Showing 231001 words to 234000 words out of 281103 words

Chapter 78 - ZAGON KASA Book Complete Document by Khadeeja Candy .txt

28 Dec 2024

61282

POV.


Duniya juyi-juyi a yayinda ake kuka mutuwar Mama, ta ɓangaren Namra murna ce ta cika gida ko ina sai guɗa kake ji ana yi, da kiɗin ƙwarya dan yau aka saka mare lalle, wato Maryam da Hindatu.


A cikin gidan aka yi sa salle ba kamar yadda wasu suke ba a ɗauka a kai wani guri inda ƴan'uwa. Yanzu ne wasu ƴan'uwan suke zuwa na garuruwa da kuma na cikin gati dan jiƙon lalle. Ƙarfe goma na safe aka saka jiƙon lalle wato ceremonial setting.
Amman ko da 9am ta yi gidan ya cika da jama'a abun da mai jama'ah, ba daga ɓangaren Abbah ba bana Anty Amarya ba, da kuma na Hajiya Barau, har mutane ƙauye sun iso. Goma dai-dai ƴan gidan angaye suka zo jiƙon lalle, yadda aka riƙa faka motoci a bakin gate ɗin gidan har aka rasa gurin aje wasu. Mutane sai mamakin ganin Namra suke da su a idonta suna mata kallon ta lalace ta yi baƙi, ita ko tana ganin har ta ɗan yi ƙuba a zaman nan na kwana biyu da ta yi a gida. Duka abubuwan da aka raba a gurin sa lallen daga ɓangaren Abbah ne aka kawo, wato gwaggwanin amare. Misalin huɗu na yamma aka yi wanki amare a gidan sama road gidan Alhaji Salisu Yayan Abbah amman wanda suke ƴan wa da ƴan ƙane (Cousin). An yi watsin kuɗi kamar ba gobe, bama kamar Hajiya Barau yadda ta zage tana watsin kuɗi sai ka rantse da Allah har a zuciyarta farincikin auren take, bayan kuwa ta ciki na ciki.


An raba abubuwa da dama a gurin bikin, bayan an raba abubuwan da al'ada ta tanada (Al'adar sokoto) wato raba kayan mata (Hakin maye) a gurin awankin amarya, sannan a ɗora ta su lalle da salatif da tsinke da ƙwarya da sauran kayanyakin aiki mata, daga bisani aka biyo da kayan ciye-ciye da na tanɗe-tanɗe.


Daman can tun kamin ka shigo gate sai an miƙa maka ledar takeaway, drinks kuwa sai wanda ranka yake so zaka ɗauka, bayan wanda zaka tarar a muhalin da zaka zauna tare da kayan tanɗe-tanɗe.






ASIM POV.


Haka ya koma kamar marar lafiya, sallah ma daker yake unƙurawa ya tashi ya yi, ya rufe wayoyinsa gaba ɗaya. Mutane sai gaisuwa suke masa. Bayan isha'i mutane sun fara laɓawa, ya koma cikin motarsa ya zauna sannan ya kunna wayarsa, yana haska cikin motar sai Apple ɗin yake nema, sai a lokacin ya tuna da wayoyinsa da suke cikin motar, da sauri ya fita motar wayarsa na ringing. Hajiya Sadiya ce take kiransa, sai ya koma can gefe inda babu mutane ya natsu ya amsa wayar.


“Asim ina ta kiran ka tun jiya baka ɗaga ba, ɗazu kuma na kira wayarka a kashe”


“Bana kusa ne”


Ya amsa mata cikin rashin daɗin rai dan zuciyarsa sak yanzu zarginta yake.


“Ina Apple ɗin da kace zaka bawa matarka? Wata ka bawa ne ko mi ya faru? Ni an kira ni sai faɗa suke min, wai an basu tsohuwa, ni kuma na san ba wannan maganar muka yi da kai ba, miya faru ne”


“Apple ɗin faɗuwa yayi a hanya ina da niyar kiranki na faɗa miki, maybe wata ta tsinceta ne”


“Amman Asim sai da na yi ta nanata maka kar a samu matsala yanzu gashi wata banzar tsohowa taje ta samu, garin yaya ma ka jefar da shi? Ko dai baka son kuɗin ne wai?”


“Ina so mana, ai yanzu akwai wani ko?”


“Eh amman sai naje na faɗa musu sai su ban wani, yaushe zaka zo?”




