Showing 45001 words to 48000 words out of 145392 words
Chapter 16 - NI ZAN LADABIH COMPLETE DOCUMENT By Sajida Nijar .txt
Ke haye kika yiwa abin dole ya gigitaki!, Zaki gane cewa da ka haifi gwamna da matar gwamna gwara ka haifo matar gwamna!, In dai mice yar gifan Badasi fulasta sai na rabaki da ABDUL RA'UF kina ji kina gani daga ke har tsinaniyar da ya aura din!"
To fahhhhhhhhh ana dara ga dare ya yi.......wata cakwakiyar wata rigimar, fitina kala kala,
To kai da ka yanke lokacin kawo aurenka AMINAR ta yarda ne?🚶🏻♀️🚶🏻♀️🚶🏻♀️🚶🏻♀️🚶🏻♀️🚶🏻♀️🚶🏻♀️
Uhum ku mu je mutanena🥰🥰🥰🥰
*NZL PAGE1️⃣7️⃣*
Ya dan karra kamar minti goma yana sake amsar kalaman soyaya har ya ji kansa ya fara daukan caji sannan ya mike da niyar tafiya
Kamar yadda ya saba baya zuwa gidan bai bar kyauta tautunci mai saka farin ciki ba hakan ne yauma, ya ajiye chek ba dan sunna cikin rashi ba ko wani abin, ya sabarwa kansa irin haka ba dan a so shi dan hakan ba, sai dan ya kasance mai yin kyauta a kowani hali, ba iya su yake yiwa irin hakan ba, nasun dai na zuwa ne da karrin jadada mutuncinsa
Har bakin mota ta rako shi, bayan ya bude ya shiga baya ya zauna ya waigo barin da take tsaye tana murmushi
Murmushin ya yi mata a hankali ya ce" Kin tabata kin daina maganar shagon ki?"
Sai da ta yi dan tsai, sai kuma ta gyada masa kai da sauri, dan ta san ko menene mahaifiyarta da ta fi kowa tsayawa kan maganar neman na kai ta kuma aikata haka da dalilinta, ta tabata ko menene zata samu gamsuwa idan ta koma yanzu, dan haka ta amsa shi da kwarai hakan ne
Murmushi ya yi a hankali ya furta" Good night an mata"
Itama murmushin ta yi ta ce" I love you My Man"
Sai da ya lumshe ido da kalar nasa salon sannan ya furta" Me too"
Daga haka ta ja baya kadan suka tayar da motar suka fice da mota uku cif masu kudi na garari, yana tafe da yan rakiya ne dan ya tabata zasu cika dare a yawo yau, domin daga nan kauye suka nufa da daren nan kuma a cen zasu kwana
Tana tsaye sai da suka bacewa ganninta sannan ta sauke ajiyar zuciya ta juya tana murmushi, sai kuma ta cire hijab din tun daga tsakiyar gidan ta shiga dan gudu gudu ta shige falonsu
Hango mahaifiyarta zaune da chek din da ya ajiye a gefenta ya sakata karasawa da gudu ta rungume maman nata ta baya tanaa daria ta ce" Thank you mama, thank you love, ni na san zaki so shi, ni na san babu wanda zai ki ABDUL dina Mama, ni na saj zaki so shi watarana"
Uwar ta yi murmushi tana janyota ta gabanta kamar wata yarinya karama ta ce" Ba tsanar Abdul dinki na yi ba baby, wasu halayarsa na iko na tsana!"
Risalah ta ce" Mama, ki masa uzuri da maganar ikonsa, yana da damar yi mama, ki masa uzuri, ni kam ikonsa na daya daga cikin abinda ke karra sakani sonsa a zuciyata Mama "
Baki ta tabe ta dauki takardar ta sake duba kudin,
Kafadunta ta dan daga, ba maganar godiya ko nunawa yar ya yi bajintar da ta isa a gode masa, dama bata koya mata haka ba, ko duniya zai bata bata koyaa mata gannin wani abin a zo a gani ne, yau ta fara kama kudi ne? Yanzunma hakan take a dan takaice da isa da basarwa da nuna kudin har wani abu ne ta ce" Za'a karra injinnan gyaran jiki a saloon dinki da kudin nan"
Tsare uwar ta yi da kallo ta ce" Saloon kuma? Inace kin ce an daina?"
