Showing 51001 words to 54000 words out of 145392 words
Chapter 18 - NI ZAN LADABIH COMPLETE DOCUMENT By Sajida Nijar .txt
mayukan gashin na gyaran ne suma tana bin kan sala sala tana sakw gyara mata shi
A sanyaye ta ce" Baba, banfa samu isashen barci ba jiya"
Baba ta yi murmushi ta ce" Ai rabonki da barci tunda aka aura maki Mala"
Kanta ta dago tana kallon Baba ta ce" Baba jiya fa Hajia tace yau tana son ganina karfe goma na safe, kina tunanin takardar sakina ne zata bani?"
"Muhammadu Rasulullah salalahu alaihi Wasallama ke wannan ya, wani irin takardar saki kuma?"
Amina ta yi tsuru tana kifta idaannuwanta
Baba Lauratu da takaici ta ce" ta isa ta baki takardar taki ne kike zaune a gidanta har yanzu? , Ke bakinki yaushe ya fara furta alkaba'inema ban sani ba?, Auren nan du ya mayar da ke wata shashasha bayan abu ne ya same ki sai dai in mutuwa kika yi zai sauka a wuyanki da izinin mai duka bayan mijin nan da kika raina ya saka ki a kabarinki, Ke Amina ki fa kiyayeni fa, walahi ki ji da kyau du wani wanda zai ja da ikon Allah sai dai a yi ba shi, kin ga auren nan da aka tashi daura shi irin yadda ya kawo rigingimj kuma Allah ya tsaya a daura shi ko? To du wanda yace ba zai gani ba sai dai kasa ta birni idannuwansa, wai wani takarda aa ranki zata baki a hannunki karshen kiyaya!"
Amina kam sai ta ja bakinta ta yi gumm, yanzun har dungurinta Baba ke yi, bayan a da bata daga mata muryama da rarashi da komai take binta
Abinda ta fi tsana ne ta hada mata watau ruwan lipton mai zafi aka kada masa kwai da madarar peak ra miko mata tana hade fuska ta mata tsaye a kai, sai da ta shanye ta yi bayi da gudu dan kuskure baki zuciyarta na tashi, takaici n cikata Babar ta bita da kallo tana tabe baki ta ci gaba da hade haden abinda ya dace tana ajiyewa dan haka take yi mata yau kwana hudu kennan ba ji ba gani kayan gyara da na sanyi dibgarsu take kamar ba gobe
Tana dawowa ta tarar da sauran kayan ta zauna ta sha , domin ta dan ciwon da ba zai barka bane gwara ya kasheka ka huta, uwa uba ita ta san aikin banza ake yi, wannan shaye shayen na banza ne, dan ta san ko gawarta abar kunya ce a gaban Abdul bale ita da ranta, ai baba sai baba walahi!
Baba Lauratu ta ajiye mata hijabinta sabo mai tsafta, dudu bai fi sakawa biyar da ta yi masa ba tana kallonta ta ce" Ki kimtsa ki je, goman ta wuce ina nan ina jiranki"
Jiki a sanyaye ta dauka ta saka kayan ta dan fesa turare kadan a hamatarta dan ta ji dadin zama
Baba Lauratu ta ambaci sunnanta
Dakatawa ta yi ta dawo daga nufin fitar Baba ta ce" ki sani, farkon fara mu'amalarki da kakar mijinki ne, dama ban sanki da raini ba, ama a yadda abin nan ke bin keyarki komai kina iya aikatawa........dan haka nake gargadinki da ki kula, idan me zata ce da ke ki tauna amsar da ta dace da ita kafin li bata, ba hakan na nufin ki je a wulakanta ki ba!, Komai talaucin bawa idan ya bada dama za'a wulakantashi, baki zo gidan nan dan roko ba, hasalima baki taba takowa kika zo dan a baki gero ba, a yau da kuke zaune da daraja a kanki mafi girma a cikin darajoji, yin biyaya wajibi ne, haka kuma kare mutuncin kanki wajibi ne a gareki, ki kula Amina"