“Nan da kwana biyu”


“Zan je na ƙarɓo maka, amman dan Allah karka min sakakace irin wacan”


“Ba za a samu matsala ba wannan karon sai kin fi kowa farinciki”


“Haka nake so”


Ta katse kiran. Shi ko ya cige baki yana kallon wayar cike da baƙinciki. Yana son ya tambayi Ƙanwarsa yadda aka yi apple ɗin ya fito daga motarsa har Mama ta ci yana tsoron kar ta zargi wani abu.


“Kun samu sa'ar jinin Uwata... Wallahi kin yi nadamar sanina da kika yi a rayuwarki, sai na ɗanɗana miki wannan baƙincikin”


Yayi wulgi da wayar iya ƙarfinsa, yana huci.




UZAIR POV.


Tare da ƙannensa biyu suka iso gidan da kuma mahaifiyarsa, tana ganin irin halin da yake ciki suka ɗauki shi zuwa asibiti.
Emergency suka wuce da shi layin ƴan haɗari aka ware masa ɗaki daban likitoci suka hau duba shi, sai ihu yake kamar wanda be san inda yake ba, bayan sun yi ɗan bincike su aka tura shi gurin hoto, bayan an masa hoton suka sake dawowa da shi ɗakin suka masa allurar bachi, amman kamar an ƙara masa zafin ciwo yake ji gaba ɗaya ya fita hayyacinsa sai ihu yake. A take suka sake rubuta masa wani hoton, aka je aka ɗauka.


Lokacin da aka fito da hoton, sai Likita ya kira Hajiya suka nufi wani ɗakin da ita sai ya ƙala hotunan a jikin computer. Yana nuna mata.


“Ɗan ki ya taɓa yin haɗari?”


“Gaskiya be taɓa ba, amman ban sani ba ko be faɗa min ba”


“Gaskiya ƙashinsa na baya na karye, kuma na cinyarsa ma ya karye, sannan....”


Kamin ya ƙarasa ta miƙe tsaye ta sauri har kujerar da take zaune samanta ta faɗi.


“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”


Ganin hakan yasa likitan dakatar da bayaninta, dan ya ga alamun zata fara masa kuka, shi kansa yasan be kamata ya yi mata wannan bayanin ba, ganin tana mace amman babu yadda ya iya tun da babu wani namiji babban da yayi kusa da mahaifiyarsa. Da sauri ta juya ta fice daga office ɗin tana kiran wayar Abbah. Dan babu wanda ya san an kai Uzair Asibiti dan basu faɗa ba, tun bayan da Yasmin ta daqo gida ba ta damu da tasan dalili ba, tana ganin kamar yayi hakan ne saboda ta janye ƙudirinta.




HILAL POV.


“Miya same ƴar ka haka ne Doc?”


Doc Zara ta tambaya cike da mamakin irin ƙunar da Ulfah ta yi. Hannayensa ya zuba aljihu yana sauke ajiyar zuciya, ita kan Teema tuni ta kusa cikin ɗakin tana hawaye kamar gaske.


“Faɗa suka yi da ƴar'uwarta shi ne wai ta watsa mata ruwan miya dake kan wuta”


“Amman gaskiya ya kamata ka sa ido sosai akan yaranka Uzair, irin wannan abun yana sa kisan kai fa”


“Ƙaddarori ne kawai idan Allah ya kawo abu”


“Allah ya tsare gaba, Ina uwargida har yanzu bata haihu ba?”


“Har yanzu fa”


“To Allah ya raba lafiya”


“Amin”


Tun da suka jero suke maganar basu rabu ba sai da ta kawo kusa da pharmacy sannan ta ɗauki wata hanyar shi kuma ya ciro wayarsa ya kira Hajiya ya faɗa mata, ita Rashida text kawai ya aika mata, sai kuma ya kama hanyar gida dan yi ma Ezzah hukunci.
Sai da ya kama hanyar gida sannan ya kira Kalsoom ya faɗa mata halin da ake ciki, dan yasan zata tashi hankalinta sosai.


Bugu ɗaya ta ɗauka.


“Kana ina ne?”


“Ina hanyar gida, na kaita asibiti da sauƙi”


“Na je gida ban samu kowa ba sai Ezzah tana ta kuka, sai ta biyo ni gani cikin asibitin ma”


“Oooooo Kalsoom miyasa baki ragawa kan ki ne? Ba fa ke kaɗai kike ba a yanzu, da izinin wa kika fita, yanzu da wannan tulelen ciki yama zaki yi driving?”


“Napep na hau”


Ajiyar zuciya ya sauke.


