Showing 36001 words to 39000 words out of 145392 words

Chapter 13 - NI ZAN LADABIH COMPLETE DOCUMENT By Sajida Nijar .txt

13 Dec 2024

8152

da kallo irin jan man da ta yi


Ajiyar zuciya ya sauke ya mike ya rage karfin ACn sannan ya dannan yadda zai ringa yin sama da kasa kar ya kafe waje daya , ya dawo ya sake gyara masa kafafuwansa yana ta dan matsa kafafuwan dan so yake ya gane idan sunna da kumburi ko basu tasa ba


A hankali ya rufa masa bargonsa sannan ya mike da nufin barin dakin


Muryarsa ciki ciki, dan har ta shake ya ce" ABDUL RA'UF"


ABDUL RA'UF ya dakata, ya juyo ya dawo yana kallonsa da sauraronsa


A sanyaye ya ce" Kar ka aikata aikin dana sani, kar ka saketa ko me zaka tarda ka ji?"


Fuskar tsogon yake kallo da daraja tamkar ta mahaifinsa
*Saki, ko me zai tarda,* yake ta maidawa zuciyarsa
Wai dama auren da wannan yarinyar ne aka daura masa?
Ya sake tambayar zuciyarsa


A hankali ya sakarwa tsogon tatausan murmushi, dan ya kwontar masa da hankali sannan ya juya ya sake ficewa


Ja ya yi daga sama ya harde hannayensa yana hangen dan karamin meeting din da ake yi a falon


Maganar kakansa cikin fadansa ne ta fado masa a rai , inda yake cewa wace yake nema din bai is ya aura ba sai wace ya aura masa ta yarda
Murmushi ya samu kansa da saki a saman lebensa
Oh ahalinsa na shagalinsu
Watau su a duniya kowane idan ya tashi yakan yi abinda yake birgeshi ne da rayuwarsa, ba ruwansu da nasa ra'ayin ko nasa burin, babu ruwansu da bin nasa tsarin


Wani murmushin ya kuma yi yana gannin yadda abokin Baba ke masu fada hadi da nasiha, a haka jama'ar da hajia ta gayato ke dan raragewa domin da yawa dama da abin hawansu, wa'inda basu zo da abin hawan ba kuwa mota na jiransu


Ji kake yi tsitt Hajia babu rigima da koke koke, gaba daya kamar an yi ruwa an kafe ta yi shiru kamar bata wajen
Kawayen natama wasu tunda baba ya mike suka fece, sun san hali da zaki ya yi barci ne suke neman yin wasa da gashinsa
Dayar dai itace ta tsaya, watau Uma, itama gaba daya jikinta ya yi mugun sanyi kamar an zare mata laka


Umarnin da Baba Rabi'u ya bada kan ta raka Hajia dakinta ta dawo ta tafi gidanta ya saka suka mike Uma na rike da ita suka shiga haurawa


A hankali ya ce da Hajia, dan ya san wacece ita, shirunta ba yana nufin ta dauka daga abinda ta hau bane, yana nufin tana kaunar mijinta ta kuma dan waye shi, yana nufin komai abinta idan ta taboshi takan yi laushi, ya san wacece ita a kak kafiya a abinda ta yi niya, dan haka ya ce" Hauwau, dan Allah kar ki yi abinda zai daga hankalinki ta kowace fuska, ki rike hakan a matsayin kadara da abinda Allah ya hukunta, ki bar yaran nan su shirya kansu, idanma da maganar aurensa ku barni da shi Aliyun idan komai ya lafa zan tado masa fa maganar tunda ai ya san da ita, tsohuwar magana ce, da ba dan shi din Abdallah din da kansa ya nemi da a dakata ba ai da an jima da yi, dan haka ku kiyaye kun ji?"