Amina ta gyada kanta a sanyaye ta fita din
Ashe mai aiki na zaune tun karfe goma tana jiran fitowarta, bata yi gigin shiga bane dab tunda aka daura aurenta Baba ya fada masu wacece ita yanzun a gidan, matsayinta yana da girman da basu isa su shige dakinta kai tsaye ba, Hajia ta turota tunda safe ita kuma sai ta zauna take jira har ta fito sai ta sanar mata sakon
A mutunce suka gaisa, ta mike ta yi gaba fan nuna mata dakin domin hakan ne umarnin Hajiar
Sun jima a kofar dakin sunna jira bayan sun buga an masu gyaran murya, har sai da aka basu damar shiga sannan suka shiga
Gaba daya kanta so ya yi ya rikice a lokacin da suka dakin da yake ainahin na barcin Hajiar ne
Daki kamar ba'a shiga cikinsa? Tsafta, kanshi, tsari abin ba'a magana
Hajiar na zaune saman kujera ne cikin shiga ta shada ta kafa daurinta irin na manyan mata , ba kwaliya ko diz a fuskarta ama sai walwali fatarta mai hasken duhu take yi tsabar gyara da hutu ga shan madara (😌)
A hankali Amina ta raka mai aikin da ta rakota tamkar zata bi bayanta da gudu ta rukunkumeta su juya tare
A sanyaye ta sake juyo dubanta a lokacin da Hajia ke kare mata kallo tun daga sama har kasa, ba zaka taba gane yaya yarinyar take ba dan wannan jarababen hijabin dake janta tamkar zai kayar da ita, kulun a cikinsa tale, ba dare ba rana, ko a cikin gida ko a waje!, Shirmen banza wannan abar ce za'a hada jikanta da ita? Ai ba gami sam
A nutse ta zauna a wajen da ta nuna matan, watau saman cafet, ya zamto ita Hajiar tana sama ne saman kujera kafarta daya kan daya, fuskarta a hade, ita kuma tana saman lalausan cafet din falon dan nesa kadan fa wasu tarin akwatunna kanta a sade a kasa
Hannayenta dake fili Hajia kw kallo, wa'inda take dan murza su a hankali wanda hakan ya nuna mata cewa lalle tana dauke da strss wanda take son controlng a zaunen da take
Bakinta ta tabe , a kadan ta dauki mintunna biyar tana sake karantar Amina
A bayane yake Amina mahaukaciyar Black beauty ce, bama irin hancinta da ya tafi a mike zuwat ya sauka dan daidai kusa da labanta, manyan idaannuwanta masu hasken fari da duhun baki sidik na ciki, sai habarta mai dan tsayi kadan sannan daga tsakiyarta ta dana bile kadan
Batada cikar kumatu irin kubulbul din nan, kuma batada ramar fuska, gaban goshinta kuwa kan iya sheda maka da ba zata rasa gashi mai kyau ba dan gayanan yana nuna kansa duda kindime shi da ake yi
Sakw tabe baki ta yi a hankali, cike da iya sarafa harshe da basarwa ta ce" Wace fuska kika ba wannan hadi ne?"
Sai da ta sake maimaitawa kanta tambayar har ta fahimta sosai , sannan ta dago a sanyaye ta dubi Hajiar cikin ido a sanyaye ta ce" Bakuwar fuska ce "
Hajia ta dan kawar da kantan nan ta sake juyowa tana kallonta ta ce" Wace kike maraba da ita ? Ko kike hangen rashin dacewarta?"
Yanzun sai da ta ji kamar ta bada amsar a zake, watau da zakuwa, sai dai ta dab kiyaye yanzunma ta bada amsar kamar yadda akai mata tambayar, a hankali ta ce" Ba cencenta, sam abin boyewa ne a wajena Hajia"
Da mamaki Hajia ke kallonta, so take ta fahimci iya gaskiyarta kennan ko bariki zata nuna mata?