Da mamaki ta kalleta ta ce" An daina? Why za'a daina?"
RISALAH ta ce" Mama yanzu fa kika cewa ABDUL an daina ?"
Yatsina fuska ta yi ta ce" A daina? Kina bani mamaki Risalah!"
Da wani mamakin ta budi baki zata sake yin magana uwar ta daga mata hannu ta ce" Look, ki ci gaba da nuna masa abinda nace muna kai a kawo a daura auren, kafin a daura auren ki tare kanwarku zatana zuwa saloon din ta kula da shi, idan kika zauna a gidanki kika mayar da ABDUL mutun ya zamto ba zai iya rayuwa ba sai da ke sai ki koma bakin aikinki ki nemi kudi Hajiata, idan baki da shi ko a cikin yan uwanki kece koma baya bale a duniya!, Ki rage kulafirci da shirme a kan da namiji!"
Tana gama fada ta mike ta haye da takardar kudin, ita kuma ta rakata da kallo
Sosai hudubar ta shigeta, da kyau kuma ta rike a ranta cewa dan ta yiwa Abdul karya dan ta samu cinma burinta ba laifi bane!, Haka kuma kudin nan da ya ajiye bata bishi da kalmar godiya ko Addu'a ba, daga naa wayar ta dauka kawai ta shiga tura masa kalaman soyayar da ta san da wahala ya mata replay ko ya bata amsa a takaice kamar haka" Thanx "
Ama bata damu ba, ta san yana sonta, shi kawai ka barshi da nauyin bakinsa ( uhum hajiata ana yiwa wace bata isa bane nauyin baki walahi!)
Yana zuwa gidan kakanin nasa sai da ya kusan minti goma sha biyar da ma'aikatan gidan sunna dan zantawa, bale mazan, matan da Hajia babar ma'aikaciyar gidan kawai suka zanta
Sai da ya gamsu da komai sannan ya shige ciki
Tunda ya shigo ya ga wayam ya samu kansa da sakin murmushi da tunanin kennan ba'a shirya ba tunda ba'a zaune a falo kallon dare kamar yadda aka saba
Juyawa ya yi ya nufi hanyar hawa ba tare da ya kallo bangaren dakinta ba , kai ko a kansa hakan bai shigo ba sam
Muryar Farid dake rusa kuka ya saka shi dan saurarawa da fara hawa ya yi tsai da tunanin kukan yaro kuma?
Har zai sake hawa ya jiyo magana kamar haka "Wayo Allahna na shiga uku, Mama idan kika zane shi hala nima zaki zane ni? Mama dan Allah kar ki zane mu , ni jikina ruwa yake yi ya yi ta ciwo shi yasa bana son duka!"
Muryarta ya tsinkayo tana fadin" Malan yi min tsittt da bakinka ko na farfasa maka jiki, kai Hasan zo nan na ce, yau zan ga uwar taurin kai da rashin ji a gidan nan, ba dai kulun a kan haka zamuna yin fada da kai ba? To yau jikinka ne zai fada maka!"
A hankali ya saurara ko zai ji muryar wanda ya tabbata wannan yaron ne mai zuciyar nan, watau wanda ya birge shi a ranar da suka watsa masu ruwan kwata,
Sai dai jin shiru ya saka shi dan juyowa a hankali ya sauko kafarsa daya ya kara saurarawa
Jin karan saukar bulala da fasa ihun Husaini ya saka shi karra sauka da dan sauri ya karasa bakin kofar ya dan saurara yana son jin da gaske dukan yaron ne take yi ko me?
