Showing 159001 words to 162000 words out of 281103 words
Chapter 54 - ZAGON KASA Book Complete Document by Khadeeja Candy .txt
ba matuƙar tana gidansu, a ƙarƙashin iyayenta.
Hijabinta ta ɗauka ta saka, ta ɗauki jakarta da wasu ƙaƙanan abubuwa nata ta saka a jakar sannan ta fito, tun da ta baya bq ɗin baya ta sake kallon ta ba har ta fice daga gidan.
Fuskarta ta kumbura sosai haka ma idanunta, duk wanda ya ganta zai san tayi kuka, hakan yasa ta sanda kai ƙasa har ta isa titi. Napep ta tara sai da ta shiga sannan ta soma tunanin inda zai kai ta. Bata da wadataccen kuɗin da zata kama wani gidan ta zauna, kuma ta san ba mutuncin ta ba ne ta kama gida a wani gurin. Kuma bata jin zama a gidan dan zata iya aikata komai saboda baƙinciki.
“Hajiya ina za a kai ki?”
Tsayawa tayi tunani, har tashi Napep ɗin.
“Kai ni tashar mota, inda ake hawa motar sokoto”
“To amman yanzu tashar gov sun tashi sai dai babbar tasha”
Ya hau kan titi yana ƙara ƙure volume ɗin napep ɗin dake tashin wakar Umar m shariff. Ita dai saurare kawai take tana hawaye har suka isa, ɗari biyu ta ciro ta bashi ya miƙa mata canjin naira hansi sannan ta fita shi kuma ya juya.
“Sokoto, Kano, Kaduna, Abuja, jigawa, Kebbi, Zamfara”
Haka ƴan union ɗin suke ta faɗi suna neman passengers. Wasu suka yo kan Namra da gudu suna tambayar ta inda zata ta, tsaye kawai tayi tana tunanin inda zata ce duk da ta zo da niyar zuwa sokoto ne sai kuma ta ji ba zata iya, har tana jin ma kamar ta koma gida...
“Hajiya Kaduna zaki je?”
Wani daga cikin su ya tambaya, sai ta ɗaga masa kai.
“Eh Kaduna zan je”
“Ga mota can daman mutum biyu ake jira, ina kayan ki suke?”
“Bana da kaya”
“Okay muje ga mota can”
Shine yayi mata ja gaba har gurin motar, sannan ya faɗa mata kuɗin motar. Cikin rashin kuzari ta cire ta biya, sannan ta shiga motar tana ta doubting akan taje can ɗin ko kuma a'a. Idan taje kaduna gurin wa zata je? Tun da bata taɓa zuwa ba duk da akwai taubashiyar Anty Amarya a can amman bata tunanin zata gane inda take tun da zuwan da duka yi tun da daɗewa ne kuma da motar gida, sunan unguwar ma bata riƙe sosai ba.
ASIM POV
A sale ya fito daga gidan, bama abunda ya fi baƙanta masa rai kamar jiƙa masa tufafi da Namra tayi, Yana ƙoƙari buɗe motarsa ya hango Mardiya tafe, ɗan tsayawa yayi yana kallon takunta, cikin yanga izza take tafiyar dan kuma kawai ta ɗauki hankalinsa ne. Shi kam yasakar mata ido sosai yana kallonta duk da jiƙaƙin tufafin ne a jikinsa, amman hakan be hana shi tsayawa gurun motar ba har ta iso, dan kawai ta ga shine yake tuƙa motar, yasan ko ba komai zai burge ta tun da yasan mata sun fi son mai mota.
Sai da ta kusa ƙarasowa sannan ya buɗe motar ya ciro ƙyale yana goge jikinsa.
“Asim ina kwana?”
Ta gaishe shi cikin kashe murya da ƙarawa muryar zaƙi. Da sauri ya kalleta yana murmushi kamar ba shine ya fito rai a ɓace ba.
“Ah lafiya ƙalau Mardiya ya gidan?”
“Gida ƙalau wallahi miya jiƙa mata kaya haka?”
“To sha'anin ne kin san halin na ku sai a hankali. Gari za a ne?”
“Eh wallahi zan ɗan shiga gra ne”
“Okay shige na aje ki”
“Mashallah ka siye sabon mota ne?”
Ta faɗa tana kallon motar cike da burgewa.
