Showing 210001 words to 213000 words out of 281103 words

Chapter 71 - ZAGON KASA Book Complete Document by Khadeeja Candy .txt

28 Dec 2024

61291

Namra haka, da ga alamu yana ji da kansa, ko kuma be gama hucewa bane oho.


“Allah sarki Namra, ashe kuwa zamu yi marmarinki”


Uwani ta faɗa cikin rashin jidaɗi, dan har ga Allah ita tana tunanin rabuwa da Namra dan yanzu sun ɗan tsaba da juna.


“Nima ai sai na yi Marmarin ku, mutane masu karamci da sanin darajar ɗan'adam”


Namra ta furta tana mai jin kamar karta tafi ta barsu. Har bakin mota Neina da Uwani da Maryam suka rakosu, ko da suka fito har Abbah ya shiga mota, Anty Amarya ta fara shiga sannan Namra, su Neina na ɗaga musu hannu direban yaja mota.




RASHIDA POV.


Ta rame sosai ta koma kamar ba ita ba, tun ranar da taje gidansu su Teema bata sake leƙa ko ina ba, gurin aikinta sun yi kira sai ta tura musu saƙon bata da lafiya ta email, sannan ta kashe wayarta, saboda yawan kiran da ake mata akan auren Teema da tsohon mijinta. Bata iya cin komai banda tea, sai ɗan lemu wani lokacin, kullum a kwance take salla ce kawai take tashinta. Musamman jiya ta san itace ranar ɗaurin auren Teema da rabin ranta 😢. Babu wanda yasan inda take balle azo gurinta, Momi kuma ta juya mata baya da duk ƴan gidansu, lallai sai yanzu ta gane duniya ta juya mata baya, shiyasa ake cewa idan kana son duniya da yawa ka fara barinta kamin ta barka, idan har ita ta fara barinka to ba zaka ga da kyau ba. Yanzu kan ta fara gane baƙin duhun da yake bibiyarta sai dai bata san iya inda zai tsaya mata ba. knocked ɗin ƙofar falo da taji ana yi ne yasa ta unƙurin tashi taje ta buɗe. A zatonta Momi ce ko wata daga cikin ƴan gidansu, ga mamakinta sai ta ga Asmee.


“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. Rashida haka kika koma?”


Rashida ta sakar mata ƙofar ta dawoɓsaman cushion ta zauna, Asmee ma zama tayi a kujerar dake fuskarta ta Rashida, tana yayw mayafinta.


“Haba Rashida, na san kina son Hilal kuma na san Teema bata kyauta miki ba, amman idan ta samu labarin halin da kika shiga ai daɗi zata ji, kin ware kanki ke kaɗai kina saka damuwa a aranki”


“Ya akayi kika gane gidan nan?”


“Gidanku naje aka kwatantamin nan, zulfa'u da Rafia duk sun je gida sai a ce musu kin yi tafiya, nima ban da na matsa da ba za a faɗa min inda kike ba, dan Allah Rashida ki cire damuwar Teema a ranki”


“Ba auren Teema abunda yake damuna a yanzu ba, irin rayuwar da zata shimfiɗa a cikin gidana yafi damuna, ita zata reni ƴaƴana, kuma wallahi azzalumace zata iya yi musu komai, gata ta iya neman magani zaya iya raba su da ubansu”


“Toh ya zakiyi Wallahi Teema ta ci amana”


“Teema ta ci amana kamar yadda nima na ci amana, ta auren min miji kamar yadda nima nayi taraiya da mijin aminiyata, Asmee duk halin dana shiga a yanzu mijin ki ne sila...”


Asmee ta gyara zama.


“Ban gane ba. Kamar ya mijina ne sila?”


“Kin ci amanar mijinki kin bada kanki ga wasu saboda neman mallakar miji, ahi kuma ya ci amanar ki ya bada kansa gare ni, mijinki shi ya saka min cutar hiv, saboda kin samo gurin wannan bokan kin saka masa, tun daga lokacin da naji kince ana zargin bokan da cuta, hankalina ya tashi saboda nasan bayan mijina, mijinki ne na biyu da nake mu'amala da shi, sanadin hakan naje nayi gwaji, aka tabbatar min da ina ɗauke da cutar, har Hilal ya gane gaskiya yaje yayi gwaji shi baya da shi da ƴaƴansa, da matarsa, sanadin hakan ya sake ni, shi kansa mijinki be san da hakan ba, amman ke nasan kin san kina ɗauke da cutar, saboda haka na ci amana, nima Teena ta ci amanata, sai dai ban san makomar yarana ba, ban san wane irin tarbiya zata basu ba”


Miƙewa Asmee ta yi tsaye gume na keto mata tashin hankali ya hana hawayen dake maƙale a idonta zuba.


