Showing 6001 words to 9000 words out of 130520 words

Chapter 3 - MAKWABTAKA COMPLETE DOCUMENT BOOK Writing by Jamila Umar Tanko .txt

13 Dec 2024

8829

tana ta
nishadi. Wannan muguwar faduwar gaba da
mugayen tunani na tuna abubuwan da suka faru
da ita a baya duk suka ragu. Haka Allah Ya amsa
addu'arta Ya rage mata tunanin matattun da ta
rasa a cikin danginta,
ta sami tawakkali a ranta cewar sun tafi ba zasu
dawo ba. Ta yi tawakkali da *yan uwanta jinin
jikinta, masoyanta na hakika da ta rabu da su
karfi da yaji. Ta tattara tunaninta, rayuwarta da
lamuranta ga mahaliccinta. Shi kadai ne gatanta,
kuma Shi ne mai
taimakonta.
Ta sami nutsuwa nan ta jawo takardun karatunta
ta yi ta karatun abin da za su yi nan gaba tun
ma kafin a koya musu. Don haka daga dukkan
alamu zata fi *yan ajinsu ganewa. Karatu ne ake
yinsa cikin sauki babu neman wani biro da littafi
ana dogon rubutu (note), a computer (internet)
za ka yi ta dubawa, kowa yana da printer sai dai
ka yi ta fitarwa a cikin takardu kana karantawa.
Bayan nan ta mallaki manyan littafan karatu (text
books) wadanda suke bayani filla-filla game da
abin da ta ke karanta, su ma suna taimaka mata
wajen ganewa sosai da sosai.
Da hutu ya kare sai ta ci gaba da zuwa
makaranta tana daukar darasi. Kullum ba ta fashi
asabar da
lahadi ne kawai take zama a gida ta yini tana
bacci safe da rana, da yamma kuma ta tsaya
akan baranda tana kallon titi. Idan dare ya yi sai
tayi karatun boko ko kur'ani, sai ta yi dan kallo
ta tashi
ta fara salloli (kiyamullaili), abubuwan da take
gudanarwa a rayuwarta kenan a kasar nan.
Har yanzu Dr. Faduwa da Engr. Abdul-Sabur ba
su dawo ba, ba wai ta damu su dawo ba, amma
koda yaushe suna fado mata a rai. Har ma ta fi
kaunar kada su dawo balle su fara shiga
rayuwarta. Ba ta ki ace da suka tafin nan ba sun
tafi ke nan har abada, zai fiye mata sauki don ba
ta son a dinga gaisawa kamar yadda suka bukaci
haka daga gare ta. Tasan sun fi ta gaskiya, kuma
ba ta kyauta musu ba.
Maimakon ta yi ta rashin kyautawar ai gara ace
ba sa nan, ba ta gansu ba, basa ganta ba. Don
ba zata iya yi musu abin da suke bukata daga
gare ta ba wannan alkawari ne ta yiwa zuciyarta
babu ita babu wani MAKWABCINTA har abada.
****************************************
A yammacin ranar lahadi misalin karfe biyar na
yamma, Umaimah na zaune a babban wajen
shakatawa na sun way Lagoom tana bangaren da
aka killace namun daji (zoo). Tana zaune a gefen
wani dutse wanda ke bulbulowa da ruwa, tana
hango namun daji da dandazon Turawan da suke
ta layin kallo da daukar hotuna. Iska mai sanyi
ce ta ke ta kadawa har cikin kanta ta ke jiyo
sanyin iskar duk da dan karamin hijabin da ta
saka. Riga da siket ne a jikinta *yan kanti masu
launin fari da baki, sannan ta saka takalmi fari
mai tsananin tsini da jakarsa fara.
Turawa biyu ne mace da namiji daban-daban
sukazo suka roke ta ta yarda su dauki hoto da ita
saboda ta yi kyau sosai. Sai ta tsinci kanta tana
duban jama,a tana murmushi ita ma kamar yadda
suke yi mata murmushi da zarar sun hada ido da
ita.
''Assalamu alaikum''.
Kalmar da ta jito kenan cikin kamilalliyar murya a
saitin kunnenta na dama. Nan da nan ta wurga
ido ta dubi inda muryar ta fito. Kafin ta gama
waiwayowa kamshin turarensa ya daki hudojin
