Showing 39001 words to 42000 words out of 145392 words

Chapter 14 - NI ZAN LADABIH COMPLETE DOCUMENT By Sajida Nijar .txt

13 Dec 2024

8163

bayi tana waiwayen Baba da ta hade gabas da yama, kudu da arewa take jira ta sake daga mata hankali, wankan ta shiga tana tunanin ran Baba ya baci ne dan ta tafi yawo da kurkum a jiki, ta tabata idan suka zauna ta yi mata dala daka zata rakata wajen babban da kanta, dan haka sai ta shiga yi din


______________________________________


Hannunsa yake dan karra sinsinawa dan ji yake yi du irin wankan da ya yi warin man jan nan akoyshi a jikinsa, shi dama baya cin man ja , jin warinsa yake yi sosai har cikin kansa
Du irin uban turaran da ya yiwa kansa wanka da shi shi kam yana jin warinsa a hancinsa


A nutse yake tafia dan zuwa wajen dining ya dauki coffee ya sha, domin ba zai iya yin barcin a yanzu ba, kansa ya fi komai caza shi a irin wannan lokacin , baya son dogon tunani sam


Idannuwansa ne suka sauka a kan MANSUR da RISALA dake zaune a falon
Shi MANSUR din shi yake kallo da wani expression a fuskarsa, ita kuma tunda ya sauko ta sada kanta kasa, domin ba zata taba manta lokacin da ta zuwa gidan nan ta tardoshi da kananun kaya sosai irin yadda suka lwashe ba, batama taba gannin namiji mai shegen jin kunyar suturarsa irin ABDUL ba


Dan sakw dubanta ya yi , hijab ne a jikinta , sai kafar wandon dake kasa da yake hange daga inda yake tsayen, sai tissu din da take ta faman murzawa wajen hancinta zuwa idannuwanta tana fyace hancin da buga hancin dan kukan da ta sha hancin ya done mata sosai


A ransa ya ayana ' Ya Salam, ranar nan gaba dayanta ta hade min da abubuwa sosai, RISALA ta ji ga dukkan alamu, mtssssssss ni kam ba zan iya yin maganar yanxu ba'


Da hannunsa ya yiwa Mansur alamar yana zuwa sannan ya nuna masa gajeran wandon dake jikinsa ya juya ya shiga haurawa


Idannuwanta ta sake dagowa ta raka bayansa da kallo har ya bacewa ganninta


Wani kukan ta barke da shi tana saukowa daga saman kujerar, lokaci daya Mansur na kokarin tausarta da bata hakuri , zai fara magana wayarta ta fara kuka


Hannunta ta saka ta dauko dan ta zaci mahaifiyarta ce dake fada kamar zata ari baki tana cen gida tana bambamin sai me? Aure? ABDUL RA'UF din ne ya yi aure tun ba'a je ko'ina ba? Ta dage kan yarta ta rabu da shi ko shine autan maza, tana ta cin alwashin ai su irin kyau ne walahi karyane su yi tsawa, idan ABDUL RA'UF baya yi wani zai yi ta yiwu wanda ya ninka shi sau dubu!, In dai ita ta haifi yarta ta kare da shi, ba zai yiwu ta yiwa kato kuka ba!, Darajarsu ta wuce nan, bata san a irin wannan lokacin tuni yar ta silale ta sadado gidan dan ta fuskanceshi ba, bata san a yanzu daf take da rasa ranta ba, ta yaya mamanta zata yi tunanin zata iya rabuwa da zazafan gayen nan? Komai nasa baba ne, shi din baba dan baba ne, soyayarsa kuwa mai zafi ce, ajinsa kuwa zazafa ne, ita yaya zata iya soyaya da wani bayan ta dandana da shi? Ta sani ne ko wacece, ko y'ar gidan uban waye zata daka ta bara mata shi ne, idan me ta zo da shi gidan ta tarar, RISALA yar gayu sunnanta ya koma ko a kasar amerika bale a kasar hausa, in menene ta taka ta iya ta kware!, Ba zata taba sharing din Abdul ba sai dai ta rikeshi ita kadai, ko wacece ta shirya mata tsaf zata kuma gwabza da ita daga nan har duniya ta tashi in dai sunnada rai su dukansu!