“Tau gani nan juyowa”


Ya katse kiran ya juya ya koma hanyar asibitin. Yana isa aibitin su Hajiyarsa na isa yare da Mama ladi (kanwar mahaifiyarsa) da ƙanensa guda biyu. Jerowa suka yi suna tafiya yana yi ma Hajiya bayanin yadda abun ya faru.


Kalsoom na hango shi tafe tare da Hajiya ta ji babu daɗi musamman dan tana tare da Ezzah tasan dole Hajiya za tayi magana wata ƙila ma zata ce ita ce ta haddasa wannan husumar. Duk sai ta rasa yadda zata yi ga tulelen cikin nan ya mata tsaye kamar wacce zata haihu yanzu.


“Hajiya ina wuni”


“Lafiya ƙalau”


Tana amsa gaisuwar da Kalsoom ta yi mata ta wuce bata ko bi ta kanta ba. Hilal ne ya tsaya gurin matarsa.


“Miya hana ki shiga?”


“Ban san ɗakin da aka kai ta ba”


“Tau muje”


“A'a sai Hajiya ta fito, kar ta gan ni da Ezzah”


“Cemin ta yi wai tana tsoron karka dake ta”


“Ai ba duka kaɗai ba karye ta ma zanyi, ba dai ke har kin kai ki ɗauki ruwan zafi ki watsawa ƴar'uwarki ba...?”


Sai kawai Ezzah tasa kuka ta kama Hijabin Kalsoom ta riƙe gamgam tana kuka. Hilal be bi ta kanta ba ya nufi sashen da zai sadashi da ɗakin Ulfah, Kalsoom ta rufa masa baya tana faɗin Ezzah ta yi shiru ba zata bari ya daketa ba.
Ko da suka shiga Hajiya na kusa da Ulfah dake bachi, tana duba ƙonuwar cike da tausayi, can jikin ƙofa Kalsoom ta tsaya tana kallon Ulfah, Ezzah na riƙe da Hijabinta har lokacin tana kuka. Hajiya ta ɗago ta kalli Ezzah cikin tausayi da ɓacin rai ta ce


“Amman Ezzah baki da zuciyar ƙwarai, ko ɗauki ruwan zafi ki watsawa ƴar'uwarki haka?”


“Wallahi ba nice ba Wallahi Mama Teema ce...!”


Ta faɗa cikin kuka.
[7/18, 8:14 PM] Khadeeja Candy♥: *82*


Teema ta katsa mata tsawa tana zare mata ido alamar dik kika faɗa sai na ci ubanki.


“Ke karki min ƙarya, munafukar yarinya fitsararriya”


“Wallahi ba ni bace, ke kika kira ni kika ce na zo naje kitchen na duba Ulfah ta ƙone...”


Hajiya ta kalli Teema ta kalli Ezzah, ƙoƙarin ɗaukar maganar ta ke, sai kawai ta jiyo kukan Teema wai Ezzah ta mata ƙazafi.


“Wallahi ba zan taɓa yafe miki ba, makira kawai munafuka”


“Ezzah kike cewa haka? Sai kace wata babbar mace? To wai kina aikin me haka ya faru”


Cewar Hajiya tana sake da baki. Ta soma bayani tana kuka da kallon Hilal ko zai kareta ɗin nan.


“Ina cikin kitchen ina girki, na ƙare tuwo sai na ce bari na ɗora miya, sai na ce ta daga kamin daddawa ita kuma Ulfah ta gyara min tabarnuwa, ni ban san gardamar mi suke ba sai kawai naji an taɓa tukuyan miyar da ƙarfi sai ihun Ulfah na ji ina juyowa na ga ta juye mata miyar”


Izzah ta tuma ta dire ta sake tuma ta dire tana kuka da jan Hijabin Kalsoom tana faɗin ba ita ba ce, amman babu wanda ya kula ta Hilal in banda harara babu abunda yake mata, yana cike da haushinta sosai Allah ka ɗai ya san irin hukunci da zai mata idan suka koma gida. Sai kawai ta saki Kalsoom ta ruga gurin Hajiya tana kuka.


“Wallahi ba ni bace Hajiya...”


“Hilal ka saurareta mana”


Kalsoom ta faɗa cike da tausayin kukan da Izzah take yi.
Hilal ya girgiza mata kai.


“Ba wani saurare da za'a mata, ai kin san halinta”


Izzah har da faɗuwa take a gurin taɓa tashi ta kama gyalen Hajiya ta riƙe ƙam.


