Showing 87001 words to 90000 words out of 145392 words
Chapter 30 - NI ZAN LADABIH COMPLETE DOCUMENT By Sajida Nijar .txt
wahakar dukawa da darzar fatar wata?????, In ya min.....idan bai min ba gaskiya aaaaaa......."
Idannuwanta ta kankance ta ce" ABDUL me kake nufi?"
Sai da ya kausasa nasa idannuwan ya ce" Abinda kika ji AMINA"
muhamadu rasululahi Sallallahu alaihi Wasallam, tana kallonsa har ya bacewa ganninta, gaba daya ya yi tafiyarsa, ita da za'a tambayeta waye fitsarare a cikin fitsararun zamani da ta fadi cewa ABDUL ne dan gidan Baba Mai Shanu walahi, idan ya kama sunnanta kirat har gabanta faduwa yake yi, inda dalili jama'a? Ana ce mata aunty da mutuncinta da komai ta zo zamanin da kannin bayanta zayana ce mata wai AMINA? AMINA fa? Ko su iyayenta ce mata suke mai sunnan Ina, dan mahaifinta har ya rasu ce mata yake yi Innata, shin shi ABDUL bai san sunnan Maman abansu ta ci bane hala?
(Ah to....tambayeshi dai)
Juyowa ta yi sai cika fuska take yi suka yi ido hudu da Risala dake tsaye wajen tagar bangarenta ta yaye tana kallon Aminar da wani mugun kallo tamkar zata kasheta da mari
Kanta ta dauke ta tataka ta nufi bangarenta, sai ga Biyu an dawo da su sunna ta maganar result din da Hasan ya samu yau da malaminsu dake masu lesson ya masu exercise
Da gudu Husaini ya kawowa uwar a lokacin da take bude bangarenta ya mika mata, sam basu lura da fitowar Risala da doso wajensu da ta yi yana fadin" MAMA, Mama albishirinki, dubi result din Hasan, dama Dady yace idan ya maida hankali zai siya mana tap da kuma babur irin na yara muna tukawa a gida , yau Dady sai ya yi dariya idan ya ga result din nan"
"Wanene dadynku?" Risala ta fada da mamaki tana kallon Husaini yadda yake dira ya karra kiba fatarsa ta karra murjewa bul bul da shi sak irin ya'yan gayu
Amina ta ninke takardar itama abinda ta so kwabarsa kennan da ya dage yana ihun yau dady kaza yau dady kaza ta kalli yarinyar nan da kallon basira bata ce komai ba a lokacin da Husaini ke fadin" Baki san dadynmu ba hala?, Ke din wacece wai?" Tambaya ce ya yi dan harga Allah bai santa ba, kuma ta fito ne irin a cikin gidansu, abu da yaro shi ai yanzu a tunaninsa ya fi kowa iko da fada a gidan nan tunda an fada masa cewa gidansu ne
"Ni kake tambayar wacece ni?" Ta fada a zafafe tana ruruko masa ido, hakan ya tsoratar da shi da sauri ya labe a bayan mamansa yana lekota
AMINA ta dubeta da kyau tana tunanin abunuwa da dama a ranta, abu daya ne ta sani a yanzu a wajen nan, shine, idan har yarinyar nan ta zo ne dan ta raina mata wayau zata dauko tsimingiya ta darwaye mata jiki tas har sai ta summa dan wahala, dan bata tunanin wannan yar ficikar y'ar zata iya rainata ta kyaleta
A dake ta ce"
A dake Amina ta ce" Am, lafiya?"
RISALA ta dawo da dubanta kanta tana sake daure fuskar itama ta ce" Magana na zo mu yi, mu shiga daga ciki ko?"