“Eh ai tama kwana biyu, sabuwa dai muke jira”
Buɗewa tayi ta shiga, sai shima ya shiga yana ƙoƙarin tashin motar ta kalli gate ɗin gidansa ta ce
“Kar fa Namra ta hango mu ko a kai mata rahoto”
“Mtsssss amman Mardiya ma kin mai yarda ni wani wawa, ni kam ai nafi ƙarfin matata ba irin mazan nan bane na banza, ashe ke matsoraciyace ba zaki iya kishi da ita ba”
“Ai kishi dabam, da ace yanzu aurna na ne zaka yi to bana shakar taji komai, amman kaga yanzu babu wata magana ta aure dole na ji tsoron irin maganar da zata je mata a kunne”
“To kisa a ranki auren ki zan yi”
Ya faɗa yana ƴar dariya. Itama dariyar tayi mai cike da jindaɗi. Har ya kai ta inda zata je fira suke kamar masu masoya ita kuma sai wani lanƙwashewa take tana karairaya. Daman shi tuni da kasheshi da kalamanta ma.
Daga gra ya wuce gidan Hajiya Sadiya, be same ta a gidan ba hakan ya tabbatar masa da akwai inda taje kenan. Ɗakinsa ya shiga ya canja tufafin jikinsa ya saka waƴan can a washing machine sannan ya dawo ya zauna. Yarinyar ɗazu ce ta faɗo masa a rai a ƙoƙarinsa na kawarda tunanin Namra a ransa dan ganin yake ita babbar maƙiyiyarsa ce, ko kaɗan baya nadamar sakinta da yayi kuma he's ever ready ya mai data idan ta yarda ta zubar da cikin.
Number yarinya ya nemo ya danna mata kira, ringing biyu ta ɗauka ciki muryarta mai sanyi. Cikin turanci ta soma watsa masa tambayar wake kiran shima ya maida mata da yaren da tafi ganewa. Nan da nan ta sake da shi suka gaisa duk kalmar da tayi masa sai ya maida mata, ya ɗan tambaye kaɗan daga rayuwarta, sai da amsa masa a inda abunda take tunanin ya sani. Ya jidaɗin da tace masa ita ƴar Katsina ce, daman ta faɗa masa tun a chat amman a yanzu ne take faɗa masa sunan unguwarsu a Katsina.
Sun daɗe suna waya sannan yayi mata sallama ya kashe wayar. Ko da ya kalli ogagon ɗakinsa ƙarfe biyu saura ya gani, sai ya tashi yaje yayi alwalah yayi salla a cikin gida. Bayan ya sallame zancen gidan ya faɗo masa rai, wai kar dai Namra tace zata sai da gidan ta gudu da kuɗin. Wayarsa ya ɗauka ya aika mata text sannan ya kunna data shi.
HILAL POV
Yana cikin aiki wayarsa tayi ringing. Sai dai be duba mai kiransa ba har sai da ya kai ƙarshen duba marasa lafiyar da yake.
Sai da ya gama da duka katinan da suke gabansa, sannan ya tashi ya nufi office ɗinsa yana duba wayar. Number Dady ya gani Abbah Rashida, yayi mamakin ganin kiran, sai dai be kawo komai a ransa ba dan a tunaninsa, akan maganar shiga kotu ne zai sa ya kira shi tun da monday nan mai zuwa za a shiga.
Sai dai ganin text ɗinsa ya sa gabansa faɗuwa, miyasa yake son ya zo gidansa ya gansa? Duk akan maganar ne ko kuma wani abun daban. Ba tare da shakar komai ba ya shiga office ɗinsa ya cire ƴar samansa ya ɗauki keys ɗinsa ya fice.
Cikin ƴan mintuna ya isa gidan su Rashiida yayi gudu ne a hanya sosai, dan baya son Rafiq ya farka baya kusa. Yana ganin Motar Rashida da ta Dadynta yasan tana cikin gidan.
Be fita cikin motarsa ba har sai da ya kira Dady yace masa gashi ya iso.
“Ka shigo ciki”
Shine reply ɗin da ya masa a wayar cikin tsawa, ko kaɗan Hilal be ɗauki haka a wani abuba dan har gobe yana girmama iyayen Rashida tun da akwai ƴaƴa a tsakaninsu, kuma duk mutumen daya aura maka ƴarsa ya fi gaban ka raina shi ko da kuwa kun rabu da ƴar ne.