"Idan hakan ya zamto tarihi ne, ina nufin abinda bai dauki lokaci ba ya shude zai dame ki kuwa?" Hajia ta fada ta a karra dubanta sosai da son idasa gane nufinta
Sosai ta yi yaki da dukan abinda yake tare da ita dan hanna kanta sakin murmushin dake ciyota na farin cikin gannin adu'arta ce zata karbu, watau dai Hajia zata salameta ne?
Da kyar ta iya hanna kan nata yin dariyar ko sakin kayatacen murmushin a hankali tace" Idan har hakan ne zabin da na barwa Allah, farin ciki ne in sha Allah Hajia"
Tap, lalle a bayane Hajia ke karantar kamar yarinyar nan itama bata son auren nan, sai dai wani bari na zuciyarta ya shiga fada mata magana kamar haka' ta yaya kike tunanin zata fito maki a mutun ta nuna maki bata son abinda ta bi wani tudu ko wani gangare ta same shi bayan ta san bakya son hakan?, Ai dole zata boye maki dan a zauna lafiya, sai dai ta makaro, ita dinta ba'a so ba komai ba!'
Hajia ta basar, ta dubi agogon hannunta na azurfa mai kyau dan karami ta sake fuskantar Amina ta ce" Na saka ki zi ne dan ina so mu yi magana da ke, ina so ki samu alkali ki nuna masa amincewarki da auren jikana, watau kin yarda ya auri yarinyar da yake so, ina so ki nuna masa cewa shi ya maki maganar ke kuma kin amince da hakan, "
Kallon da Amina ke yi mata ya dakata itama kureta da kallo, kallon take son fahimta ko na menene? Sai dai bata gane ba, dan haka ta ci gaba da magana kamar haka" Amina, ke kin san ke din ba zabinsa bace, haka kuma ba zaki taba amsa abubuwan da ake da bukatar ki amsa dan huce takaicin zama matar gwamna ba, ABDUL RA'UF yanada yarinyar da suke soyaya, sun shirya kansu ana shirin aurensu maganarki ta bilo, a yanzu da kika samu hakan ina tunanin zaki yi masa adalci shima ya samu tasa wace yake so"
'waye ya ce maki jikanki shine abinda yake gabana?, Waye yace maki aurensa ko rashin aurwnsa ya dameni ne? An fada maki inada casss da abinda ya tsarawa rayuwarsa ne? Ko an fada maki ni din macen siyasa ce?, Hajia, dama zaki dubi maraicina, ki dubi karamin karfina, ki saka jikanki ya salameni, da kin rufan asiri duniya da kiyama kin kuma samu lada, domin bana tunanin zan taba yiwa kannin bayana *LADABAIH!*' wannan furuci shine Amina ke kokowa da shi a cikin zuciyarta da kuma kirjinta, sosai ya danne mata kirji yana son falasa kansa ama ta ki bashi dama ta rike shi da dukkan karfinta, bata so ya tonata ya saka ta raina baba, bata so ta yi abinda Baba Lauratu ta hanneta duda tunda ta zauna a wajen bayan ciwa kanta mutinci babu abinda ake yi
Hajia ta dora da fadin"
*NZL PAGE2️⃣0️⃣*
Hajia ta dora da fadim" Ki duba kayan nan, suturunki ne da na saka aka hado maki aka kawo min, zan dora da makudan kudi da kuma mota dan ki rarashi mijina a yi auren nan, ina so daga yanzu har a gama maganar auren kar ki zamo matsala a ciki, ki bada hadin kai a yi komai da ke, idan ya so daga baya ko menene sai a sake zama a warware abinda yake cikin duhu"
A sanyaye Amina da ta kasa kanta furta wannan furucin a yanzu ta dubi Hajia ta ce" Hajia, zai salameni ne?"
Hajia ta yi mata duban bata fahimta ba?