Har Amina ta zo kiyawa, sai ta tuna ai a cikin ba zata rasa bulala irin ta caza ba haka, dan haka ta janyo hannun Hasan dake tsaye yana jiran ko ta kwana ta fara tura su ciki fuskarta hade ta ce" Maza ku je ku yi wanka ganinan zuwa"
Cikin suka wuce gaba dayansu yaren, ita kuma ta karasa wajen da soket take ta ciro cazar wayarta ta yi tsaye irin tsayuwar nan da kake yi idan zaka zane yaronka tana kallonta ta ce" Bismillah "
Hannun nata ta bi da kallo, a ranta tana ayana Allah ubangiji ya sa ABDUL da ta gani ysaye yana kallonsu ya biyo bayansu ya tardo Amina da bulakar dukan nan, da ta ji dadi taa gode Allah da ya bata damar gala mata sharin da ABDUL zai saketa, dan ta tabata ba zai kyaleta ta masa aikin nan a gidansa
Risala ta yi tsaye a saitin da zata iya gannin mai zuwa tana kallonta ta ce" Zuwa na yi mu yi magana a kan Mijina!"
Amina dai tana kallonta bata tanka ba
RISALA ta sake fadin" A kan mijina na zo mu yi magana......"
" Wa fa kike magana a kansa?" Amina ta fada tana sake fuskantarta
Risala ta ce " Wane kuwa da ya fi wanda kika san hanyar da kika bi kika aura, ABDUL nawa ne, mun yi soyaya da shi mai karfin da na kori duk wata yar iska ko wata mai tunanin ta isa, haka na juri wuya ko dadinsa, na yi ta dakon gannin aurena da shi, tabas kin ci galaba da kika same shi ta hanyar Waina, ama in sha Allah daga yanzu zan dawo da Abdul nawa ni kadai abina, domin bana tunanin zan iya rabashi da wata, ko budurwa bale ke, bana jin zan........."
" Ki saurara haka!" Amina ta fada a kausashe tana warware hannunta dake nade
Ta dubeta sama da kasa ta ce" Wama sunnanki plz?"
Risala ta wani rike kugu tana jijiga ta ce" RISLA, RISLA"
AMINA ta tabe baki ta sake dauko dubanta tun daga sama har kasa ta watsar ta ce" Ke kika san dadinsa, ke kika rayu da tsarin yadda zaki rayu da shi, ke yake gabanki!, In kin kula ba ni na roka ba, haka kuma da ina ra'ayin da na tabatar maku kwalelenki a kansa, domin yadda kika ga a ayo na fiki, to fa a shekarunma haka ne, haka kuma a iya tuku sitiyarin balagage!, Ki kama kanki ki juya ki barmin daki, domin idan kika yarda maganar batanci ta shiga tsakani RISALA kike ko? Walahi sai na wanke maki jiki da dukan da za'a kasa gane ki, dan ni ba saarkkkkkkkkkkkkkkkkkkkkk"
Wani irin ihun yan bori da Risala ta saka sannan ta aniya ta maku a kasa ta sake kwala wani ihun tana fadin" Daga magana sai ki dake ni? Daga magana sai ki dakeni? Innalilahi na shiga uku jama'a wayo a ceceni............."
Baki sake Amina ta tsaya da bulalarta a hannunta tana kallon Risala
Ita abinda ta shiga tunani ko mahaukaciya ce, sai dai kafin ta gane hakan ta ga shigowar ABDUL RA'UF, hakan ya bata amsar tunaninta
Da ido take ta kallon ikon Allah ABDUL ya nufi Risalar ya yi tsaye a kanta yana karra son fahimtar wai da gaske Amina zane Risala ne take yi?
Amina wani irin abu ya tsaya mata a wuya ta nunota da bulalar ta ce" Ni zaki yiwa shari a kan abinda baya gabana?, Ni zaki yiwa karya har a falona?, Bara na zane kin sai ki yi mai dalili......." Kun san fa wanda bai iya munafurci ba baya iya boyewa, shi yasa Amina ta kasa daukan wasan Rislaa itama ta dana, sai kawai ta yi irin abin nan na mai fitowa kwado kwado ya fadi gaskiya ta fadi hakan harma ta nufi Inda Risalar take
Hannunsa daya ya saka ya tareta sannan ya fuzge bulalar dake hannunta yana binta da kallon dake nuni ransa a matukar bace yake
Sake tirzawa Amina ta yi da nufin sake dosar Risala da ta mike ta labe a bayansa tana kukan karya bilhaki ita Amina dukanta ta yi
Sai dai bata kai ga isawa ba ta ji yaa yiwa hannunta wani riko daya tal a tsayen da yake yana kallon yadda take haki ita a dole sai ta daki Risala sannan ya janyota ta bayanta ta hadu da kirjinsa yana dan sasauta rikon da ya yi mata a wajen kunnenta dake fitar da kanshin nan mai saka zuciya nutsuwa ya ce" Ki nutsu mana aunty kar ki sa a maki fasarar cewa kina kishin ABDUL ne?"