“Ba zaki rufewa mutane ba ki ba, Wallahi zan dake ki yanzu nan, ba sai mun je gida ba”


Hilal ya faɗa ciki fushi yana mai jin kamar ya kamata ya ɓallata gida biyu. Ihunta ne ya tashi Ulfah daman can ba wani dogon bachi ta yi ba, saboda zafin wuta ko an maka allurar ba bari yake ka yi bachi ba.


“Wayyo Allah Momie, Hajiya, Dady ka kai ni inda Momie ko Anty Kalsoom ko inda Hajiya, bana son gurin Mama Teema ta watsa min wuta, wayyo zafi dady zafi Mama Teema ta ƙona ni, Anty Kalsoom, Momie, Hajiya”


Sune ƙawai sabbatun da take tana murza jikinta sai da Hilal ya riƙe mata hannu. Suna haka sai ga Rashida ta shigo hankalinta a tashe, tana kallon Teema hawaye suka fara mata zuba.


“Ɗaya bayan ɗaya za ki bisu ki kashe, na sani Teema kaɗan daga halinki ne amman ki sani kin ci amana kuma kema amana sai ta ci ki”


Sai kuma ta juyo gurin Kalsoom tana kuka, itana Kalsoom ɗin kuka take, Hajiya ma haka, balle Teema dake ƙoƙarin kare kanta, ƙanen Hilal ma babu wanda baya hawaye.


“Kin ci amanata, sai da na ce miki ki riƙe min yara na amman kika ƙi, yanzu ga shi abunda ya faru, bana da kowa a duniyar nan sai su, su ne farinciki na”


Jakar da ke hannunta ta saki ta nufi gurin ƴarta dake sabbatu, magangun ɗazu kawai take maimaitawa. Rashida ta gadon ta riƙe tana kuka.


“Laifina ne, nice ban riƙe mutuncin aurena ba, ni na kasa zama da ku ni na cuceku Ulfah laifi na, kuma na ci amanar matar da ke riƙon ku tsakani da Allah...”


Ezza ta yi gunta da kuka.


“Momie Wallahi ba ni bace, Dady ya ce sai ya raba ni gida biyu.. Wallahi ba ni ba ce”


“Ba zan ɗauka ba, wannan ba zata kwanta jinya ba, ka kama wannan ka karya min ba, ka saurareta Hilal Wallahi ba ita ba ce, karka ɗauki alhakin yarinyar nan Hilal”


Cikin kuka Rashida take maganar gwanin ban tausayi. Hajiya ta share hawayenta tana kallon Ezzah.


“Miya faru faɗa mana”


Ras Ezzah ta zana musu abunda ya faru, duk wani tsoro na teema yau baya tare da ita, tun da ta ji zancen Hilal yace zai raba ta biyu. Duk suka cika da mamaki sai kawai Teema ta ƙara rushewa da kuka, Hajiya ta girgiza kai tana faɗin.


“Amman Fatima kin ban mamaki, kw da ake yabo da salla?”


Hilal yayi saurin ɗaga mata hannu.


“Hajiya dan Allah kar ayi maganar nan a nan, asibiti muke, kullum sai ace nine family na cikin matsala”


“Kai dalla gafara can, kai har yanzu baka san ciwon kanka ba akan ƴaƴanka, ko wace mace ka aura da irin azabar da take gwadawa ƴaƴanka, Kalsoom ta kashe Rafiq wannan kuma tana ƙoƙarin kashe Ulfah wannan wane irin masifa ce”


Rashida ta kalli Hajiya tana hawaye.


“Wallahi ba Kalsoom ba ce ta kashe shi, Wallahi nice ni na kashe ɗana da kai na...”


Sai duk kallo ya koma kan Rashida har Kalsoom ɗin kallonta take. Hajiya tasa wani dogon numfashi ta sauke ta ce


“Muje gida mu yi wannan maganar, Hilal muje gidanka a yi wannan maganar, Ke ki tsaya nan ki kula da Ulfah”


Ta faɗa tana kallon ɗaya daga cikin ƙanensa, sai kawai ta nufi ƙofar fita tare da tawagarta. Rashida ma fita tayi ta rufa musu baya dan ta shirya fasa ƙwan yau kam, bata san gidan Teema ba dan haka ta nufi tsohon gidanta kuma gidan Hilal inda Kalsoom take zaune. Hilal kan sai ya bawa ƴarsa magani tare da allura ta koma bachi sannan ya sako matansa gaba suka kama hanyar gida. Ko da suka shiga falon Hajiya na zaune falon tana jiransu, Ezza kuma na riƙe da Hijabin Kalsoom kamin ta saketa ta nufi gurin uwarta da gudu.