Gannin hoton zuciya da jinni kamar yadda ta yi seving din numbersa ya sakata jikinta na bari ta daga ta kara a kunnenta hadi da saurarawa


A tausashe ya ce" RISLANAH, plz go, zan shigo gidanku yau, kin san na hannaki zuwa gidana? Nd yanzu bana iya doguwar maganar plz"
Daga haka ya katse kiran


Tamkar ya katse da numfashinta ne, domin mikewa ta yi tsaye da sauri ta juya wajen da MANSUR ke tsaye ta budi bakinta zata yi magana, sai dai ta gagara yi ta shiga jan maganar da bakinta da hancinta, karshema gaba dayanta ta rike gaban kirjinta ta kifa a wajen da take tsaye hannunta rike da kirjinta, idannuwanta sunna neman kakafewa.........








Ya Salam, anya baku dauki lamarin nan da zafi ba kuwa?


Happy wkdn mutanena🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰😊
*NZL PAGE1️⃣5️⃣*










Gaba daya Mansur ya mike tsaye daga zaunen da yake


A hanzarce ya karaso inda ta kife din, da irin abinda ta yi kafin ta ja numfashi ta dauke ya sake rikita shi


Hannayensa duka ya kai da niyar daukanta
Lokaci daya ya tsaya cak da abinda ya so yi din ya yi baya sannan ya juya da gudu gudu yana haurawa


Yana karasawa ya ringa doka kofar dakin ABDUL RA'UF yana ambataon sunnansa


ABDUL RA'UF dake idasa bala boturan rigarsa daga sama ya juyo da dan sauri yana sake saurarawa
Jin sunnansa a bakin Mansur ya saka shi takowa a dan hanzarce kadan domin irin yadda Mansur din ke ambaton sunnansa lalle zaka san ba lafiya ba


Yana budewa Mansur ya ce" Man, me ka fadawa yarinyar cen ne? Ta summa fa, ta summa?"


Har ga Allah sai da ya ji kamar kansa zai sarra, Innalilahi wa inna ilaihi rajune, shine abinda yake ambata a kasan zuciyarsa hankalinsa na neman tashi, gaba daya kansa ke sara masa, cofee dinma bai sha ba bale a kai ga hutawa kafin la'asar ta shige


'Summa kuma?' ya saske tambayar kansa


A dole ya fito ya bi bayan Mansur yana sauka a nutse suka nufi inda take yashe kafarta daya har a jirge dan bata fadi a daidai ba


Duban Mansur ya yi girarsa na karra hadewa sosai na ciwon kai ya ce" Summan ne kuwa wannan Mansur?"


Mansur ya dube shi, ya sake dubanta, a hankali ya ce" Na si na dubata da kyau duda ban fito da kayan aiki ba, to gani na yi iya din ba muharamata bace, sannan babu wani da ya bani damar hakan a makusancinta"


Kwarai Mansur yanada gaskiya, sai dai shi dinma ai ba muharamar tasa bace, subahanalah, shi yasa kwata kwata baya son irin abinda take son nunawa, ta tashi ya zo gidansa su cewa junna me? So take yi mutuncinta da yake gani ya daina ne? Me yasa ta cika naci a kan abinda bashida wani anfani? Menene ya sumar da ita ne?
Sai dai a yanzun ya zama wajibi su bata kula, abin takaicin a kasan hijab dinta wando ne dogo wanda a yanzu da ta fadin gayanan a fili a jikin kafarta ya bayana, shin me yasa yarinyar nan ke wasa da abinda yake dorata a kai? Shi yasa ya dakatar da maganar kai kudi gidansu, yana so sai ya gamsu da ita da tarbiyarta, ama a kulun sake baudewa umarninsa take yi


A nutse ya ce" Ya zama wajibi ka bata irin kular da ta dace ai Mansur, kai din likita ne, idan muka ce sai mun nemi muharaminta ya riketanma karshe kai din zaka dubata, ka dubata kawai Allah ya bata lafiya!"