“Duk yarda da Amincin dake tsanina da ke, ace kin rumtse ido ta auren ki kin yi zaman banza da mijina? Ina tunanin nayi abunda zan iya na hanasa aure, ashe na kashe macijina ban tsare kan ba, wallahi ko a mafarki ban za ci zaki min haka ba, ƴar iska macuciya, ai wallahi sai kin ga abun ki, dan Teema sai ta salwantar da rayuwar ƴaƴanki... Kuma Allah ya isa tsakanina da ke!”


Ta fisgi gyalenta ta fice a fusace. Rashida kan kuka kawai take, tana mai jin tsantsar damuwa da nadama a zuciyarta. Kuka tayi sosai, daman kullum cikin yinsa take, sannan ta koma ɗakinta ta ɗauki kkaton hijab ta saka ta saka niƙab ta ɗauki makullun motar ta ta fice.






ABDOOL POV.


Tun da ya baro ƙofar gidansu Lamido cikin farinciki yake, dan yasan sahibarsa ma tana can tana farinciki, kuma yasan zai samu ladar sulhunta uwa da ƴarta, horn ɗaya yayi aka buɗe masa gate, cikin nishaɗi yayi fakin motarsa ya fito da murmushi kamar wanda aka yi ma albishir.
What he saw a bakin ƙofar shiga part ɗinsa was surprise him, kurciyar daya gani a abuja itace a nan? Haske ne ta ko ina a gidan kamar rana, hakan ya bashi damar ganin layan dake wuyanta.


“Umar...”


Ya ƙwalawa Mai kula.da gidan kira, sai ga shi da gudu yana amsa kiran da yake masa. Keys ɗinsa ya miƙa masa.


“Zagaya ta baya ka buɗe ƙofar nan a hankali, kurciyarta nake son ta shiga ciki mu kamata”


“Ranka ya daɗe ai za'a iya halbeta da danƙo”


“Kana da danƙon ne? Kasan yadda zaka halbeta bata tashi ba?”


“Eh za a iya saitawa, amman ranka ya daɗe kurciya da dare baka san me take nufi ba, balle kuma ga laya a wuyanta”


“Idan mutum yana addu'ah babu abunda zai same shi, kawai ka halbe min ita idan zaka iya”


“Toh”


Ya nufi wani part ɗin na gidan, da ɓangarensu yake a can, be ɗauki dogon lokaci ba sai ga shi ya dawo da danƙon har da duwatsunsa guda biyar. Ayatul kursiyo ya karanta sannan ya saita inda take ya harba da bismilla. Firr tayi zata tashi sai ta faɗi saboda ya same ta a ƙafa. Da sauri Abdool ya ƙarasa zai kamata sai ta sake unƙurin tashi ta kasa har ya kama ta, sai da yayi bismillah sannan ya cire layar dake wuyanta. Umar ya miƙawa kuciyar ya shiga buɗe layar. Wasu surkulle ne aka yi aka kulle da fatar baƙar akuya, sai wata farar takardar a tsayarki takardar an rubuta sunan Namra da larabci.


“Namra”


Ya maimata sunan cike da mamaki da ɗaurewar kai.


“Miya kawo sunan Namra anan? Waya aikata mata haka?”


Yayi ma kansa tambayar da bashi da amsar ta.


“Umar kasan yadda ka yi da wannan kurciyar”


Ya faɗa sannan ya shiga cikin falon da abun a hannunsa.






KALSOOM POV.


Hannu ya kai ya shafa fuskarta.


“Haba dai baki kishi ranar ɗaura aure ba sai yanzu zaki yi? Ko dai wani ne ya zuga ki?”


Kai ta girgiza masa alamar a'a, ta janye hannunsa daga fuskarta ta miƙe tsaye.


“Zan shiga wanka”


Hannunta ya riƙe.


“Kalsoom ko na miki wani abu da ba daidai bane?”


Ta saka mashi kuka.


“Baka min komai ba, kawai dai...”


miƙewa yayi tsaye ya haɗe bakinsu, yana shafa bayanta alamar rarrashi. Sun ɗauki tsowon lokaci a haka sannan ya sake ta.