“Maimata abunda kika faɗa ɗazu ko kina da wata shaida”


Cewar Hajiya tana kallonta. Rashida ta girgiza kai.


“Bana da wata shaida sai Allah da kuma Teema, amman Wallahi Kalsoom bata da hannu a mutuwar Rafiq, ni naja komai”


“Kamar ya ki fito ki yi bayani mana”


Hilal ya katsa mata tsawa, Teema ta yi saurin saka baki.


“Karki ci amanata Rashida ni ban san komai akan ɗan ki ba”


Rashida bata kulata ba, ta soma koro da bayani.


“Bayan da Hilal ya sake ni, sai na riƙa zagaya makarantar su Ezzaha ina zana mata irin makirci da rashin kunyar da zata yi ma Kalsoom, ina tunani kamar idan ta yi hakan zai tausaya musu ya dawo da ni, da naga hakan be samu ba, sai na koma bin bokaye, ina neman yadda za ayi Kalsoom ta bar gidan Hilal kuma ya dawo gareni, naje wanu gurin aka mata magani aka sako mata jini, cikin dake jikinta ya kwanta ya ɓace bat, na sake komawa na yi mata wani a wannan karon be faɗa kanta ba, ya faɗa kan ɗa na Rafiq, ni kai na ban san ya faɗa kansa ba, har sai da naje na kaiwa Teema kukana ta kaini gurin wani malami shi ya faɗa min cewar na yi magani ma kishiyata ya faɗa kan ɗa na, shiyasa a asibiti aka rasa gane kan wannan matsalar sai ya nuna guba ne sai kuma ya nuna gas ne, ba komai ba ne sai sihiri. Duk wani shige-shige da nake na magani tare da Teema nake yinsa, ta kai ni gurare da dama, saboda ta fini sanin bokaye, nayi mamakin da aka ce Hilal zai aureta saboda na san an gudu ba a tsira ba ne. Sai dai na ɗauki hakan a matsayin cin amanar aure da nayi na keta haddin Allah na tozarta aure, dole nima Allah ya tozarta ni, na ci amanarki Kalsoom na yi ta miki abubuwa ko a zaman da muka yi da ke a gidan nan, ashe ma ke ƴar'uwata ce ba kishiya ba...”


Kuka take sosai ita da Kalsoom da Teema, sai dai ko wannensu da abunda yake yi ma kuka. Kalsoom babu komai a zuciyarta sai farincikin yau Allah ya wanke ta da kuma tausayin Rashida da ƴaƴanta.


“Na yafe miki Rashida, Wallahi na yafe miki har a bada, kuma na miki alƙawarin zan kula miki da ƴaƴanki fiye da yadda ke zaki kula da su, amman idan Hajiya ta yarda”


Kalsoom ta faɗa tana kallon Hajiya data soke kai tana hawaye.


“Haƙiƙa na cutar da ke Kalsoom, na miki kurkuren fahimta, na ɗauki alhakinki, na cutar da ke matuƙa, Wallahi na ji kunyar kai na sosai”


“Haba Hajiya ai ko nice a matsayin da kike kwatankwacin abunda zan aikata kenan, saboda gaskiya ba ta bayyanaba a lokacin kuma ɗan adam da zahiri yake aiki sanin baɗini kuwa sai Allah, ni dai abunda kawai na ke so ki yarda da ni kawai”


“Wallahi na yarda da ke ɗari bisa ɗari kalsoom, kuma daga yau yaranki gurinki zasu zauna. Teema baki yi ƴa ba, kin bani mamaki, ina gani kamar na ɗauko ma ɗauka mutuniyar kirki ashe ɓara gurbi ce”


Kuka sosai Teema take ta sauka daga saman kujera ta zauna ƙasa kusa da Hajiya ta kama ƙafafunta.


“Wallahi Hajiya ƙarya take min, na miki alƙawarin zan canja daga yau, ba zan sake yin wani abu marar kyau ba”


“Nasa Hilal ya aure ki ne saboda ita tunanin ke ta ƙwaraice, Fatima ko da mun zauna da ke babu aminci a tsakanin ke da mijinki da ƴaƴansa da kuma ni, mace mai shige-shigen malamai iya mata sai Allah karki je ki yi mana irin na Rashida, kin ga ƙara a rabu tun abu be yi nisa ba, kije can Allah ya haɗa ki da rabon ki, ni kan Hilal ba dan kar na zama


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login