Ita dai kai ta gyada masa, idannuwanta suka sake sauka a kan Amina da kanta ke hade da gwuiwarta , babu wanda ya ji muryarta ko ya gane abinda take ciki, tunda Baba ya fara fada da ta yiwa kanta haka bata kuma dagowa ba, a yanzu haka babu wanda ya san halin da take ciki,


Kai ta dauke suka idasa haurawa


Kasancewar hankalinsu a gaba basu lura da tsayuwarsa a barin dakin Baba Mai Shanu ba suka yi bangaren Hajiar




A hankali ya sake juyowa yana hangen Baba Rabi'u da kuma yarinyar nan




Kai ya sake girgizawa ya dago hannunsa dake maiko maiko da warin Man ja ya zubawa ido








Page 1 bayan free🥰🥰🥰🥰
*NZL PAGE1️⃣4️⃣*












'shin su basu damu da nawa ra'ayin bane? Basu gane an kawo lokacin da namiji ko mace take da damar rairaya da tankada dan su dauki abokin rayuwar da suka gamsu zasu iya rayuwa fa shi duk rintsi duk wuya ba?, Shin yaya Baba yake tunanin shi ABDUL RA'UF UMAR FARUK ALIYU UMAR FARUK zai iya gabatar da rayuwar da mace zata bashi dama kafin ya dauki wata macen idan har yana ra'ayin hakan? Yaya suke tunanin shi din nan zai iya wata rayuwa da fitsarariyar nan?, Ganninta na farko da ya yi ana dambe da ita a wajen aikinsa ga yarenta masu kuka, na biyu da harare ta bi shi bai san me ya yi ba, na uku sun tsaya a bakin titi da kato yama zata mijinta ne Lukman ya watsa mata ruwa sakamakon tare hanyar da suka yi ga gefen hagu dinsu babar mota ce da ta shigo titin sosai, shigarsu ruwan ya zama wajibi ne ama ta kama masifa bata ko jin ta gaji harda jefa dutsi da yin Allah ya isa, sai yanzu da ta kwala masa kai uwa birgin bulo, ta cakumar masha riga da kazanta a hannunta karshema wai shi ta daga hannu ko zata yi menene ? Allah masani,itace aka daura masa?, Tabdijan'
Dan kara saukowa yake yi yana sake kallon Baba Rabi'u da ya dage yake magana ba ko hutawa, har ya gama yana shirin tashi biyu suka shigo , Husaini yana aikin da ya saba, watau ciye ciye, hasan kuwa hannunsa daya a cikin aljihun shadarsa, dayan kuwa na reto kadan suka nufo wajen Mamansu dake zaune Husaini na fadin" Mama tsaya ki ji, tun kafin ya fada maki karya, na ranste da Allah bani ya yi, nace bana so, bana so ya dage ,karshema yace mai mayar da hannun kyauta baya dan wuta ne, sai kawai na amsa, kafin na kawo miki ne dai na dan bude na taba kadan, kai Hasan tsakaninka da Allah ba haka aka yi ba?"


Hasan din ya wani maka masa harara yana cicijewa ya ce" Ka kuma ce min karya sai na fala maka marin mutuwa a gidan nan, sa'anka ne ni wai? Baka wani kin karba ba, na farkonma kana mika hannu kana kallona ne kace Mama ta hanna, shi kuma yace ai Mama amarya ce bata son rigima ba zata yi maka fada ba, sai kawai ka amshe ka kama ci ko wanke ledar ba zaka yi ba, kai dai ka ji kunya!"


Baba Rabi'u na dariyar fadan biyu da baya karewa ya ce" Kun ga, yanzu dai ku je wajen Inna tana baya tana kiranku inaga ko me zata ce maku?, Ku je cen daga nan sai ku buga ball kun ji?"