Kamar ya wanka mata mari haka ta farka daga zuciyar da ta dabeta ta dago tana kallon sajen fuskarsa da idannuwansa dake nunin ransa a bace yake
Muryarta a cec ciki ta ce" Ama ai kai ka san ba haka bane ko?"
Kallonta yake yi, komai nata sai lamarin yarinta ya bayana, du yadda ta so mazewa dan a ga girmanta sai ta shagalar da shi da abinda ke sanyaya zuciyarsa
A hankali ya ce" Eh to, kin san daga aikinka ake fasaraka yanzu duniya"
Amina ta wani turo baki kasa kasa ta ce" raina ni fa ta yi, wai kashedi take min, ni banma fara dukam nata ba ta fara wannan haukan fa ABDUL"
ABDUL ya yi murmushi yana tare Rislaa dake son jin abinda suke fada ya kara rage amon muryarsa sosai ya ce" Gwara dai kar ki biyata ke ai baba ce ko?"
Amina ta gyada kai
Abdul ya ce" To kyaleta kawai kin ji?"
Amina ta gyada kanta tana dan lumshe idannuwanta dan yadda yake maganar cen kasa sai ta nutsu koda zata iya jinsa
A hankali Abdul ya zarro harshensa ya dan lashi gefen kunnenta da shi
Zabura ta yi tana wartsakewa ta ja gaba kadan tana kai hannunta hadi da sosa kunnenta ta juya tana fadin" Kin ci Sa'a, gobema ki zo min nan ki gani, dilla malama yara kanana sai raini......"
Su dukansu sunna kallon kofar da ta rufe ne a tsaitsaye, shi har ga Allah da tace yara kananan ne ta saka masa stop, in ya fahimta dai kamar matarsa ta janyo masa wajen uman biyu
Ita kuma abinda take son fahimta shin maganar da ta yi ya gane mai take nufi ne ko menene ya cewa Aminar?
A sanyaye tana dubansa ta ce" AR, dukana fa ta yi da bulalar nan"
ABDUL ya dawo da dubansa a hankali kanta, samun kansa ya yi da dan tsura mata ido, sai kuma ya budi bakinsa ya ce" A haka kuke yawo a cikin gidan kema gardaye na yawo? Wai ko so kuke yi na fitar da ma'aikatan gidan nan ne na zuba maku mata ? Koda yake yanzun matanma sai mutun na kula kar a sakashi uku ........"