A lokacin ne ya ji muryarta a hankali tana fadin" Ba zaka fahimtar da ni ubanda kake aikatawa a ajin ba ko Hasan? Watau ba zaka yi magana ba sai dai na kasheka ko?, To yau ni da kai a ga wanda ya fasa, kai kuwa Husaini idan bakinka bai min shiru ba sai na fafasa maka shi a wajen nan"
"Wayo Allahna na kyale, Mama na kyale, Mama ki barshi haka kin ga baya wasa baya yin komai a ajin, nima ban san me yasa yake zuwa na buta ba mamanmu"
Sake jin saukar bulala da karanta a kam wanda yake tunanin ake duka ya saka shi dora hannunsa a saman abin budewar a hankali ya bude kofar sannan ya dan guara tsayuwarsa ya leka dubansa dan so yake ya fahimci abinda yake faruwa, haka kawai yake son daina jin saukar bulalar kamar wani wanda abin ya shafe shi
A tsaye take ta ba kofar baya, jikinta sanye da wando irin budaden nan sosai, domin iya kugunta kadai wandon ya rike kuma kalar ruwan madara ne, harda yar igiyarsa da bai san bata daure igiyar bane take reto ta tsakankanin kafafuwanta ba ko menene? Sai kuma rigar dake saman wandon ita ba budadiya ba ita ba damamiya ba, kuma hannu daya a yanke daya har tsintsiyar hannun, kanta sanye da hula ga bulala a hannunta tana rike da kugu da hannu daya ta saka yara a gaba tana cin zali
Daga bulalar ta yi tana fashewa da kukan da ya kusan sakashi fashewa da daria, domin tana dagawa doka masa zata yi ama fadi take" Au baka tausayina? Na dake kan ko? Na mutu ko Fadeel? Na dake ka ba zaka yi min magana ba ko fadeel? To bara na karra maka idan na farfasa maka jiki ai shikenan!"
Kukanta take yi bilhaki, ga kuma yaron jikinsa na rawa kuma yana so ya matsa jikinta ama ta ki bashi dama dan ta san idan ya rukunkumeta an kare ba zata dake shin ba
Shigowa ya yi gaba dayansa yana sake kare masu kallo , a makoshinsa ya dan yi gyaran muryar da ta sakata juyowa a zabure dan bata san da an shigo dakin ba
Ido ya zarro sakamakon yelow din kwabin kwan da ta shafawa fuskarta da tumaturi ya bushe mata ga kuma hawaye na zarya a kai
Hannunsa ya kai wajen bakinsa yana dan sake kallon fuskar da nan take yake karantar shirye shiryen tafka masa fitsarar ake yi
A hankali ya mika hannunsa wajen da Hasan ke tsaye bayan ya cire dubansa a kanta yana kallonsa bai yi masa magana ba, yana nufin ya zo wajensa, dan ya tabata yadda yaron ya cika hadiye harshe kalamansa na fita ne ta hanyar motsi da hannayensa ko yannayin idannuwansa
Da sauri ta saka hannunta tana share hawayenta hadi da rarumar hijabinta ta zurma a jikinta tana hade fuska ta ce" Malan ya haka da shigowa dakin mutane ba ko salama, Allah dai ya sa lafiya?"
Bai ce da ita uffan ba, a hankali ya sake rage tsayinsa ta hanyar dan dukar da gwuiwoyinsa kadan yana sake duban yaron da haka kawai yake ji yana so ya zo gareshi, sannan ya sake mika masa hannayensa duka biyu yana kallon fuskarsa da yannayinsa
Hasan din dake ta haki ua ya cira dubansa ya sauke a kan fuskar Mamansu da ta cire kai ta turo baki gaba yadda ka san wata yar baby ita ala dole fushi take yi ya sake kallon ABDUL RA'UF wata ajiyar zuciyar na kwace masa , ya kalli hannayen ABDUL RA'UF din da kallo irin na nacewar nan sai kuma ya sake sada kansa yana ta wani iri shi ba kuka ba, shi ba hakin summa ba
A hankali ABDUL RA'UF ya dantse lebensa na kasa yana sake kallonsa, bai janye hannunsa ba, haka kuma bai daina yi masa tausasashen kallon ba