Da sauri Husaini ya fara juyawa, Hasan kuwa mamansa yake ta kallo , gannin tunda suka shigo bata dago ta kalle su ba sai ya ji ya kasa motsawa


A hankali ABDUL RA'UF ya dan sake gyara tsayuwarsa yana karantar yaron


Har Hasan din ya juya ya dan fara tafia, sai kuma ya ga ya juyo ya dawo daa hanzari ya duka kusa da mamansa ya saka tafukan hannayensa biyu yana dago fuskarta


Abinda ke jikin fuskar nata ya sinsina sai kuma ya yi murmushi ya kalli Baba Rabi'u ya ce" Har gabana ya fadi na zata kuka take yi"


Baban kansa sai da ya ji abin a zuciyarsa, yaro ne fa karami Hasan, ama irin yaran nan masu nacin uwa
Dukkan motsinta a jikinsa a ransa, a bayane zaka ga shi din mai bata kariya ne duda karancin shekarunsa, dan uwansa kuwa a bayane zaka fahimci mai bukatar a bashi kariya ne a dukkan al'amarinsa


A hankali ta dafe hannunsa muryarta cen ciki ta ce" Fadeel tafi mana"


Sake tsura mata ido ya yi, sosai ya so fasa zuwan, sai dai daure fuslar da ta yi ya saka shi mikewa ya tafi yana waigenta


Babanma sake mikewa ya yi yana jadada mata kalmar biyayya da hakuri, in sha Allah zata ga ribar abin


Ita dai bata ce da baba ufan ba har ya fice a gidan shima
Ta jima tana kallon waje daya, sai kuma ta mike tana dingisa kafarta da ta yi tsami ta nemi nufar dakin da aka bata dan ta harhada komatsanta ta san inda dare ya mata tun yau, ba da ita ba wannan rigima, ita? Ina ba da ita ba!




"Ke zo nan" ya fada a kausashe yana saukowa gaba dayansa ya nufi babar kujerar dake falon


Wani wawan birki ta ja ta ci, ta juyo a haukace cikinta na curewa waje daya


Daga sama har kasa ta debo dubansa ta sauke masa kafin ta yatsina fuska ta juya da nufin tafiyarta


A kausashe yana tsatsareta da kakausan kallo, muryarsa na kausasa ya sake fadin" KE ZO NAN NA CE!"


"Ba ke sunna na ba malan, sunnana AMINA!" Amina ta fada bayan ta juyo ta dafe kugu da hannunta na dama zuciyarta na tafarfasa tana sake kallonsa yadda ya wani hakimce


Hannunsa ya watsa irin du dayan nan , da idannuwansa ya yi mata nuni da wajen da yake nufin ta zo ta zauna


Sosai ta zo yin tafiyarta, sai dai wani tunani da ta yi cewa ta yiwu ya sawake mata ta kama gabanta ya sakata dawowa ta zauna, ama ba a wajen da ya nuna matan ba tana kafe waje daya da ido


Sai da ya sake kare binta da kallo yana ta nazartarta, yannayinta, girman fitsararta ( bai san a kansa kadai abin ke tashi ba ), sai kuma ya kada kai a rarabe ya ce" Kin san bana ra'ayin haka , gana daya hadin bai yi maching ba ko?"


Amina ta juyo tana kallonsa, kallo daya ta masa ta dauke idannuwanta tana fadin ' Ni da kaina abin ya kasa zaunar min a cikin kwakwaluwana, wannan wani irin gaurayen abinda basa kamanceceniya ne?"


"Ko?" Ya fada yana dan dage girarakinsa biyu


"of course, menene ke damun Baba fisabililahi da zai tashi ya dauki kannin bayana ya bani a matsayin miji?" Ta fada wannan karron tana kureshi da manyan idannuwanta
Wani irin haushi idannuwansa ke bata, irin kallon kasa kasan nan kamar tsohon kwarto ke bata haushi, bayan shi din bai tafasa bama bale ya kone, irin yadda yake yin kallonsa ke matukar kume mata zuciya da wuya, haka ta yi ta babatun magana a office dinsa ta zatama kurma ne ashe wai yana ji dan tsogon wulakanci da yarinya, ai sai ka yi fito na fito ka rama abinda na fada maka kau?


