Showing 99001 words to 102000 words out of 281103 words
Chapter 34 - ZAGON KASA Book Complete Document by Khadeeja Candy .txt
Wallahi”
Anty Amarya ta tashi da sauri ta nufi part ɗin Abbah, kamin ta ƙarasa ta hangoshi jikin mota, yana jiran direbansa ya tashi motar.
Gurin ta ƙarasa ta tsaya masa a gaba.
“Kai kace azo da Namra?”
“Amman sati ɗaya na yarda ta yi”
Haka kawai ya faɗa ba tare daya kalleta ba, ya buɗe motar ya shiga. Sai ga Anty ta dawo falon da far'ah tana cewa Maryam da Aisha su je su taho da ita.
RASHIDA POV.
Kwanan ta biyu asibiti suka sallame ta bayan anyin mata wankin ciki, sai dai duk tsawon kwana biyun da tayi Hilal be liƙe inda take ba, duk kuwa da kasancewar a gurin yake aiki.
Kuma duk tsoron kwanakin be kawo yaransa ba, sai dai ma'aikaitam gurin sun yi ta zuwa ganinta, sanin cewa ita uwargidan Doc ce.
Ranar data dawo gida ta ci kuka kamar ta mutu, babu irin rarrashin da ƴan'uwanta ba su mata ba amman sam ta ƙi ji sai da tayi kukanta har ta gaji sannan ta saurarawa kanta.
Daren ranar da aka sallame ta ne Asmee ta zo gidan, ita tayi ta bata haƙuri tana ƙara mata ƙarfin guiwa akan inda zata kai ta Hilal ya mayarda ita, sun kitse magana akan zasu tafi tare gobe idan Rashida zata fita. Sun daɗe suna tattauna lamarin kasancewar su biyu ne kawai a ɗakin, tun Rashida na kuka har ta daina.
Tun dawowarta gida bata sa komai a cikinta ba, bata komai sai tunanin Hilal da kuma makomarta, gani take idan har da gaske tana da hiv ya makomar iyayenta zai kasance tun da dole ne tayi mu'amala da mutane. Wayarta ta janyo ta kira wata ƙawarta wace ta kasance likita ce. Bugu biyu ta ɗauka, bayan sun gaisa, Rashida take ce mata
“Dr Fatima, ina son na tambaye ki ne akan hiv, wata sis nace take rubuce-rubuce shine take tambaya ni kuma na ce bari na tambaye ki tun da ni ba sashena ba ne”
Dariya Dr Fatima tayi ta ce
“Amman gaskiya bayanin yana da ɗan tsowo, why not na yi miki ta whatsapp kina online yanzu haka”
“Yauwa to haka ma yafi, bari na hau”
“Daman na san ba zaki kira ni haka nan kawai ba”
Rashida tayi dariya bata daɗin rai ba, ta kashe wayar. A take ta kunna datar ta sa hau online. A contacts list ɗinta ta shiga ta nemi Dr Fatima tayi mata sallama. Sai da ta ɗauki ƴan mintuna sannan ta amsa sallamar sai ta koro mata da bayani.
“CUTAR KANJAMAU/TSIDA (HIV-AIDS)
HIV (human immune virus) ita kwayar cuta ce da take haifar da AIDS (Acquired immunodeficiency syndrome) ma`ana karyewar garkuwar jiki wadda aka fi sani da tsida ko kanjamau. Ita wannan cuta, cuta ce da take karya garkuwar jiki (immune system) wanda ke bada daman wanda, ke dauke da ita ya kamu da wasu cu tuttuka sakamakon karyewar garkuwan jiki. rashin kiyayewa ko kula da wannan cuta kan sa mutum ya halaka a takaitaccen lokaci kamar daga shekara 9 zuwa 11 ya danganta wani yanayi.
HANYOYIN DA AKE KAMUWA DA CUTAR KANJAMAWA/TSIDA
Ana kamuwa da ita wannan cuta ta hanyar shigar kwayan cuta HIV (human immunodeficiency virus) chikin jini. San nan hanyoyin da kwayar cutar ke shiga jiki na dewa, kan iya shiga ta hanyar haduwar jinin me dauke da cutar ga mara dauke da cutar kamar ta hanyar cizon sauro, maniyi, ruwan farji (vaginal fluid) mafi yawan cin masu dauke da wanan cuta na kamuwane ta hanyar saduwa (sex) da me dauke da cutar. Ana kuma iya kamuwa ta hanyar yin anfani da allurar da me dauke da ita yayi mfani dashi. San nan jarirai na iya kamuwa da ita kwayar cutar daga uwa ta hanyar shayar wa, da lokacin da suke a ciki (pregnancy).
