya, dan tun da yaji muryarta hankalinsa ya tashi, a tunaninsa ko tazo tayi masa wani abun ne.
Tun daga samansa ta kalle shi har zuwa ƙasan shi, daga shi sai guntun wando, sai da ta kai zuciyarta nesa sannan ta iya ƙirƙiro murmushi ta yaɓa a fuskarta.
“Matar ka na nan?”
“Lafiya kika mana sammako haka?”
“Lafiya ƙalau, sirrin mu ne, saƙon zan bata”
Kamin ya ƙara cewa wani abu har Asmee ta ƙaraso gurin tana tambayar wanene.
“Nice na doko muku sammako, saƙon ki zan baki”
Rashida ta amsa da kanta, tana mata murmushi. Wani kallo Asmee ta watsa ma Alhaji Bashir, irin ya zaka zo daga kai sai guntun wando haka. Sai kawai ya juya ya shige ɗakinsa.
Asmee ta riƙo hannunta suka shigo falon.
“Ke lafiya kika zo haka?”
“Taimakon ki nake nema, idan har baki taimake ni ba, zamu iya rasa ran mu ni da mijina”
“Subhanallahi miya faru?”
“Mijina ya aiko ni zuwa gare ki, maganar da zan faɗa miki sirri ce bana son kowa yaji, ko da kuwa mahaifiyarki ce ko mijin ki”
“Ban taɓa sirri dake ba na faɗawa mahaifiyarta ba, balle kuma mijina taso muje ciki”
Dar ƙarshen gadonta, Asmee ta kai ta suka zauna, sannan ta kalle ta tace
“Faɗa min damuwarki, matuƙar ina da maganinta wallahi zan miki”
“Irin samarin nan nake nema kidnappers”
Asmee ta daki ƙirji.
“Aka yi da wani ko za'a miki?”
“Wani muke son a a ɓoye mana shi, saboda ta hanyar shi ne kaɗai ne, mijina zai cigaba da rayuwa da ni, dan Allah idan kin san inda irin mutanen nan suke ki faɗa min”
“Ni ɗan maye ma miye haɗina da shi balle kuma ɗan kidnapped, Wallahi ban san wani mai wannan aikin ba”
Rashida ta kama hannayenta ta riƙe ta fara kuka.
“Ko cikin ƙawayen ki ba kisan wacca tasan mai irin wannan aikin ba? Dan Allah Asmee ki ceci rai na”
“Bana da ƙawar da zata iya faɗa min sirrinta har haka sai ke, ko da suna da irin waɗannan mutanen ba zan iya sani ba, sai idan gurin wannan Malamin zaki je, sai ya haɗa ki da wani cikin masu zuwa gurinsa, dan yana basu taimako sosai”
“A ina Malamin yake? Dan Allah ba ni addireshinsa”
“Ba a cikin garin nan yake ba, a ɗan dutse yake da kin shiga garin ɗan dutse kika ce Malam mai gobe da nisa ko ƙaramin yaro yasan gidan sa, bari na baki number wayarsa, kamin ki isa zan kirashi na faɗa masa”
“Na gode Allah ya saka miki da alheri, samin number”
Ta faɗa tana miƙa mata wayarta. Sai da Asmee ta saka mata Number sannan tace
“Amman kin san garin kuwa?”
“Karki damu zan tambaya har na isa garin, ai bada motana zan je ba, gidan mu zan bina na aje motar, saboda gudun sa ido”
“Allah yasa a dace, amman ina jin tsoro Rashida”
“Babu abunda zai faru, ba mummunan abun zan aikata ba”
“Dan Allah aro min niƙab ɗin ki da Hijab”
Ba musu Asmee taje ta ɗauko mata ta saka.
A gaggauce ta fice da daga gidan, zuciyarta har wani ɗar-ɗar take, tana ayyana irin rashin mutuncin da zatayi Doc Sabo, lallai yau zata nuna masa ta fishi zama yar duniya, Zagon ƙasan da yayi mata ƙarami ne, yanzu zata masa babban.
Kamar yadda ta tsara, a gidansu ta biya ta aje motar, ko cikin gidan bata shiga ba, balle su gaisa da Momi, tana rufe motar ta fito ta tari Napep ta shiga, ya ɗauki hanyar tasha da ita.
HILAL POV.
Be daɗe ba ya dawo, daman allurai kawai yaje ya ɗauko, yana shiga ɗakin ya haɗa allurar yayi mata, sannan ya ɗauko tawul ya jiƙa shi da ruwa, ya riƙa dafa mata a goshi.
A hankali ta fara motsi tana nishi da miƙa irin ta gaji sosai ɗin nan, hankalinsa ya ɗan kwanta lokacin daya ga ta buɗe idonta, sai ya sakar mata murmushi.
Daker ta unƙura ta tashi zaune, saboda nauyin da jikinta yayi mata.
“Wane irin bachi nayi haka?”
“Magani na saka miki a tea ɗin, tashi kiyi sallah”
Ta ɗan kalli window taga yadda rana ta fara hudowa, sannan ta unƙura da zimmar tashi tsaye, sai Doc ya kai Hannu ya riƙa hannunta.
“I trust you Kalsoom dan Allah kar ki bani kunya”
Wani kallo tayi masa, irin ban gane ba. Sai kawai yayi murmushi yana ƙoƙarin ɓoye feelings ɗinsa.