Buɗe motar yayi ya fito, yana tuna when last ya shigo gidan nan. Babban falon Dady ya nufa daman ko lokacin da yana surukinsu a can Rashida take sauke shi idan sun zo gidan.
Yana shiga ya samu Dady zaune yana jiran ƙarasowarsa. Momy ma tana zaune daga gefe tana watsa masa harara. Cikin ladabi ya ƙarasa ya zauna saman kujera yana gaishe shi. Dady be amsa ba dan ba gaisuwar ce a gabansa sai kawai ya hau shi da kalamai masu zafi.
“Ma cuce mayaudari, yanzu da kaga ka laƙa mata ciwo shine ka sake ta ko? Ai ni daman nasan sakin da ka yi mata bana Allah ba ne, kaje can kayi yawon ka ka samu cuta kaxo ka laƙa mata”
Ɗaga kai yayi yana kallon Dady maganar ta xo masa a baibai kuma da halshe biyu. Radhida ce ta faɗa musu ko kuma su suka gano haka? Har da shi tace yana ɗauke da cutar ko kuma ita kaɗai?
“Dady zan so Rashida tana nan kamin na yi magana”
“Ta zo ka kunsa mata baƙinciki ko? Ka zo ka ƙaryata ta ka ƙara mata baƙinciki ko? Ɗan iska marar mutumci, wallahi Allah sai ya isar mata”
Wannan karon Momy ce take magana tana wani ɗagowa kamar ta kama Hilal ta dake shi.
“Kuna magana ne a jahilce baku san gaskiyar lamari ba, ya kamata a kira Rashida ayi komai gani ga ta sai a fitar da wanda be da gaskiya”
Dady ya kalli Momy.
“Jeki ki kirata. Wallahi na rantse maka Hilal sai duk abunda na tara ya ƙare amman tun da kayi ma ƴata haka sai na wulaƙanta ka”
Ya ƙarasa yana kallon Hilal, jijiyar kansa har wani tashi take irin na ɓacin rai ɗin nan ya kai maƙura.
Momy ta tashi a hasale ta nufi sashenta. Kai tsaye ɗakin Rashida ta nufa sai da ta soma da buga mata ƙofa amman ta ƙi ta Buɗe har yanzu, sai kawai Momy ta zauna a gurin ta soma mata kuka.
RASHIDA POV
Babu yadda Momy batayi amman Rashida ta ƙi ta buɗe ƙofar har duka ƙanenta suka dawo daga makaranta.
Sai da aka yu salla la'asar sannan ta buɗe shima dan Momy ta zo ta zauna a gurin tana kuka ne. Da sauri Momy ta shiga cikin ɗakin cike da tausayin ƴarta.
Bata yarda ta zauna kusa da ita ba, sai dai space ɗin dake tsakaninsu ba wani mai tsawo bane sosai.
“Hilal ne ko? Shine ya saka min wannan cutar shiyasa ya zaɓi rabuwa da ke”
“Miye amfanin sanin wanda ya sa min wannan cutar, bayan cutar ta riga da ta kamani, babu amfanin ayi ta jayayar abu har a tona asirinsa, duk abunda ya faru da ni, Dady ne ya ja min”
Momy ta kalleta
“Ga Hilal can mum kira a falon Dady ki amman ya ce ba zai yi magana ba sai kina nan”
Gabanta yayi dakan huɗu-huɗu har bata san lokacin data kalli Momy baki sake ba.
“Miyasa kuka kira shi? Me zai muku?”
“Shine silar wannan ciwon na ki Rashida dole na zauna da ke, dan me zai sake ki”
Fashewa tayi da sabon kuka.
“Ni bana son ganinsa dan Allah yayi tafiyarsa”
“Ba zai je ko'ina ba har sai an tabbatar da wannan maganar yau”
Momy ta riƙa hannunta suka fito tare. Ba dan Rashida ɗin ta so ba, sai jan Momy dake janye da hannunta har suka isa falon. A jikin ƙofar Rashida ta tsaya ta risina kanta na ƙasa dan bata son kallon Hilal.
Shi kuma ya tsare ta da ido tausayinta duk ya kama shi.
“Dawo nan ki zauna, babu abunda ya isa yayi miki”
Cewar Dady yana nuna mata kusa da shi. Tasowa tayi ta dawo nan tana shirin zama kukan da take ɓoyewa ya fito fili.