Mansur ya yi gagawar fadin" To ai ka kamata mana, ina zaka je kuma?"


ABDUL RA'UF ya ce" Zan koma na sha magani ne nima, kaina ke ciwo, nd zafi nake ji har cikin idannuwana"


Da kula Mansur ya ce" To wa zai kama min ita?"


ABDUL RA'UF ya ce " Ka san ba zan iya tabata ba ko? Kai kana da damar tabata dan talafawa rayuwarta likita ne kai, ni fa?"


MANSUR dake ta kallonsa sai da ya ajiye wata ajiyar zuciya mai zafi, dan walahi yarinyar nan ta tsorata shi, kuma bai tabbata ba dan ya san waye abokinsa a kan matsalar kishi, shi fa yakan ce macen dake yafa mayafi wani kato ya kalla ya raya a ransa shi kam ya haramtawa kansa ita, yanzu haka a cikin rudun da yake da Baba Mai shanu ya sheda masa cewa ai maman biyu ce za'a aura masa, har suka je daurin auren a tare suka dawo yana cikin tunanin ra'ayi irin na ABDUL RA'UF, macen da ta auri wani har ta haihu aka aura masa ba da ra'ayinsa ba? Ya san abokinsa na son kakaninsa kamar ransa, ama kuma baya hada ra'ayinsa da na kowa ( kun san shima bai san cewa ba itace uwar biyu ba )


"Duda haka, ka tsaya kana tsaye mana, ka sani ko me ya summar da yarinyar nan yanada nasaba da kai, ka yi kokarin mutuntata kamar yadda ka saba, ka fi kowa sannin irin son da take yi maka, ba karya bane, ba kuma dan abin hannunka bane, so kuma ba karya bane "


A hankali ya karra juyawa ya kalleta
Idanuwansa ya lumshe, shi kadai ya san damuwar dake daskare a zuciyarsa


Dawowa ya yi ya zauna saman kafet din a hankali ya tankwashe kafafuwansa ya mayar da kansa baya saman kujerar ya lumshe idannuwansa


Mamaki ke neman halaka shi
*SO?*
Shima ai yana sonta! Sonta da yake ne ya sa yake hakuri da halayanta, lalle tana kular da shi da bashi haushi, ama ai shi dinma yana sonta
To ama..................to ama fisabililahi...................
To shi din nan a kan SO ko ciwon yar yatsarsa zai yi ne bale Summa? Wai har a kai ga mutuwa!, So ko wani dalili daban? RISALAH dama mai tsananin tsananta abu ce, ko abinta a gidansu babu mai taba mata, nata fa nata ne, domin ba zai manta wani lokaci da cousin sister dinta ta yi masa wasan cewa mijinsu, RISALA dan rashin wayo a ranar fata fata suka yi da yarinyar, kuma har yau basa magana, a gonakinsa hakan ta faru, ya je kauye ne ya kwana bakwai dan ya bi harkar nomansa da alkhairan gonarsa tace itama zata je kauyen wajen dangin mahaifinta, suka je da y'ar uwar tata, shi tunda ya fahimci karya ta yi ba wani dangin mahaifinta biyo shi ta yi ya cenza mata, kuma sai aka samu matsalar nan Yar uwar tata ke masa irin tsokanar nan, karshema sai shine ya bada mota aka maida y'ar uwar tata, bale yanzu ta ji an aura masa wata? Uhum


Yana hakan MANSUR ya ringa zirga zirgar hanyar kicin da wajen da RISALA ke kwonce har na tsayin mintuna kusan ashirin


Cen ya ji jan numfashinta, sai kuma ya ji kacaniyar da ya tabata ta kokowa ce


A hankali ya sake lumshe idannuwansa dan baya so ya bude ya ga a wani yannayi ta farka da kokowar?