Sai a yanzu Amina ta fahimci abinda ta fada, dan haka ta ji nauyi da kunya na son lulubeta, harma ta kasa katabus
Muryar Hajia ta sakata dagowa a hankali tana kallon Hajia
Hajia ta ce" Ban fahimci maganarki ba"
Amina ta sake sada kanta, ta riga ta furta, dole ta bayana ma'anar furucinta,
A sanyaye ta sake dagowa , bata ko jin tsoron dakewar hajiar ta sake dubanya, ta kuma duban akwatunnan da suka firgitata, tarin alwatunnan da robobi manya dauke da takalma, a haka an yi abin ne irin jeka na yikan nan, ama ita gani take yi ta je ina da kayan nan? A sanyaye ta ce" Hajia, ni Uwa ce, na saba fita na kai yarana makaranta sannan na koma na dauko su, kafin na dauko su nakan zo na yi yan sana'a'o'ina irin gyaran amare da tuyar kosaina, na dakatar da karatuna dan jarabawar da zan zana a lokacin ban cike abinda ake da bukata ba, Hajia, kika ce za'a warware abinda yake cikin duhu, shine nake son sannin kina nufin idan aka gama maganar auren nasa, ni zai bani takardata ne? Dan na je na ci gaba fa tawa rayuwar kamar yadda na saba?"
A hankali ta ajiye maganar, sai kuma ta sake duban wajen kayan ta ce" Hajia, bama sai an bani kayan nan ba, walahi zan yi ba sai an bani komai ba, in dai zai bani takardar shikenan, a lokacin da Baban ya yi furucin sama min miji da ya alakanta haka da na nuna masa cewa ya bani datijo, ko dan yan yarana"
Ikon mai yi mana ruwa kawai Hajia ta tsaya tana kallo, gaba daya sai ta so shiga wani tunani daban a kan yarinyar, kai harma sai ta so afkawa a tunanin kiyaya ce ta saka haka ko kuwa kwarewa a iya wasan ne?
Ta dan jima tana nazartarta a haka, karshe ta ba kanta amsa daya jal, koma meye ke dawainiya da yarinyar ita ba shine a gabanta ba, a yanzu abinda ya fi dadada mata rai da tace zata yi , ta zata idan ta ji maganar kishiya hakan zai daga mata hankali harma ta kasa boyewa, sai ta ga ba wannan bane a gaban yarinyar gaba daya
Kai ta dan girgiza ta sake duban kayan, to ita kayan nan ai ko kyautar da ake yiwa ma'aikatan gidan idan zasu kai lefen aure ya fi haka yawa bale wai matar ABDUL
Duda bata san abubuwan dake cikin akwatunnan na, ama ko meye a ciki ta tabata kadan ne a abinda matar ABDUL zata malaka harma ta anfana
Motar kanta ba wata baba bace dan ba zata wuce million bakwai ba da ta sa aka kawo sannan ta zuba kudi a ambulop du saboda koda ta karkare ta siyeta da kudadan da ta tabata kaf danginta basu taba rikewa ba, sai ta samu mamakin furucin yarinyar
Kafadunta ta dage ta ce" Kina nufin zaki yiwa Alkali maganar nan ba tare da kin nuna masa saka ki aka yi ba, kuma ki nuna masa da Abdul kuka tatauna maganar, irin kin aminta ne da son ranki?"