“Yi shiru yanzu ba lokacin kuka ba ne, faɗi maganar ki”
Kasa magana Rashida tayi har sai da Hilal ɗin da kansa ya soma bada labarin abunda ya faru from a to z. Sun gamsu sun kuma samu tabbaci ganin yadda Rashida take ta kuka ta kasa ta kare kanta.
Dady ne ya miƙe tsaye ya soma safa da marwa. Ajiyar xuciya kawai yake saukewa yana maimaita
“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”
Momy kan saka kanta yai cikin hijabi tana kuka. Rashida ma kukan take kamar ta mutu. Dady ya kalli Hilal cikin idonsa na marasa kunyar iyaye ya ce
“Zaka iya tafiya”
“Na gode”
Hilal ya furta sannan ya miƙe tsaye ya fice, jiki a sanyaye.
“Kin cuci kan ki Rashida kin kuma watsar da tarbiyar dana baki yanzu ai kin ci ribar zina sai kije ki auri wanda kuke aikata saɓon tare, uban waye ne ma wannan mutumen?”
Dady ya tambaya a tsawace. A nan Momy ta ɗago kai ta kalleshi cikin ɓacin rai ta ce.
“Duk waya ja mata wannan abun ba kai ba? Tana zamanta lafiya ƙalau da mijinta kace dole sai ta yi aiki, babu irin lallaɓar da yarinyar da mijinta ba su maka ba, amman ka dage akan dole sai tayi aiki, ai ga ribar aikin nan ta kwaso ta kawo maka, shine yanzu zaka taso ka rufe ta masifa ka barta ta ji da abunda yake cikinta ko so kake ta kashe kan ta”
Tashi Rashida tayi ta bar musu falon tana wani irin kuka kamar ta mutu. Momy ma miƙewa tayi tsaye ta fice a hasale tana kuka da bata san ranar tsayawar haweyen ba.
Komawa Dady yayi ya zauna har yanzu xuciyarsa bata gama gamsuwa Rashida ƴarsa tana ɗauke da cutar ba, shi dai ya fi son ayi wani gwajin.
Ajiyar zuciya ya sauke, wani yana tuna wani kalami da wata tayi masa a 1952.
KALSOOM POV
Har yanzu hankalinta ba a kwance yake ba, amman ba kamar da ba, dan yanzu tana da tabbacin Hilal ya yarda da ita, ta kan samu sassaucin hakan idan ta tuna.
Sai dai har yanzu bata cin abincin kirki, sai dai abu mai ruwa ko kuma ruwan kawai.
Tana cikin kitchen ta ji ƙarar tsayawar motarsa, nan da nan ta je aikin da take ta nufi ƙofar falo ta tarboshi.
Yanayinsa ya kararta da ita damuwar mijinta, dan haka bataa buƙatar tambayarsa akwai damuwa ko babu mafi ala kawai ta kwantar masa da hankali sannan ta nemi sanin dalilin damuwar tasa.
Da kanta ta zaunar da mijinta ta ɗauko ruwan sanyi ta siyaya masa a kofi ta kai masa a baki, kaɗan ya sha, ya ɗauke baki, sai ta cire ɗankwalinta ta soma shafe masa gefen fuska.
Hannunta ya riƙe ya jata zuwa ƙirjinsa ya rumgume ta, zuciyarsa cike da tsantsar ƙaunarta.
“Hajiya ta har yanzu bata yarda da ke ba”
Ya faɗa dan ya canja tunaninta izuwa wacan damuwar ta gurin Hajiya.
“Ba lallai ne tayi saurin yarda da ni ba, kuma tana da damar ta zarge ni yadda ranta yake so, zan ɗauki ko wani irin hukumci Hajiya ta yanke matuƙar hakan xai sa ta aminta da ni”
Tana kwance a ƙirjinsa take maganar hawaye na bin fuskarta.
“Hukuncinta ɗaya ne, wai sai na ƙara aure”
Ɗagowa tayi ta kalleshi ta girgiza kai ta fashe da kuka. Ɗan murmushi yayi dan kukanta ya sashi nishaɗi, yana shafa gefen fuskarta ya ce
“Ba zaki yarda mijin ki ya ƙara wata ba ko?”
Kai ta ɗaga masa. Sai ya ce
“To ya zaki yi da Hajiya?”