Tun Hasan na cire dubansa a kansa har ya dawo ya tsayar da duban nasa a kansa, sai kuma fuskarsa ta ringa nunawa, a hankali a hankali ta ringa wani irin shagwababewa, a hankali kuka ya kwace masa ya daga kafarsa da sauri ya karasa ya fada jikin ABDUL RA'UF ta hanyar shigewa cikin hannayensa ya rungume shi a cikin kirjinsa yana murzar fuskarsa a gaban rigarsa
Daga ita har Husaini ido suka zarro na mamaki
Matsanancin mamaki ne ya kama su na gannin a yau Hasan hankalinsa ya kai kololuwar tashi ya doshi wani mutun daban dake bako a gareshi
Shi husaini kasancewarma tsoron mutumen nan yake tunda ya ganshi sau biyu baya masa fara'a na farko a office dinsa, na biyu a bakin layi ya sa ko a yanzu da ya shigo da sauri ya labe a bayan mamansa , gwara maman tasa ta masa dukan mutuwar kawai da wani bako ya daki banza!, Sai ga Hasan, Hasan dai Fadeel nasa, Hasan na gidansu ya rungumi wannan mutumen marar fara'a
A hankali yake shafa kansa da ya fara tara suma yana jin kukan yaron a ransa
Idannuwansa ya dago dake risine a bayan yaron ya sauke mata duban da zata fasara na ta ji kunya ne? Ko kuma shashasha ne? Ko irin kamar ta sato ɗan nan ne? Ko na zalinci ne? Ita dai duban gashi nan kala daban kamar na wata yar kidnaping, bayan shi din nan ba dansa bane, ya tardo mace da danta ya yi mata ba daidai ba? Lalle yaron nan ya cika raini da wulakanci ! Abinda take ayanawa a zuciyarta
Bata ankara ba ta ga ya mike tsaye da Hasan ya daga shi sukut a jikinsa ya juya mata da ɗa zai tafin mata da danta
Daga iya har Husainin ji suka yi kamar za'a tafi da rayuwarsu ne, dan haka da sauri ta biyo shi daidai ya sake bude kofar zai fita tana fadin" Ya haka wai, bani dana mana Malan!"
Dan dakatawa ya sake yi ya juyo yana kallon fuskarta hadi da yatsina nasa fuskar, domin walahi karnin abin ke dukansa, shi ya rasa me ke damun yarinyar nan da take yaba abubuwan wari a jikinta haka, meye anfanin abubuwan nan ne? Wannan din dake jikinta sai wani iri ya mata da ta sha kukan ama bata kyankyami tana wani dakewa da fuskewa abinta
Wajen da takardu ke ajiye biyu ya kai dubansa
Da Hasan din a kafadunsa ya juya ya dauki takardun sannan ya janyo kofar ya rufe ya yi gaba da shi a jikinsa ya nufi sama wajen Baba
Amina dake ji kamar zata haukace dan gannin ya fa tafin mata fa yaro sai da suka bude suka fito ita da shagwababenta, sai dai inda ta ga ya haura da ɗan ya sakata komawa tana sakin ajiyar zuciya tana rike da hannun Husaini taf a hannunta suka zauna a jikin kofar Husaini ya kwontar da kansa a hankali jikinta yana fadim" Mama Hasan fa? Zai dawo ne?"
Kai ta gyada da sauri murya a rarabe ta ce" Zai, zai dawo, zai dawo in sha Allah, muna jiransa zai dawo ka ji? Mu yi jiransa a nan"
A hankali ya saka hannunsa ya tura kofar ta Baba sannan ya shiga da salama
Tunda ya shigo gabanta ya kwonci kwonci ya fadi abinda ta gani a rungume a jikinsa
*NZL PAGE1️⃣8️⃣*
Tunda ya shigo gabanta ya kwonci kwonci ya fadi sakamakon abinda ta gani a rungume a jikinsa
Kureshi ta yi da ido, dukkan farin cikin da ta kwasa na rarashin mijinta da ta yi da kyar ya saurareta suka sasanta kansu, da kuma jin dirar motocinsa ya nemi bacewa battt
A hankali ta sauke dubanta a wajen da ya ajiye yaron da irin zaman da yaron ya yi sai ajiyar zuciya yake saukewa ga dukkan alamu kuka ya sheka ko meye oho
"Aa, subahanalah wannan kamar mai tsuntsaye na hadiyar zuciya, Abdallah ina ka samo Mai tsuntsaye haka ne?"