Ita wanan kwayan cuta HIV (human immunodeficiency virus) bata rayuwa da keu a wajen jiki saboda haka akan iya kamuwa da ita ta hanyar sunbata (kissing) kokuma yin anfani da wani abu wanda me dauke da cutar ke anfani da shi kamar kofin shan ruwa, abun yanke farce, ma gogin baka (brush).
Idan yazama cutar ta kai marhala na karshe ma`ana AIDS (acquired immunodeficiency syndrome) ba`a kamuwa da ita ta hanyar sunbata (kissing), cin abici tare da me dauke da ita, amfani da kayayyakin ko abubuwa da me dauke da ita ke anfani da su kamar kayan sawa, wayan salula, agogo, wanka a swimming pool, zama a kujera, cizon sauro, ma taci (comb), tawul, da kuma tafiya, hada hanu, zama,da yin aiki tare da me dauke da cutar”
Tun da Dr Fatima ta fara bayaninta Rashida take karanta abunda take aiko mata, sai da ta kai nan sannan Rashida ta aika mata da wata tambayar.
“Amman Dr ya alamomin cutar yake?”
Ta samu minti biyar zuwa shida kamin tayi ma Rashida reply
“Alamomin ita wan nan cuta ta banbanta daga mutun zuwa mutum. Mutane biyu kan iya kamuwa a lokaci guda amma ba lallai sun nuna alamomin iri day aba. Anan zamu raba alamomin kamar kasha uku muyi bayani akai.
(acute illness)
(asymptomatic period)
(advanced infection)
Acute illness
(acute illness) ma`ana alamomin farko na kamuwa da ita wannan cuta. Kashi tamanin cikin dari 80% dake dauke da cutar na farawa da jin kamar alamomin mura (flu-like) dake kai tsawon sati biyu zuwa hudu rukunin farko. Abubuwan dake faruwa a wannan rukuni sune:
Kuraje kana na a jiki (body rash)
Zazzabi (fever)
Boshewar makokoro (sore throat)
Jin gajiya (fatique)
Kumburi a (lymph nodes)
Fashewar baki da alaura (mouth and genital ulcers)
Chiwon nama (muscles pain)
Ciwon gabobi (join pain)
Amai da hamami (nausea and vomiting)
Zufa cikin dare (night sweat)
Wa yan nan alamomin na faruwa mutum ya gaggauta zuwa kuji don gane yana dauke da ita bai dauke da ita.
Asymptomatic period
(asymptomatic period) ma`ana lokachin bacewar alamomi. A wannan lokaci cutar bata nuna ko wace alama na rashin lafiya ko ciwo na wasu watanni ko shekara. Amma akwai kwayar cutar a jikin mutum. A wannan lokacin kwayar cutar na dada yaduwa (replicating) da kuma kashe garkuwar jiki (immune system). Sannan a wann lokaci kwayar cutar tafi karfi da kuma yadu ta hayoyin da mukayi bayani a yadda ake kamuwa da cutar.
Advanced infection
(Advanced infection) a wannan lokachi kwayar cutar ta riga tayi damejin garkuwar jiki (immune system) yana daukan lokachi amma idan ya kai wannan lokachi to cutar ta kan zama AIDS (acquired immunodeficiency syndrome) mutum kan kamu da wasu cututtuka sakamakon damejin garkuwar jiki (immune system damage) zaizama garkuwar jiki bai iya yaki da kwayar cuta. Alamomin wannan bangare sune:
Hamami
Amai
Gudawa
Ma tsanachin gajiya
Raguwar nauyi /rama
Tari da numfashi sama sama
Zazzabi me tsanani akai akai (recurring fever)
Kwararraji masu ruwa a baki ko hanchi ko a fata da kuma alaura,
bushewar makokoro
kunburin lymph node na gabobi mara warkewa.
Kidimewa, tabuwar kwakwalwa daga nan kuma watakil sai mutuwa”
Hankalin Rashida ya tashi sosai wasu daga cikin abubuwan da Likitar ta faɗa duk tana jinsu, amman tayi tunanin ko cikine a lokacin. Ji take kamar ace ba da gaske bane
“Amman Dr Bayan wannan babu wata alama da mutum zai iya gano tabbacin yana ɗauke da cutar?”