“Wallahi ban aikata ba Hilal Allah shine shaida na”
“Ai ba nine ban yarda ba, Hajiya ce bata yarda dake ba”
“To a tambaye Rafiq ɗin ai yana magana idan na bashi wani abun zai faɗa”
“Rafiq baya magana yanzu, ya koma wani iri kamar ba shi ba”
Cikin rashin jindaɗi yayi magana, yana ciro wayarsa dake aljihu tana ringing. Saurin picking yayi ganin number Nurse ɗin dake kula da Rafiq.
“Subhanallah okay gani nan zuwa”
Yayi saurin ɗaga Rashida daga jikinsa, ya tashi ya nufi ƙofa hankali tashe. Rashida sai tambayar lafiya take be kula ta ba.
ABDOOL POV.
Sai da dare ya dawo Part ɗin Ummi ɗan ya tabbatar ta dawo a lokacin. Duka falo ya same su zaune suna ta fira. Ummi na ganinsa ta aje lemun fata dake hannunta tana masa kallon mamaki.
“Ni nace fa naga Motar ka Haleema tace min wai ba kai ba ne”
Ya ɗan wara ido yana kallon Haleema, kamin ya zauna a kujarar da Amira take zaune dan three seater ce.
“Ai ba zata faɗa ba, a ɗakin ki na same su suna ta miki taɓe taɓe ita da wannan yarinya”
Ya nuna Amira data tsare shi da ido.
“Wallahi gyara ne Amira take miki, ba wai komai muke miki ba, hba sai ka ce yara”
Ummi bata bi ta kan Haleema ba ta kalli Abdool.
“Ya hanya? Ka ci abinci?”
“Na ci gidan Babana, ku da ban ma tarar da ku ba”
“To ai baka faɗa ka ce za ka zo ba, gashi ma miyar kifi aka yi kuma baka son kifi”
“Ni wallahi wannan zuwan ma be min daɗi ba, ɗan hutu ne na samu ina da zumuɗi zan zo gida shine wai kuma Mai Martaba sai naje zaria ɗaurin aure”
“Ai shine dai-dai kai kenan baka son shiga mutane kamar wani aljani. Me za'a girka maka?”
“Wa zai girka min?”
“Ni”
“Okay to a min wani abu new. Ba wanda aka saba ba”
Tashi Ummi tayi ta nufi ɗakinta tana dariya.
“Kai kam matarka ta shiga uku kullum.ba maimata abinci sai anyi wani abu new”
Shima.dariyar yayi ya tashi ya rufa mata baya yana faɗin
“Lallai kam, idan kam mace bata iya abincin ba zamu samu matsala da ita”
“Ko da kana son ta?”
“Aifa...”
Amira ta bishi da ido, daɗi har cikin rai. Dan tasan indai ɓangaren abincine ba daga baya ba, tun daga kan waɗanda ake yayi har na gargajiya gwargwado ta iya. Ga kuma xama da yayi a kujerar da take zaune abun yayi mata daɗi.
[7/18, 8:12 PM] Khadeeja Candy♥: *62*
*1952*
```Cikin rawar jiki ta shigo gidan sai rabon ido take idonta tab da ƙwalla, kana ganinta kasan tana cikin halin damuwa. Bata san inda zata dosa ba tun ba data samu masu gadin suka barta ta shigo cikin gidan, gaba ɗaya a rikice take har bata iya kwantar da hankalinta ta banbanta parts ɗin
“Ke me kike a nan?”
Da sauri ta juyo ta kalle tana ganinsa sak tasan ɗan mai gidan ne, hakan yasa ta risina har ƙasa ta gaisheshi muryarta na rawa. A maimakon ya amsa mata sai kawai ya ƙara haɗe fuska dan ya fahimci irin mutanen ne masu zuwa gurin mahaifinsa a taimaka musu
“Gurin Mai gidan nan na zo, taimako za a min, mahaufiyarmu ce bata da lafiya shine aka rubuto mata magani a asibiti kuma sun ce za a mata aiki, shine aka ce na zo nan za a taimaka mana”
Da kuka ta ƙarasa maganar tana nuna masa takardun asibiti dake hannunta. Karɓar takadardun yayi yana kallon fuskarta da kuma yanayinta, taga komai a rubuce amman saboda mugun nufinsa ya kasa gasgata ta.
“Wata ƙila ma ƙarya kike, haka kuke dan kawai kun ga mahaifina yana taimakawa mutane, kowa sai ya kwaso ƙaryarsa ya kawo ”
“Wallahi ba ƙarya na ke ba, idan baka yarda da ni ba zamu iya zuwa ka duba ta