“I promise you ba zan miki wani abu da xai cutar da ke ba”


Ya kwantar da kanta ƙirjinsa. Ba shi take ji ba, Amaryar tasa take ji dan bata san da me tazo mata ba, bata son ta sake shiga irin rayuwar da tayi da Rashida a baya. Sai da ya tabbatar ta samu sukuni sannan ya sake ta yana tambayar me zai siyo mata.


“Ina son zogale”


“Okay”


Yayi mata kiss, ya shafi cikinta sannan ya juya ya fice. A gurin ta tsaya har sai da ta ji tashin motarsa sannan ta shiga wankan. Tana cikin wanka taji tsayawar mota sai kuma kamar ba ta Hilal ba, hankali kwance ta yi wankanta ta ɗaura tawul ta fito. Haka kawai ta ji bata da natsuwa idan bata leƙa taga wanda ya shigo ba, dan haka tana fitowa ta zira doguwar riga ta ɗora ɗankwalin a saman kanta ta nufi falon.
Abunda ta gani ya bala'in ɗaga mata hankali Rashida ce zaune saman kujera tana kallonta, fargaba da tsoro suka tunkarota lokaci ɗaya, idonta be gama tantance Rashida ɗin bace ko waninta, dan ta lalace sosai ta rame, idan har ita ɗince mi tazo yi gurinta, ga ta cikin hijabi niƙab a hannunta.






ASIM POV.


Yana saka kuɗin sai ga kiran Hajiya Sadiya, sai da ya shiga mota sannan ya yi picking.


“Hajiya na saka kuɗin”


“To yayi kyau, ina son muyi wata magana da kai Asim mai muhimmaci”


“Okay na zo kenan?”


“A'ah ba sai ka zo ba, saboda ƴata bata riga ta tafi ba”


“Toh ya za'ayi kenan”


“Ka same ni a wacan gidan, akwai zan maka wani tayi ne kuma ina fatar ka amsa”


“Okay what time zan zo?”


“An jima da yamma”


“Okay Allah ya kai mu”


Ta kashe kiran. Kai ya girgiza yana cizon bakinsa.


“Ta tabbata Nably ƴarki ce”


Ya kunna motarsa ya bar gurin. A unguwar su Hajiya sadiya yayi sallah la'asar, 6ana hango lokacin data shiga cikin gidan. Sannan shima yaja motarsa ya shiga cikin gidan.


Yana ta sallama bata amsa masa ba sai da ta fito bedroom sannan ta amsa masa. Cikin ladabi ya gaisheta yana kallon yanayin fuskarta mai ɗauke da damuwa.
Shi ya fara zama sannan itama ta zauna tana kallonsa.


“Asim ya maganar matar ka ta dawo kuwa?”


Ya ɗan sosa kansa.


“A'ah nayi nayi taƙi dawowa, kuma yanzu ta daina ɗaukar wayata ma, gashi ba gidansu ta je ba”


“Yanzu dai babu zancen dawowar ta kenan?”


“Gaskiya babu shi, daman ni dan kin matsa ne shiyasa nake son na dawo da ita”


Ajiyar zuciya ta sauke, sannan ta kalleshi a natse ta ce.


“Asim ina son ka auri yata, kuma auren shekara ɗaya, zan baka miliyan ashiri, zan baka gurin da zaku zauna, bana buƙatar ka yi komai, zan maka lefe zan baka kuɗin sadaki, zan mallaka maka shagona na siyar da zinari da sabuwar kasuwa, kuma duk wani event da za ayi ni zan ɗauki nauyi”


Da sauri Asim ya miƙe tsaye yana mamakin irin wannan narkakkiyar dukiyar da zata bashi, saboda kawai ya auri ƴarta ƴar da bata taɓa labarta masa tana da ita ba.




________________________________


BEST REGARDS 🌹
I LOVE YOU ALL♥️


*77*


Kalsoom ta yi baya-baya kamar zata koma ɗaki, sai Rashida ta yi saurin miƙewa tsaye ta ɗaga mata hannu.


“Dan Allah ki tsaya ki saurare ni, ba cutar da ke zan yi ba, zuwa na yi na roƙe ki kuma na nemi taimakon ki”


“Akan mi, mi zan miki?”


“Ki dubi girman Allah ki taimaka min ki riƙe min ƴaƴana...”


“Ban gane ba, kamar ya ƴaƴanki?”