Ko da ta tura mata saƙon ta riga ta sauka online, a lokacin 10:23pm ne. Kasa natsuwa tayi har sai da ta lalobu number Dr Fatima ta sake kiranta.
“Dr kina min bayan sai kika sauka”
“Eh Wallahi mai gida ne ya shigo”
“Dan Allah ki taimaka ki ƙarasa min, gobe zata rubuta abun yanzu haka duk ta dame ni”
“Okay bari ya gama cin abinci zan hau online”
Daga haka ta kashe wayar tana tunanin nata mijin. Whatsapp ta shiga tana duba last seen ɗinsa, ta ga biyar da kwata na yamman nan. Dp shi take kallo wani hoto ne ya ɗora yana sanye da kayan likitoci yana murmushi. Fashewa tayi da kuka ta rumgume wayar a ƙirjinta.
Sai da tayi kukanta ta gaji sannan ta ɗago wayar ta sake kallon hotonsa tayi masa kiss sannan ta shiga chat ɗin su da Dr Fatima, ashe ma tuni ta turo mata da bayanin bata gani ba.
“Ana gano mutum na dauke da wannan cutar ta tsida ta hayar gwajin jini, (serum), miyau, ko fitsari ta hanyar sanya musu wasu sinadarai dake sanya a gano kwayar cutar aciki wato HIV (human immunodeficiency virus) wadda ita take haddasa AIDS (acquired immunodeficiency syndrome) wanda mukayi bayani a sama. Anfi gano mutum na dauke da cutar ta hanyar gwajin jini”
Ta haɗeye yawu ya fi sau biyar sannan ta sake aika mata da wata tambaya, wace ita ce dalilin tambayarta tun farko.
“Dr ya mutum zai kare kansa ko kuma wani nasa daga kamuwa da wannan cutar?”
“Yin gwaji don sanin akwi ko babu.
Rage yawan saduwa.
Anfani da roba (condom) wajen saduwa.
Kiyaye saduwa da mata/maza daban daban.
Gwaji da kuma maganche cututtukan saduwa STDs (sexual transmitted disease).
Kiyaye yin amfani da allurar da wani yayi anfani da ita.
Tabayar likita dangane shan PrEP (pre-exposure prophylaxis) shima wani hanya ne na kiyaye kamuwa da ita wannan cutar
Rashin kiyaye ita wanan cuta kan sa mutum ya halaka da wuri. Ana kiyaye cutar ta hanyar yin anfani da (antiretroviral drugs) magunguna ne da ake afani dasu wajen magance cututtukan virus, kusan ita wanna cuta bata da maganin warkewa sai kiyaye ta, ta hanyar anfani da magunguna da likitan ya dorashi mutum akai”
“Na gode sosai likita Allah ya saka da alheri”
“Ba a son mai cutar yana kusantar hayaƙi, ko cizon sauro ko wani abu makamancin wannan, saboda abu kaɗan yana iya ƙara cutar, an fi mai cutar ya ci abubuwan gina jiki like vegetables”
“Thank you”
Rashida ta rubuta daga ƙarshe, sannan ta kashe wayarta tana hawaye.
“Dole ne naje nayi gwaji dan na tabbatar, wata ƙila ma na ɗauke da cutar, ai za a iya min sheri tun da ba a son zamana da Hilal”
Ta faɗa a fili tana share hawayenta. Sai kuma zancen da Asmee ta faɗa mata ya dawo mata na zargin kanta da take tana ɗauke da cutar, ita kuma ta san tana mu'amala da mijin Asmee. Jefar da fillon dake saman gadon tayi ta wani irin matsa gashin kanta.
Haka ta kwana har safe tana kuka idonta ya kumbura sosai kamar an zuba mata wani abu a ciki, bata fita ɗakinta ba, abincin da Momy ta kawo mata bata ci ba, sai kawai ta shiga banɗaki tayi wanka ta saka abaya, ta fito falo, ba dan tana jin ƙarfin jiki ba, sai dan tafitar ta zame mata kamar dole ne.
Momy na ganinta ta cika da mamakin ganin ta fito da shirin fita.
“Ina zaki je?”
“Ina son na ɗan fita ne, zan je office na ɗauki hutu sai na je gidan Asmee”
“Haba Rashida yanzu cikin wannan yanayin zaki fita sai kace wanda bata son kanta?”