Da haushi haushi ta juyar da kanta tana son jan tsaki, domin har ta hade labanta ta basu kalar turowa kamar za'a saka ribom tana shirin bude su kadan dan iskar da zata samu hanyar shiga ta tsakankanin hakoranta dake cije ta samu hanyar shigewa ta bada amon tsakin ta ci ya ce" Kin san tsaki raini ne, bai dace ka yiwa danka bama shi ko AMINA?"


innalilahi wa inna ilaihi rajune, yaron da ya dace ya kireta da aunty ne yau ta yi faduwar tasar da wannan raini mai zafi ke shiga tsakaninsu? Shin me ta yiwa Baba ne? Du datijan dake zagaye da shi ya gaza dauko daya ya bata sai jinjirin da bai wuce goyo ba? , Shagwababen gaban kaka wanda a kansa kakarsa sai ta tada duniya? Uhum, dama Hajia ta kwontar da hankalinta, da ta daina daga hankalinta a kan abinda ba zai kai gobe ba!


A kausashe tana mikewa tsaye ta dube shi ta ce" Ka san a kan mutuncina babu abinda ba zan iya yi ba, kudinka ko masu tsaronka ba su zasu hanna na rama ba idan na ga za'a wulakanta min girmana ba!, So kawai mu mutunta junna kowa ya tashi da mutuncinsa, ni dai ka san na girmeka nesa ba kusa ba, rashin sanni ne ya biyo ta nan da mu, yanzu da aka sani farar takarda sai ta sameni a ciki, bana son sa in sa da kai, domin ba mutunci bane ka gane ai!"
Irin ta yayaba maganar nan, tana jira a yayaba mata ko ta samu ta sake amayar da takaicinta ta huce, sai ya karra tafka mata abin haushin nan ya sake yi mata shiru kuma yana kallonta


Walahi kamar zata fadi ta saka ihun kula ta kama bori daga nan har bakin titi
Wayo Allahna wulakancin dan Adam, dan tana talaka? Dan tana marainiya za'a yiwa haka?


Juyawa ta yi da karfi karfinta ta nufi ciki, sai kuma ta dawo wuuuuuu ta warci dan kwalinta da ya fadi a kasa ta yafawa kafadunta ta sake hararar gefen da yake zaune ta kuma wucewa cikin dakin nata


Murmushi ya yi ya maida kansa baya yana lalubar wayarsa dan ya kirayi direbansa ya zo ya kaishi gida ya yi wanka ya cire kayan maikon nan ko zai dawo cikin hayacinsa, ji yake abin na kama wuyanda sosai walahi, to ita du mayukan duniya ta rasa na shafawa sai wannan?


Kai ya sake girgizawa kasa kasa ya furta" Yarinta kennan, kanwar hauka, Allah ya sa kar na karya y'ar mutane kafin na salameta" ( na shiga uku ni sajidede)


Amina na shigewa dakin ta ja kofar ta rufe da karfi sannan ta dora hannayenta bibiyu a saman kanta ta silale a jikin kofar a hankali kuka mai daci na neman kubce mata ta ji wata zazafar dankwasa ta sauka a dandin kanta


Da sauri ta dago gefen da ta ji abin zuciyarta na yankewa da faduwa da tunanin ko biyota ya yi ta rufe dakin da shi? Harda fargabar ko shine ya rafka mata dankwasar nan? To abu da yaro babu abinda ba za'a gani ba, sai ta ga Baba Lauratunta tsaye a kanta tana yi mata harare irin na fil'azal , harare na usulin kwararru a fannin juyar da ido bakin dake cikinsa ya bace bat farinsa ya tsaya yana mata mar mar mar


"Ke yanzu in banda mayar da kai shashasha da neman fitina yarinyar nsn tunda na shafa maki abin nan kika bace min da azuminki a bakinki sai yanzu zaki shigo? Ina kika je kika zauna sai yanzu zan ganki ta nan? Ni me kike son mayar da kanki ne Amina? Gyaran nan inace ke kika koya min kin fini sannin yaya ake yinsa, shine zaki dauki kafa ki je cikin mutane a haka? Kin ganki kuwa? Kin ga da abinda kike kama? Daga ina kike ne?" Baba lauratu da ta biyo ta hanyar nan dan ta katse balin Aminar, domin abubuwan da duka faru babu wanda bata gani ba, karshema da ta ga rigimar ta koma tsakaninta da Sarkin samarin ne ta yi wuf ta shige daki dan ta san daga cen nan zata biyo, domin ta sani ne babu wanda zai risinawa dan uwansa a yanzu