“Bana son amaryar da Hilal yayi ta riƙe su, saboda bata da tarbiya kuma azzulamace zata iya cutar da su”


Kalsoom ta nuna ta da yatsa tana mai jin duk wani tsoro nata ya tafi.


“Ke Rashida yadda kika yi boko haka nima nayi, karki nemi raina min hankali wato na rikasu a sake cewa zan kashe su ko? Naga dai yanzu mu biyu ne, be kamata ace ni kaɗai kike kishi da ni ba”


Hawaye ya cika idon Rashida.


“Ba kishinki nake ba wallahi, gaskiya nake faɗa miki kuma nake roƙon ki, ki taimaki rayuwar ƴaƴana ki riƙe su”


“Teema ce tafi kowa dacewa data riƙa ƴaƴanki, saboda ita ce ta gari a idon Hajiya, kuma an yarda da tarbiyarta, sannan naga ƙawarki zata kula miki da su kamar ke, dan haka ki fita ki bar min gida ko na kira Hilal yanzu na faɗa masa”


Ta share hawayen da suka zubo mata.


“Ba sai kin kira shi ba, zan fita, na gode da kika saurare ni, ban cancanci ki saurareni ba amman kin saurare ni na gode sosai”


Ta saka niƙab ɗinsa, sannan ta juya cikin kuka ta fice. Rufa nata baya Kalsoom ta yi, ta tsaya bakin ƙofa tana kallonta, har sai da taga ta shiga motarta mai gadi ya buɗe mata gate ta fice sannan hankalinta ya kawanta.


“Allah ya min tsari da sherin ki ni wannan wane irin mugun kishi ne!”


Ta faɗa tana maida ƙofar falon ta rufe.


*** *** ***


Da wani irin kuka Rashida ta ƙarasa gida, tana mai jin zuciyarta kamar zata tsage biyu, saboda baƙinciki da damuwa, ta rasa inda zata sa ranta taji sanyi, ta rasa inda zata saka rayuwarta ta samu sassauci, lokaci ɗaya duniya ta juye mata ta zo mata baibai.
Bata samu gurin faka motarta ba saboda motar Alhaji Bashir da ke waje, hakan ya tabbatar mata da yana ciki kenan.
Tafiya take kamar wata tsohowa, daman bata da wani kuzari saboda rashin cin abincin kirki da kuma damuwar da ta gama karya mata gaɓoɓin jiki.


Safa da marwa ta hango yana yi a ƙofar shiga falonta, ko be faɗa mata ba, tasan Asmee ta kai masa labarin da ta faɗa mata ɗazun ne, dan tana iya hango tashin hankalin dake shimfiɗe saman fuskarsa. Tun kamin ta ƙaraso inda yake, ya soma nuna ta da hannu, cikin wata irin murya da shi kansa be san yana da ita ba.


“Macuciya azzaluma, dan taki rayuwar ta ƙare shine kike neman abokin kuka ko? To nafi ƙarfin ki Wallahi baki isa ki rushe min rayuwa ba”


“Kamin ka zo nan kana min hargagin banza ina fatar kaje asibiti sun tabbatar maka da kana ɗauke da cutar ko? To ni ba abokin kuka nake nema ba, kai ne kake neman abokin mutuwa, dan rayuwa sai ta fi taka tsawo, sannan na gama rushe maka rayuwa Alh Bashir matuƙar baka aure ni, dan ban dace da zama da kowa ba sai kai, kai ne ka sani a halin da nake ciki”


“Ko kuma kika sani ciki ba, daman ai na daɗe ina zarginki, duk mace da zata bada kanta ga wani namiji ba mutum ɗaya zata tsaya ba, waya sani ma ko mijinki ne ya ɗauko cutar ya saka miki ke kuma kika saka mana, ni ban san ƙaddararta kai ni mu'amala da ke ba”


“Ni bance ka zame min ƙaddara ba kai zaka ce na zame maka? Na rasa abubuwa da dama sanadin mu'alama da kai, ƴan'uwana sun guje ni, mijina ya sake ni, na rasa lafiya ta, da duk wani farinciki nawa sanadinka Bashir, duk kai ka jani ga wannan halaka”


“Ko kuma kika jani ba, da baki sake jikinki ba zan gani ne har na yi sha'awa? Idan baki yarda ba fyaɗe zan miki ne? Baki kiji na faɗa miki da zarar naje aka gwada jinina aka tabbatar ina ɗauke da wannan cutar kutu ce zata raba ni da ke...!”