Idonta ya cika da ƙwallah
“Momy ina son fitar ne ko zan samu gwarin jiki, kuma na sha iska, ko damuwa zai rage min”
“Kuma Sisters naki duk sun tafi school balle su raka ki, zaki iya driving ma”
“Zan iya”
“Shiga ɗaki ki ɗauka keys ɗina”
Momy ta faɗa cike da tausayawa. Ɗakin Momy ta shiga ta ɗauki makullin motarta, dan ita yanzu komai nata yana can gidan Hilal babu abunda aka ɗauko.
Cikin ƙarfin hali take driving ɗin, kamin ta ƙarasa office ɗin ta tsaya gefen titi tayi parking, ta kira number Malamin nan. Bayan sun gaisa ta koro masa da bayaninta.
“Malam aiki nake son ka min akan kishiryata”
“Me kike son a mata a kashe ta ko a haukatata?”
“Bana son a mata ko ɗaya, wani daban nake son ka mata wanda mijina zai gaji da ita ya rabu da ita sai ka min wanda zai dawo gare ni, a halin yanzu mijina ya rabu da ni”
“Me kika masa? Ina labarin waɗancan mutanen dana haɗa ku da su?”
“Ba mu yi aikin ba, saboda auren ya riga ya mutu, kuma wallahi ina son miji zan iya mutuwa idan babu shi a kusa da ni”
Ta faɗa cikin wani irin kuka, kamar ance mata malamin yana gabanta ne.
“Ya isa daina kuka, ai wannan mai sauƙi ne, akwai aikin da zamu masa ya dawo gunki da gudu ma, ita kuma za mu sakar mata jini sannan mu saka mata warin jaɓa idan ya gaji da ita zai sake ta, amman zaki kashi kuɗi”
“Kuɗi ba matsala bane zan baka ko nawa kake so, amman ina son a buga min ƙasa a bincika min komai nawa”
“Zan miki haka, duk abunda ƙasa ta faɗi zan faɗa miki idan kin zo, amman idan kin shirya aikin ki zo da tulo da zanen haila wanda ita kishiyarki take amfani da shi”
“Malam ya za'ayi na same shi yanzu, bayan bana gida kuma ai kasan yanzu ba'a amfani da irin wannan abun yanzu duk pad ne ake sawa”
“Pad ɗin shima ai zai yi, ki bincika a bolar gidan, idan kuma ba zaki iya ba, kisa zo ki biya kuɗi mu zamu sa aljani ya ɗauko mana”
“Zan zo nan da kwana biyu, na gode”
Daga haka ta kashe wayar ta ɗora kanta saman sitarin motar, kamin ta ɗago ta cigaba da tuƙin.
Wata pravate hospital ta nufa dan yi gwajin jinin so that ta tabbatar da zarginta.
AMIRA POV.
Har suka sauka garin Abuja bata wani farinciki musamman data ga hoton wanda ake son su kashe ɗin, sai duk jikinta ta mutu, ta tabbatar mutumen ƙwarai ne dan in ba haka ba babu abunda zaisa wasu su nemi a kasheshi.
Mutumen data taɓa gani a tv she can't recall his name, amman dai tasan shine wanda aka taɓa tattauna da ashi akan tsaro har ta ji ya kwanta mata a rai.
“Guy please karku taɓa mutumen nan”
Hancinsa yasa yana gogawa a kumatunta.
“Ina son ki sosai Amira, amman akan aikina zan iya ɓatawa da ke, so ki daina sa baki a kan aikina”
Ya ciro wayarsa dake aljihu ya kara akunne
“Hello ....Okay”
Ya kashe wayar yana kallonta
“Wai ya fita, zo muje”
“Tun yanzu za ku kashe shi?”
“A'a zamu fara farautarsa ne, yana Sahaba Restaurant, akwai yara dana aje Sahaba Hotel, kisa da inda yake, nima kuma can zanje amman sai gobe”
Ajiyar zuciya ta sauke ta janye hannunta daga riƙon da yayi mata.
“Ba zan je ba ku tafi kawai”
Duƙawo yayi ya mata kiss, sannan ya fice.
Ji take bata da natsuwa idan bata faɗawa masa abunda yake faruwa ba, sai dai kuma taya zata faɗa masa bayan shi ɗin babban mutum ne ganinsa ba hakan ake yi ba. Kuma idan har ta aikata ta jefa rayuwarta cikin matsala.