Amina dake dafe da kanta ta wani langwabe kai hawaye na ziraro mata ta ce" Aya, da kin san abinda na jiyo da sai kin yi takaicin bata naira dari ukunki wajen siyo madarar nan kika hada abin nan kila shafa min, da kin san abin kunyar da ya tunkaroni da kin tayani kuka Baba"


Ikon Allah, Baba ta ayana a cen kasan zuciyarta, koda yake tunda Amina ta wayo gari da kula da kanwarta, da aurar da kanwarta, da rainon biyu ta dauki girman duniyar nan ta dora daman kanta, Amina kamar ita ta yankewa kasa cibiya, a kulun maganarta itace ka samu dan datijonka ka aura ka je ka yi zamanka, sai ga wayewar gari an tashi da Amina da auran yaro kanninta? Shekara fa bata fi daya da ta bashi ba in ta cike dayanma, kuma Aminar in ba karfin zuciya irin tata ba aa hadiye sai Abdul Ra'uf ya hadiyeta da yawun bakinsa ko asuwaki ba zai yi ba bale maganar kora ruwa kar a shake, ita mamakinma fa ta yi da take masa kallon yaro bayan a cike yake kuma ya ajiye saje irin na samari masu ji da kansu da tsafta suka kuma tada kai da yayan banki suka yi asuwaki da kafar dawisu!, Ta yiwu dan shirunsa, da bada amsarsa da murmushi irin na kililin kasau majicin kumba ne ya sa take saurin haye masa? Da ta san sari ka noke yake yana iya zuba mata gubar da zata kaita ga halaka da ta bi komai a hankali ta yadda zata kai ga ci ba tare da ta jigata ba


A sanyaye Baba Lauratu ta ce" Allah ya rabamu da abinda kike fada Amina, Allah ya nisantamu da kunya da abin kunya, meye abin kunyar a ciki?"


Amina ta ringa kallonta, kallo irin na son fahimtar ko ta san abinda aka yi mata ne?
A hankali ta ce" Baba, Hala kin san yaron cen aka aura min?"


Sai da baba ta kama habarta, sai kuma ta ce" Ki maida hankali, kin ji? Nace ki maida hankali sosai ki ringa yiwa lamarin nan muguwar fasara ta yadda bakinki zai tabo maki rigima danya, ke yanzu in ba abu irin naki ba mijin naki zaki ringa cewa irin haka? To ki hanzarta hawa ki tarda Mai Shanu mana ki ce masa kul kar ka konani ka kona kanka bana so ka kashe auren nan dan fitsarariya ce ni komai zai iya faruwa , nace ki je ki same shi a cen sama bashida lafiya ki tashe shi ya yi abinda kika yanke kar ya barki da abin kunya!"


Sosai Baba abin ya kular da ita, gani take yi wannan din ai rashin hankali ne da rashin sannin ciwon kai
A kaikaice take yaba mata magana da fada da sharar fage, domin tana yi mata fadan ta ce da ita" Tashi dan Allah ki shige ki wanke abin nan da sabulu da soso dan kin bata min gyara ga na kwan na hada maza ki fito mu shafa, kin san dai na kwai ba'a masa wasa ko? Da yama zan koma gida kulun da safe na dawo dan dazu mai Shanu ya bada kudin siyayar nan na gyaran jiki dole zan je kasuwa na sisiyo , a kadan ma kusan wata muna yi fa, tashi tashi tashi bana son bata lokaci!"


Walahi sai Babar take neman cenza mata a idannuwanta da tunaninta, gyara na kwai? Yaushe ta samu kudin kashe kwaya kwayan yin gyara irin na kwai? Kwan da a kadan a kashe goma cikin madara da kurkum a murje jiki gaba daya da shi shine tace ta hada hadin? Ita kuwa kudin zata lalata hala a wannan abin?


Har ta shige

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login