Yana kaiwa nan ya doshi gurin motarsa. Ita kuwa ta raka shi da maganganu tana hawaye.


“Idan ka fasa kai ni kotu baka haifu ga uwarka da ubanka ba Bashir kai ba ɗan halak ba ne, azzalumi macuci wanda be ji kunya keta dokar Allah, sakarai mai neman Matar abokinsa Allah ya isa tsakanina da kai”


Sai ta ta kunna motarsa ya bar gidan sannan ta durƙushe a gurin tana kuka.


“Kaico na ni Rashida, ina ake siyar da farinciki ne na siya! Ina zan yi musanyar damuwa da kuka na samu sanyin zuciya! Mi na ma duniya haka ne? Miyasa suka ƙaddarori zasu taru a kai na ne? Allah na tuba ka yafe idan zunubi na ne yasa ni a wannan halin”


Kuka take sosai tana ji kamar ƙasa ta haɗiyeta ta mutu ta huta gaba ɗaya da wannan rayuwar. Ra rasa dalilin daya sa rayuwa take koya mata darussan da take ganin bata cancanci koyansu ba.






NAMRA POV.


Kai tsaye direban ya nufi gidan Mai Martaba kamar yadda Yarima ya umarce shi, horn ɗaya yayi aka buɗe musu gate, ɗayan part ɗin gidan ya nufa da su, sai ya faka daidai ƙofar part ɗin ya fito da sauri ya buɗe ma Abbah ƙofa.


“Ya ce akwai komai a ciki, idan akwai abunda kuke buƙata zaku min magana”


Kai kawai Abbah ya ɗaga masa ya nufi ƙofar. Anty Amarya ce ta amsa masa da to, Namra na riƙe da hannun Anty kanta kuma kwance saman kafaɗar Anty, har suka shiga falo, sanyin ac ne ya fara musu martabun, daga bisani ƙamshi ya biyo baya. Kai tsaye Abbah ya nufi wani ɗaki dake ɗayan ɓangare da wasu ɗakunan, yana shiga ya hango manya tufafi kala biyu saman gadon, sai kuma kayan bachi da ba a cire daga leda ba kala ɗaya, an ɗora takalmi da turare da hula mai kyau saman kayan, hakan ya tabbatar masa nan ne ɗakinsa, ɗan murmushi yayi kaɗan ya rage kayan jikinsa ya nufi bathroom.


Mamaki ya cika Namra da Anty Amarya lokacin kowa ya samu tufafin sajawa da kayan bachi saman gadonsa, bama kamar Namra da ta tarar har da pants da pad ya aje mata, ya akayi yasan bata sallah shine abunda ya fi tsaya mata a rai. Bathroom ta shiga, ta yi wanka, sannan ta shirya cikin kayan bachi masu kama da na maza, ta fito ta nufo falo. Anty Amarya da Abbah ta samu zaune a dinning suna cin abinci. Abbah ne ya fara ɗagowa ya kalleta, murmushin da ta gani a fuskarta yasa idonta cika da ƙwalla.


“Toh Sarkin kuka zaki fara ko?”


Cewar Anty Amarya fuskarta ɗauke da annuri, tana miƙawa Abbah tea da ta haɗa masa.


“Komai ya zo min kamar mafarki, gani nake kamar ba gaske bane, ban yi zaton Abbah zai saurare ni haka da wuri ba har ya yafe min, nasan nayi muku abubuwa marar kyau da yawa, amman duk da haka suka samu fili a zuciyarku kuka yafe min”


“Kin cancanci yafiya Mamana, saboda kin gane kuskurenki, sai dai kin shiga rigar mutane masu mutunci wanda hakan yasa kika samu yafiyata a kusa, sai dai ina fatar ba zaki ƙara aikata irin wannan kuskuren ba”


“Wallahi ba zan sake ba Abbah, na maka alƙawari har na koma ga mahallici na,ba zan sake aikata kwatankwacin wannan kuskuren ba”


“Allah yayi miki albarka”


“Amin Abbah na gode, i love you so much”


Ta zo da sauri ta rumgume shi tana kuka. Anty Amarya ta share hawayen idonta tana kallon Abbah.


“Allah ya saka maka da alheri, na gode”


“Yanzu ai ta kuka da ciwon zuciya ya ƙare ko?”


Cewar Abbah fuskarsa da murmushi yana kallon


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login