Muryar kukanta, da ratsatsin abin da ya tabata na madubin gilas din dake dauke da ruwan lipton da lemon tsami da akan matsa masa mai yawa a ajiye masa dan bukatarsa ta kansa wace shi kadai ta shafa


Sai kuma muryar MANSUR dake magana da ita yana ta ambatar sunnanta da fadin ta nutsu kar ta jima kanta ciwo, ta nutsu kar ta yi abinda zai ilatata, ko me ya daga mata hankali idan ta bi a hankali ai zata ji saukinsa


Kuka ta kuma fashewa da shi a hankali ta kai zaune tana duka hannunta a saman cinyarta


Idannuwanta da suka fara kumbura suntum , sunna dauke da gashin ido gazar gazar masu tsadan nan ta dauka ta sauke a barin da ABDUL RA'UF yake


Hannunta ta kai daidai zuciyarta tana murzawa a hankali , hankalinta a karshen tashe ta dake kallonsa muryarta a raunane ta ce" Dama zan ga wannan ranar? Dama zan ji haka da kunnena ? Dama zan wayi gari My man, my heartbeat, my happiness my love ace min ya auri wata? , U'r are mine....ka tabatar min da haka da ka barni na kamu da soyayarka!"




A hankali ya dago kansa, jajayen idannuwansa ya sauke a kan fuskarta, muryarsa mai karfin ta balagagun maza ba masu lankwasar harshe irin na launin muryar mata ya bude a hankali ya ce" Kina da matsala!"


"What? U say inada matsala? Inada matsala?"


" Ki min magana a tausashe, nd ki daina min ihu a kan shirmamiyar maganar nan RISALAH, sai da na ce maki ki koma gida, zan zo shine kika....................."
Ya dan nuna wajen da ta summe din irin a rashin damuwa ya sake dubanta ya ce" Ke din ba yarinya bace, ke din ba karamar yarinyar da zata ringa yin shirme bane, ina tunanin kin kai wajen da sai dai ki yiwa wani nasiha da irin abubuwan nan"


Ciwo take ji a zuciyarta, da rarafe ta rarafa da saurin gaske da niyar kamo hannunsa dan ta sake nuna masa irin halin da take ciki na tashin hankali
Sai dai da sauri ya janye hannunsa yana kallonta wannan karron a hankali ya ce" RISALAH?"


Lebensa da ya yi maganar take kallo, jan lebensa mai kama da na jariri take kallo, sajensa dake kwonce da dan madaidaicin gemunsa take kallo, ta san dalilin kiranta da ya yi a haka da kuma janye hannunsa


"U knw, i lv u, i really really love u ABDUL, ka san ba zan taba iya rayuwa da kai da wata ba ko? Kai ka san ba zan iya hakurin hakan ba ko? Wacece ita? Soyaya ka yi da ita bayana? Me yasa baka zo ka aureni ba sai ita ka je ka aura? Yar siyasar su Mama ce tace a gidanku ma ta kwana, tace ka zo, ni banma san ka zo ba, tace aurenka ka zo.........ka daina sona ne ban sani ba? Ka daina ra'ayin aurena ne bani da labari? ABDUL ka daina sona ne?" Ta karashe da muryar kuka sosai, muryar kuka mai taba zuciya sosai, muryar dake taba cen kasan zuciya sosai


Mansur ya kuma yin yinkurin fita a karro na uku


A hankali ABDUL RA'UF ya ce" I said ka zauna tare da mu, domin bana so shedan ya yi tasiri a kaina ta kowace fuska!"


"Ya salam" ya fada kasa kasa, shi da kansa shekara daidaidai hudu ya ba ABDUL RA'UF a duniya, taraiyarsu ba ta ya bishi bane dan yana da kudi, taraiya ce ta mutunci, sun hadu a aji daya tun secondary, shi ABDUL RA'UF an sakashi makaranta ne da wuri sosai, sabanin shi Mansur sai da ya kai shekaru kusan tara ya fara zuwa makarantar sakamakon cenje cenjen waje da tsatsauran ra'ayi irin na mahaifinsa, a sanninsa da ya yi, har zuwa yau da suke dinke matsayin abokai ya sanshi da yin taka tsantsan da harkar mata, ABDUL RA'UF nada kyankyami mai masifar yawa, haka kuma yanada kishi mai kargin gaske,
Ba zaka taba sannin ABDUL RA'UF shima namiji bane sai ka yi zama da shi mai sunnan zama, kamewarsa ta sa baya shiga irin magangannun samari a kan lamarin mata, ko ya nuna zakewarsa ko ya nunaa yes shima yanada wani abu mai sunna feeling a kan mace