Amina ta gyada kanta ta ce" Hajia, duka kaf zan yi, zan yi gaba daya , in dai nima zan koma bakin shagulgulana na yau da gobe"
A gaskiya Hajia bata da cass da hakan, bata da matsala da hakan ko daya, dan fice da shigowarta kuwa bata tunanin zai damu wani, ta je inda zata je, ta dawo a lokacin da take so, bata da matsaya da hakan, in sha Allah ita kuma zata bata damar yin abinda take so har a yi auren nan, in yaso da laluma sai a saketa ta kama gabanta,....ashema abin ba wani wahala ko raini a ciki
Murmushi ta yi na samun nasara tana gyada kanta ta ce" Ya yi, ama ki sani kayan nan da kudin nan duka ai hakinki ne, haka kuma motarma taki ce, kina iya hawa ko ki saida duka malakinki ne, ina so daga gobe ki same shi, idan har ya amince da maganar ki shaida masa karshen watan nan ne za'a tura din, kuma saka auren sati biyu ne suke so"
Kai Amina ta gyada sannan ta karra yin shiru tana sauraron dukkan tsare tsaren da Hajia ke dorawa da abinda suke so a yi ita da jikanta
Sai da ta gama ta salameta
Tare da yan aiki suka sauko aka shiga shigewa da tulin kayan da aka batan ana jibgewa
Baba Lauratu da ta kasa tsaye ta kasa zaune tana gannin hakan ta mike tana duban Aminar da yannayin son karrin bayani
Sai da suka gama suka tafi sannan Amina ta samu waje ta zauna ya sada kanta zuciyarta na afkawa a kogin tunani
Aure? Dan bata da daraja, an bata danar fita a lokacin da take so ta dawo a lokacin da take so? Lalle gaske hankalinta ya dugunzuma ya tashi a kan maganar auren dan gata, koda babu maganar shekaru rayuwar nan ba tata bace sam
Baba Lauratu ta kalla dake yi mata tambayar wadinnan fa?
A hankali ta ce" Baba, da kika je gidan Fido kin kuwa fada mata komai? Ama ban ganta ba?"
Baba ta zauna fuskarta na cenzawa ta ce" Kin sani sarai fa yar nan, ga ciki ya tsufa ga rayuwar firdausi sai yadda Allah ya yi kawai, ana fatan samun cenji na alkhairi in sha Allah "
Amina a wani sanyayen ta ce" Zan je gidan nata gobe in sha Allah, Baba ai cikin nata yanzu zai kai wata takwas ko?"
A kufule Baba Lauratu ta ce"Ke Amina, yaya ina maki wata maganar ke kina yi min wata ne?, Ina maki magana a kan kayan nan ke kina min wani shirme daban? Wace irin fita? Auren naki dudu kwana hudu yau ki fara fita gobe ko bazawara kike ai kya gama amarci bale ko tarewa baki yi ba?"
Amin ta yi murmushi tana sada kanta , sai kuma ta dago a sanyaye ta shiga labartawa baba duka kaf abinda ya faru, komai da komai bata boye mata ba, ta dora da fadi " Baba, ki yarda, sannan ki saka dangana da maganar nan, ba aure kike so na yi ba? Zan yi, daidai da ni, zan yi auren , ama ki bari lamarin nan yaa warware cikin ruwan sanyi, akoy cin zarafi a cikin lamarin, wanda ya hada din kuwa ba wanda zan ringa tararwa da kukana bane a kan wace take iyalinsa, sai abin ya fado a kan gabar nima bana ra'ayin hakan, Baba idan da halima ni din nanma ya fitar da ni ya dauko hudu tashi daya, shine isar namiji ba wai daya tal ba, kayan nan ko tsinke ba zan taba ba, kuma kin manta gobe juma'a ranar tuyar wainar Baba ce? A goben kuma nake son zama da Baban in sha Allah"
Tabas abu ya daki Baba Lauratu, magangannun gaba daya sun shigeta ta yadda ba'a zato ba'a tsamani, haka kuma irin abinda Aminar kanta ta yanke ya bata mamaki
Koda yake haka ne, idan kana cikin hali na wuya wuya din zuci babu abinda ba zaka fadi ba
Murmushi ta yi tana kada kanta, a ranta ta ayana' Lalle akoy ranar kin dilaci, akoy ranar da zamu zauna da ke da kuma kakarsa da shi kansa mu nemo mafita a abubuwan kunyar da ake tafkawa, watau ita ta take dikar mijinta ta kuma kyamaci talaka, ke kuwa kin biye mata kin yi naki rashin kunyar kin nuna mata bakya son danta, shima uban tafiyar baima nuna ya yarda cewa mace aka bashi ba ko?, Ba damuwa lokaci ke raba gardama, rai dai da lafiya, ama da mamaki idan aka wayi gari kowa ya manta wanene