Sai da ta ji tashin motarsu sannan ta tashi ta shiga binciken gidan, har ta samo paper da pen tayi rubutu akai sai ta sanya doguwar riga dan jikinta inner ne kawai ta fito harabar gidan tana dubi-dubi.
Har tayi tunanin ta hau Napep sai kuma ta tuna Abuja ba ko ina ake farin Napep na shiga ba, sai kawai ta koma ciki ta tashi ɗaya daga cikin yaransa ta ce ya kai ta, yaso ya musa mata amman sanin halinta da kuma yadda Guy ke ji da ita yasa dole yaja mota ta shiga suka kama hanya.
Suna isa Sahaba Restaurant, sai ta hango Sahaba Hotel kamar yadda Guy ya faɗa mata. Nesa da gurin tasa ya aje ta tace ya tafi ya barta zata je gurin Guy, ba musu yaja motar ya koma. Sai da ta daina hangosa sannan ta nufi Sahaba Restaurant zuciyarta cike da tsoro gabanta kuma kar ma zai zube ƙasa.
Guy na daga gefe ya hango Amira ta doshi Restaurant ɗin sai waje-waje take.
“What the fuck, me Amira za tayi can ? Ko ta ɗauka ina can ne?”
Ya tambaya yana kallon yaransa da suke tare da shi cikin motar, wanda ko wannensu ba shi da amsar ba shi. Da sauri ya buɗe motar ya tara hannayensa a baki yana mata fiito (shewa) irin na tsuntsaye. Amira na jin kira ta san Guy son ne, maimakon ya ga ta dawo sai kawai ta ranta cikin na kare.
ABDOOL POV.
Ganin kurciyar ta firanye sai kawai yayi musu alama da hannu akan su koma kawai. Shi kuma ya koma cikin gidan, ya kunna tv yana kallon news, lokaci zuwa lokaci yake jan tsaki saboda lamarin nijeria kullum abu yaƙi ci yaƙi cinyewa, yau wannan kakeji gobe wani kala ne. Idan ma kace zaka maida hankali akan abun sai tunani yayi maka yawa.
Wuni yayi a cikin sallah ce kawai take fitar da shi gidan, sai da dare ya sauya kayan jikinsa ya fita siyen abinci dan be yarda a dafa masa a abinci duk kuwa da kasancewar akwai masu masa dafa masa, amman baya ci sai dai sauran ƴan gida su ci. Ko a gurin siyen abincin ba guri ɗaya yake tsayawa ba, saboda tsaro.
Bayan ya karɓi takeaway ɗin ya biya sai ya juyo ya nufi ƙofar fita. Yana fitowa ya hango budurwa tana gudu iya ƙarfinta ta doso inda yake, kallon mamaki yake mata yana son tantance abunda take ma gudun.
Sauran taku kaɗan ta ƙaraso inda yake, sai ƙarar bindiga ya tashi, cikin wani irin zafin nama ya riƙota dan ya gane ita aka harba, sai dai haka be hana bindigar samunta, sai ta sulale a hannunsa tana banƙarar bayanta saboda zafi da kuma dafin albarushin da taji ya soke ta abaya.
Daga shi har ita tare suka kai ƙasa, cikin hanzari ya ciro wayarsa ya kira yaransa. Sannan ya kira head quarters.
*🌺🌺 ZAGON ƘASA 🌺🌺*
*© Khadeeja Candy*
Don't read if you didn't pay...!
*PAGE - 44*
NOT EDITED ⚠
_An kaiwa Major General Abdullah Ahmad Mai-doki hari_
_An yi nasarar kashe waɗanda suka kaiwa Major hari_
_Yarima Abdullahi Ahmad Mai-doki Ɗan sarkin Katsina ya tsallake rijiya da baya_
_Wata yarinya ta sadaukar da ranta saboda ɗan Sarki_
Shine abunda kowa wace jaridar Nigera ta online ta yi ado dashi a fuskarta shafinta, har ma da na ƙasashen waje, bayan mintuna 25 da faruwar lamarin.
Online rumors updated kuma kowa da abunda yake rubutawa, har da masu cewa har shi an harba da masu cewa ma ya mutu, da masu cewa yaje siyen abinci da karuwarsa, wasu kuma matarsa ko dai da irin yadda tayi masa daɗi yake ƙaƙarowa ya rubuta a social media.
Dandazo ƴan jarida suka yi a bakin asibitin da aka kai Amira,