Da yawa na masa kallon anya zai iya sakewa da mace kuwa? Da yawa na tunanin da wahala idan yana daya daga cikin maza masu anfani da damar da Allah ya basu dan su mori rayuwarsu ta hanyar badala da ƴaƴan mutane MATA da suka wulakantar da kansu, sai dai basu gane bane, shi din ya fi su more rayuwarsa domin ya guji harkar kazanta yana tanadar zamansa da *WACE ZATA YI MASA LAFABI!*
Ko zamansa shi kadai a gidan nan sai da aka kai gauro aka kai mari kafin kakansa ya amince, kai kakansa ko a yanzu yakan yi masa ziyarar bazata, sannan ya ringa bin daki daki dan bincikensa, yakan yi murmushi idan ABDUL RA'UF din ya tsatsareshi da ido yace" Ka daina kallona a haka, ka san yaren zamani ba'a shedarsu, bale kanada masu bugawa bawa gangar shedan?, Shi yasa nake dan dubawa dan na ringa dan tunatarwa cewa idan aka daki layin an tafkawa kai kuskure mai zafin gaske"


Sosai ya tausasa muryarsa aa tunaninsa, sannan ya yi iya yinsa dan gannin bai wulakanta lamarinta ba, cikin nutsatsun lafuza ya ce" RISALAH, da ni, da ke, da dukan wanda yake tare da mu bamu isa mu zanawa kanmu komai ba, munada ra'ayinmu da muke iya nunawa da karfin ikon da muke da shi a hannayenmu, a tunaninmu!, Bamu san komai da gobenmu ba, gaibunmu ne, ki kasance iyalina ko akasinsa ban taba zama da ke na maki alkawarin zan aureki na rayu da ke ke kadai ba, wannan kuma damata ce, ni a yanzu bani da isashiyar lafiyar da zan iya bi maki komai daki daki...................."


Ya dan dakata yana kallon reaction dinta da son sake fashe masa da kuka, a hankali ya ce" Hey, hei RISALAH saurareni plz..........."


Kanta ta langwabe tana kallonsa , dan murmushi ya yi mata a hankali ya ce" I love u too "


Kanta ta karra langwabewa sosai tana kallonsa da son gaskata maganarsa


A tausashe ya sakar mata da murmushin da ya sakata lumshe idannuwanta da jin tamkar zata dira ta fada masa ta rukunkume shi dan kauna da soyaya, yakan jima bai furta mata kalmar soyaya ba, yawancin lokuta idan ta furta masa yakan ce da ita "ME TOO", Du idan yace da ita I Love u takan adana maganar a kuryar dakin zuciyarta ( kar wanda ya ga laifinta, so ne fa, so ne mai tsanani, wadda na tabata babu wace batada wanda zuciyarta ke yiwa irinsa, sai dai wata ta iya danne shi, danne shin da hanna shi falasa baki dayansa shine alkhairi, domin zamanin namu ne ya zo da kalar gigitarwa!)


A hankali yana kallonta shima ya ce" Zaki yi hakuri ki je gidan har na zo?"


A hankali ta sauke ajiyar zuciya ta waiga barin da Mansur ke zaune ta ga gefe daya yake kallo bayaa ko kallonsu, shi yasa mutumen ke birgeta, kuma Allah yana gani a duniya shine mai taimakon soyayarta da ABDUL, domin wani lokacin ABDUL kan cireta kwata kwata a rayuwarsa, idan ta kama Mansur da kuka sai ya shirya su, ita kam da yau zata ga yarinyar nan da aka ce an aurawa mijinta da sai ta shake wuyanta ta kasheta , sai dai itama a kashetan!


A hankali ta daga masa kanta, dan ta san tunda yace zai zo din, to fa zai zo din ne, kuma ta san idan har ta saukar da kanta kasa suka yi magana to fa tabas zai saki yarinyar nan, dan itama ta san yana sonta


Mikewa ta yi tana jan hijabinta da kyau stiilll tana kallonsa


A

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login