Ya idasa yana nufar hanyar ficewa a dakin Amina
Dan daga kafarta ta yi sai kawai ta yi luuuuuuuuuu ta tafi da karfi ta kifu a kasa
Da sauri ya ja da tafiyar da yake yi ya juyo inda ta fadin
Cikin sasarfa ya karaso wajen yana fadin" Subahanalah, Risala, Risala"
Mace, du yadda ta so tafiyar da tsarin rayuwarta a sila na daukan alhaki ko cin galaba a wani abin sai dai idan bata saka kanta ba, shi yasa ko me take yi a yawaita yi mata nasiha, Adu'a, fada, da kuma uzuri
Du yadda ya gane cewa harda shari a lamarin Rislaa faduwar nan da ta yi take rike numfashinta sai ya daga masa hankali
Cike da damuwa ya nemi aboki kuma amininsa ya zo ya dubata harma ya banka mata allura ta dexa domin shi lamarin numfashi a yadda ka sarafashi ake ganninsa, haka masu ciwon huka idan ba a lokacin da ta tashi ba aka yi masu hoton wajen ba za'a taba gannin ciwon haka ba
Bata da shi, batada dalilinsa ta ringa jan jumfashin tana hucin mai huka a dole aka yi mata allurar da ta hadasa mata rawar jiki da bugawar zuciya , domin haka take ko baka da lafiyar ne ana yi maka ita take hadasa maka haka a hankali kuma ta saki
Dukka wannan azabar Risala ta ji ta gani ta dauka, zata iya jurewa in dai a kan Mijinta ne
Du yadda ya so mayar da ita nata bangaren abin ya gagara, da sauran kwanan Amina daya Risala ta kwana a bangarensa, sai dai bai yarda wani abu ya shiga tsakaninsu ba, du irin yadda ta bale mabalin riga ta langwabe da gangan sai ya tashi ya bar mata dakin, domin ba zai taba bari yana cikin hayacinsa ya saka kansa a uku ba..............ita dai ta karra daukan hakuri dan ta san ai daga gobe komai ya kare ta kama aiki, a nan zata nunawa Amina menene kula da miji
________________________________
Washe gari, kusan karfe takwas da rabi Amina ta karasa bakin kofar dakinsa ta tsaya tana tunanin ta yadda zata iya bugawa
A kadan ta dauki minti ashirin a nan, domin har zama ta yi ta rafka tagumi tana kallon dan rainin hankalin da ya hannata fita a gidan
Tunanin da ta yi da sake duba message din cewa daga yau har zuwa kwana bakwai je kake da damar ajiye takardunka , ta kuma san cewa tanada gyare gyaren da zata yiwa takardun nata, ga kuma gyaran kulin wainar Baba domin gobe ne juma'a ya sakata yin safiya dan ta je ta gama komai da wuri ta dawo, ga yar uwarta da ta kwana a ranta, idan tana tune da irgen bai fi sati biyu ba Fido ta cike lokacin haihuwarta, a irgensu fa , domin ba asibiti ta je aka fada mata ba
Sake mikewa ta yi ta kai hannunta a hankali ta shiga kwonkwasawa sannan ta dan dakata
Sake saka hannun nata ta yi ta kuma kwonkwasawa sannan ta saka hannunta wajen abin budewar ta murda da fatan Allah ya sa ya tashi ta shiga da salama a bakinta
Ido ta zuba a abinda ta samu tana kallo
Da wani irin langwabewa Risala ta rigo hannunsa tana furta" Weshhhh baby ba zan iya zama ba ka bani a bakina plz"
A hankali ya kamata da kyau ya zaunar da ita
Risala ta karkatar da zamanta tana wani irin dantse lebe tamkar a kasanta ne take jin zafi
A hankali Amina ta bi yannayin nata da kallo, ta samu kanta da sake zuba mata ido na yan dakiku sai kuma ta dawo da dubanta kan ABDUL dake tsaye yana kallonta, yar simple din makup din da ta yi ta fi komai shiga idannuwansa, abinda ba koda yaushe take yi ba shi yasa komai kankantarta idan ta yi takan yi kyau sosai
A hankali ta bi shigar jikinsa da kallo, farar riga ta ciki irin ta maza fara kal kal ta lafe a ginanen jikinsa ta dan hau saman wandon dake jikinsa na yadi ruwan madara wanda har arzuzumin dake jiki ana ganni da kuma irin yannayi dai na tsarin hakitar gamjin namiji sannan ta hauda dubanta har zuwa lebensa mai ruwan na jarirai ta kai wajen hancinsa sannan ta sauke idannuwan nata tar a cikin nasa idannuwan suka yiwa junna kallon ido cikin ido
A hankali ta janye ta juya tana manta kwata kwata abinda ya kawota dakin
"Aminah".....ya furta a sanyaye yana kallon bayanta, tar saman bayanta dake cikin hijab har kasa ja, ama irin dinkin hijaban yan matan zamani hijab kamar doguwar riga jama'a ya bi ya lafe a jikin matar mutun?