“Yanzu idan aka ce ina da hiv zaki zauna da ni?”
Dawowa tayi ta zauna, ta kai hannayenta ta riƙa fuskarsa.
“Idan har kana da hiv zan zauna da kai, kuma idan har kana da shi nima nasan ina da shi, so babu dalilin ƙyamar juna”
“What if aka ce ke kike ɗauke da shi ba mu ba?”
Shiru ta ɗan yi tana nazarin tambayoyinsa, anya Doc zai mata irin wannan tambayar haka kawai.
“Idan har ni nake ɗauki da cutar zan nisanta kai na daga gare ku, gudun kar ku kamu da cutar, har sai ta zama aids, domin wannan kwayan cuta HIV (human immunodeficiency virus) bata rayuwa da keu a wajen jiki, saboda haka akan iya kamuwa da ita ta hanyar kissing ko kuma yin anfani da wani abu wanda me dauke da cutar ke anfani da shi, kamar kofin shan ruwa, abun yanke farce, da brush.
Amman da zarar cutar ta kai marhala na karshe ma`ana AIDS (acquired immunodeficiency syndrome) zan cigaba da mu'amala da ku kamar yadda na saba, saboda ba`a kamuwa da ita ta hanyar kissing, cin abici tare da me dauke da ita, amfani da kayayyakin ko abubuwa da me dauke da ita ke anfani da su, kamar kayan sawa, wayan salula, agogo, wanka a swimming pool, zama a kujera, cizon sauro, ma taci comb, tawul, da kuma tafiya, hada hanu, zama,da yin aiki tare da me dauke da cutar, amman ba zan bari ka kusance ni ba, ko da kuwa zaka na shan magani da amfanin da kororon roba, saboda it's risk.
Sai dai kuma ka sani, rayuwata zata tarwatse zan nisanta da ƴaƴanka, duniya zata ƙyamace ni, kuma dole na rabu da kai”
Ta ƙarasa maganar hawaye na bin fuskarta. Ɗan murmushi yayi ya tashi yana ƙoƙarin ɓoye hawayen da suka cika masa ido.
“Intelligent woman, je kiyi sallah zan haɗa ma yara breakfast”
Har ya fice hawaye take, zuciyarta cike da tunanin abunda yasa Doctor yayi mata wannan tambayar.
NAMRA POV.
Ko ta koma gida, ta samu duk sun tafi walimar aure, ta wata maƙociyarsu, da ake yi yau jumma'ah. Mardiya ce kawai a gidan, ta zauna cikin ɗakin ta rafka uban tagumi.
Sallamar da Namra tayi ma sai da ta firgita ta.
“Ke lafiya kike kuwa? Ke kaɗai aka bari a gidan?”
Namra ta tambaya tana zama kusa da ita. Ajiyar zuciya mardiya ta sauke.
“Kawai ina tunanin rayuwa ne”
“Rayuwa kuma kamar ya?”
Shiru tayi tana tunanin irin ƙaryar da zata yi ma Namra, dan bata son faɗa mata asalin abunda yake damun ta.
“Inna ce duk ta bi ta dame ni akan rashin auren nan, kamar ni nayi ma kai”
“Ayyah wai wani abun ba'a kusa yake ba, komai yana da lokaci”
“Na sani matsalar iska ne yake damuna, ina ganin kamar shine ya hana ni aure, amman ita inna ta kasa ganewa”
Ta bijiro da damuwarta a fuskarta kamar da gaske abunda yake damunta ɗin kenan. Ita kuma Namra sai tausayinta take.
“Ki riƙa azkar kina faɗawa Allah damuwarki, inshallah zai miki magani”
“Ina yi Wallahi babu inda ba mu shiga akan neman taimako ko ina sai ace mana Aljani ne ya aure ni”
“Subhanallahi, amman Mardiya, ai dole aljani ya aure ki tun da kina yawo babu ɗankwali, gashi kina yawan sauraren waƙe-waƙe, da ace baƙara kike yawan karantawa nayi imani ba zai samu nasara akan ki ba”
Ajiyar zuciya Mardiya ta sake saukewa, a karo na biyu, ta ƙara gyara zamanta.
Namra ta kalleta cike da tausayawa tace
“Ki samu allo ki rubuta suratul azari, daga farkon ta har ƙarshe, idan kin yi alwala la'asar kika rage ruwa sai kiyi amfani da su ki wanke rubutun ki shanye har kwana uku, indai matsalar aljani ne mai hana aure inshallah zai rabu da ke”
“Na gode sosai Inshallahu zan gwada”
“Allah yasa a dace, da naso ki raka ni kasuwa amman naga kamar kina cikin damuwa bari mu bari har gobe”
Kamar kar Namra tayi maganar nan da nan Mardiya ta kai idonta gurin ƙaramar jakar da Namra take riƙe da ita, sai kuma ta kawar da kai.
“Mu bari har goben dai yanzu yamma yayi”
“Eh nima ai haka na gani”
Ƴar nokiyar dake hannun Mardiya ce tayi ƙara, sai ta tashi ta bar ɗakin tana amsa wayar.
Tashi Namra tayi ta cire hijabinta, ta rataye, sannan ta ɗauki jakar wanda kuɗin suke ciki ta saka a cikin akwatin Mardiya na kaya, da zimmar ta aje a cikin dan kar taje ta jefar da ita wani gurin, sannan ta fita