Takardun ya ninke ya ajiye gefen kujerar shima ya zauna saman kujerar yana kallon kakanin nasa irin zaman da suka yi ya nuna masa sun shirya
Baki ya tabe yana girgiza kansa da ya tuna irin bali da jama'ar da suka tara masu har ana wani ririke su gaba dayansu
"Hum" ya fada takaici na tiko shi, yanzun du irin abinda suka raba da tataro mutane dan a shiga tsakaninsu a yiwa daya magana ana wani rike su sunna iface iface bama kamar Hajia har ya wuce sun mance? Ah to su sun mance sun rabawa duniya abin fada sun dinke abinsu a daka, uhum
"Magana fa nake yi bawan Allah nace ina ka samo min mutumen ne na ga hankalinsa tashe?"
A takaice ya ce" Wajen mamansa"
Sai da ta kusan zabura a bayane, sai kuma ta dane kanta tana kallon ABDUL ddin da son su hada ido hudu da shi dan ta fahimci abinda yake nufi ama ya gagara, domin kiri kiri ya wani basar kamar bai san abinda ya fada da bakinsa ba
Sai da ya gama shan kanshinsa shima yana gannin yadda kakansa ya taso ya kama hannun Hasan suka koma wajen zamansa ya raba yaron a jikinsa yana ta yi masa tambayoyin da yaron ya ki fadin koda A ne a cikin tambayoyin yana ta hakinsa dai
Gaba daya abinda ya dan birge shi irin yadda hankalin Kakan nasa ya ki kwonciya a kan lamarin yaron,
Murmushi ya saki a ransa yana ayanna ' Bafa zai yi maka magana ba, gwarama ka kyale shi'
A bayane kuwa a dole ya amshi gaisuwar kakarsa da take ta tankwalowa ya shiga gaishe su gaba daya harda su tambayat yaya Risala? Ya bata amsar tana kalau.............,
Hajia ta gyada kanta tana sake kallon yaron da ya tsaya mata a wuya , si take ta yi tambaya, sai dai tana tsoron amsar da take iya samu a gaban mijin nata, bale yanzu suka gama sasantawa da kyar da walahaula da jibin goshi
ABDUL kuwa kallon kakansa yake yi har ya ga ya dan rabu da tambayar yaron abinda yake damunsa dan ya ki ya yi magana
Maganar anfanin gonar ya fara daukowa yana masa bayani a kan nomar da suke yi da talafin sababin kayan aikin da suka kawo, sunna yin noma ne irin na kasashen da suke da karancin wadatacen ruwan sama ama kuma babu wanda ya kaisu kayan alatu da na anfanin abinci domin sunna anfani da ruwa a lokacin da ba na damana ba su yi noma har su samu anfani mai yawan gaske da kuma gardi,
Baba Mai SHANU ya dafe haba yana girgiza kansa ya ce" ABDUL RA'UFu, anya kuwa wannan anfanin gonar yana da inganci kuwa? Kai zamani na tafe da abin tsoro, yaushe za'a yi noma ba lokacin damana ba?"
Yar dariya abin ya bashi domin haka suka sha da mai garin da gonakinsa suke , har jiya da ya bugo masa waya haka yake salalami yana fadin dawa ta yi tsayi har ta fito? Jama'a hatsi har ya yabanya? Tumaturi kwonce rututu jajajir rudu rudu? Santin abin dai ba'a magana, wai anya kayan nan ba cutarwa a cikinsu?
Zamansa ya gyara yana fadin" zaka sha mangwaro a rani kuwa bana Elhajin Hajia"
Murmushi Hajiar ta yi tana hango lamarin, gaba daya a kasar fa yanzu shi kadai yake da budaden kampanin da zaka samu kayan masarufi sabon fita ba dadadiyar ajiya ba, da farko da ta ga yana da nacewa a kan nema ta hanyar nan haka zata saka Mai SHANU a gaba da rigimar ga sana'a su gwal , su waye waye ama ya nace noma da wani kiwo