A hankali ta juyo tana sake kallonsa
Sai a lokacin ta tuno abinda ya kawota dakin
Ido ta dan lumshe a hankali ta ce" Dama, zan fita ne, wai sai yace ka saka dokar sai ka sanar masu idan wani zai fita a gidan.....gashi ina sauri inada muhinman abubuwan dake gabana"
Har ta dire aya yana biye da hannunta na dama da take dan nunawa da shi tana dan wanawa da shi kadan kadan haka.........., Sannan ya sake zuba mata ido da yannayin da ta ajiye maganar tana sake kai dubanta wajen da Risala ta kara karkacewa tana furta" Baby....zafi nake ji......................"
A hankali ya dauke dubansa bayan ya sake kallon Risala da tunanin hukar nata har hanna mata zama yake yi?, Ya sake duban Amina ya ce" Uman Biyu, ina da ina zaki je ne?"
Amina ta kai hannunta gaban goshinta ta dan murza tana fadin " Zan je gyaran takarduna ne, sannan na biya wajen Baba"
Zaunawa ya yi saman kujerar yana dauko kofin lipton din still yana binta da kasalalen duban nan ya ce A'a baza ki tafi ba
Ku gafarceni dan Allah, abubuwa ne a kusa kusa hidimun biki
Na gode sosai😍😍😍😍
A hankali Amina ta zubawa fuskarsa ido
Daure fuskar da ya yi, da irin zaman da ya yi yana zuba lipton din a kofi mai dan girma ya zuba madara isashiya ya mikawa Risala yana fadin" take"
Sai ta ji wani abu ya tsaya mata a wuyanta,
A kan wani dalili zai ce mata wai ba zata fita ba kamar wani wanda yakeda hurumi a kan hakan? Ya zauna gaban yarinya shi ga jarababe sunna wani abu kamar basu san ciwon kansu ba zai hannata fita?
A hankali ta ce" ABDUL"
Abdul ya dago yana sauke mata kausasun idannuwansa a kanta
A kausashe ya ce" Idan zaki zauna mu karya ne bismillah...., Idan ba wannan bane ki tafi dakinki kawai"
Magana ce mai nauyi take son fada masa, magana ce mai masifar nauyi take son yayaba masa, sai dai kuretan da suka yi da ido daga shi har fitsarariyar matarsa sai ta ji ba zata fada ba
Abu ya zo mata wuya ya yi mata katutu ta juya da sauro sauri dan bata so ta yi kuka a gaban kannenta ta jawa kanta raini ta fice a falon ta nufi nata dakin
Tunda ta fita ya kura kofar ido na yan sekwani, sai kuma ya saki murmushi a ransa yana ayana' Na san yanzu itama wanda ya daure mata ya yi kirana ya ja min kashedi, oh ni ABDUL RA'UF da gidanka da iyalinka ana saka maka ido"
"Baby bana iya sha da kaina" RISALA ta sake fadi tana hayewa jikinsa dan ta mantar da shi dan cenjin mood din da matarsa ta hadasa masa yanzu tana sake makalkaleshi cen ciki tana ayana' madallah, haka nake so har sai wahala ta isheki kin bar gidan da kanki, wai Ni za'a nunawa bariki ki zo da gardawan ya'ya wai su ringa kiran min miji Dady?, Ina ji ina gani ya ringa kulaki? Zaki yi bayani ne!'
A nutse ABDUL ya dan tareta a jikinsa yana kallon fuskarta,
Tun jiya ya gane take takenta, irin abubuwan da ta ringa yi masa ne ya saka shi a yau kasa ficewa da sasafen nan domin kusan tsirara ta fito a bayi tana ihun kyankyaso yan biraren mamanta sai sama da kasa suke, da yan duwawunta kamun cokali saia dan babarbabar suke abinsu......da kyar ya hanna kansa turmusheta a lokacin , ama a yanzu fitar nan da makociyar dakinsa ta yi tana sababar sababar ya sake motsa shi har kamar ya ci babu, domin irin harbawar da ake masa a cikin wandonsa tamkar za'a tsaga wandon ne a fito a samu abinci a koma barci
A saman kujerar ya juye da ita gaba dayanta, ya zamto tana kasansa, shi kuma yana samanta
Du irin yadda take amsarsa da romancing ya kasa jin abinda yake son ji a lokacin da ake ture shi ana masa ihu da fade faden magangannun