hancinta, ko ba a fada mata ba tasan kanshin
wannan disigner ne (Dolce Gabbana) ya fesa.
Ta daga ido da sauri ta dubi kyakykyawar surar
jikinsa, har zuwa zukekiyar fuskarsa. Yayin da
idanuwanta suka tsaya cak tana kallon wasu
fararen hakoransa yana yi mata dariya. Ta yi
matukar mamaki da ganinsa a wannan waje
kuma a dai dai wannan lokaci. Ba ta amsa masa
ba, sai ta
dukar da kanta kasa.
Abdul-Sabur ya sake matsowa gare ta cikin
harshen Nassara ya ce, ''Kin yi min izinin na
zauna tare da ke?
Ta girgiza kai alamar a'a
Sai ya yi murmushin karfin hali ya ce, ''Ni ne
Abdul-Sabur makwabcinki, yau satina guda da
dawowa.
Wannan kalmar ta makwabci ita ta sake saka
mata tsanar ya kasance a kusa da ita, don haka
tun bai rufe bakinsa ba, ta yi cimak ta mike tsaye
da sauri ko waiwayowa shi ba ta yi ba, ta nufi
get din fita.
Kira ya ke, ''Maye! Maye!!
Ta ki waiwayowa a inda kalmar 'maye ta sake
hassalata. Ba ta yi wata-wata ba ta tsayar da
tasi ta shige ta tafi gida. Ta nemi nishadin
zuciyarta ta rasa, sai takaici da ya taru ya yi
mata dankar. Ta yi da na sanin zama a gidan nan
saboda takurawar da
Abdul-Sabur yake yi mata. Tabbas dole ta tashi
daga gidannan da zarar kudin hayarta na shekara
ya kare gara ta nemi inda babu bakar fata ko
daya balle ya yi tunanin yi mata magana. Tana
fitowa daga tasi ta ci karo da Dr. Faduwa ita da
kawayenta sun fito daga cikin get daga dukkan
alamu rako su tayi za su shiga tasi su tafi gida.
Don haka ta yi saurin tsayar da ya kawo
Umaimah, ta yi ta kallon Umaimah tana so su
hada ido ta yi mata magana, yayin da Umaima ta
ki kallon inda suke balle su gaisa. Ta zaro kudin
mota ta biya ta saba jakarta, ta kawar da kanta
gefe ta kara gaba.
Dr. Faduwa ta bi ta da kallo kawai tana girgiza
kai da alama tana mamakin hali irin na Umainah.
****************************************
Jiki da jini, dare daya Allah Ya ke sauke ciwo
sauki kuwa sai ahankali. Kwana daya da yini
guda cur ta yi tana ciwon ciki mai tsanani, tun
tana kan gado tana murkususu har ciwo ya
tsananta ta fado kasa.
Juyi kawai ta ke a tsakar daki babu abin da ta ke
ambato sai, ''Wayyo Allah, wayyo Allah cikina,
Allah
Ka taimake ni. Idan ciwon ya dan lafa kadan sai
ta rufe ido ta fara
dan bacci, can sai ciwo ya dawo ya turniketa, ta
sake kwalla kiran sunan Allah, tana neman
agajinSa.
Allahu Akbar, Shi kadai ne mai yaye ciwo a duk
sanda Ya so. Addu'a ta ke, kuka ta ke,
murkususu ta ke yi ita kadai, amma ciwon bai
dauke ba ga shi ta kasa tashi zaune ma balle ta
tashi tsaye tayi tafiya.
Tun cikin dare Abdul-Sabur yake ta kasa kunne
yana sake saurarawa shi dai kamar daga dakin
yarinyar nan yana jin ihu ana kiran Allah-Allah.
Don haka a zaune ya kwana, idan aka jima sai ya
tashi ya bude wundo ya yi ta leken gidanta bai ga
kowa ba, kuma bai daina jiyo karar ba. Ya bude
baramda ya fito ya tsaya yana ta sauraro, tabbas
ihun mace ne, kuma daga saitin dakin yake
fitowa. Tabbas yau ba lafiya akwai matsala!
To amma ya za'a yi ya sani? Ta ina zai iya
taimakonta?
Abin da ya kwana ya yini ke nan yana zulumi. Ya
saukko ya hau benensu kofar gidanta ya tsaya.
Ya
tabbatar ta ciki aka datse. Ihun take yi kuma
sosai yana jiyo ta, sai yai kamar zai buga mata
kofa sai ya
tuno sakon jan kunnen da ta bayar a bashi, don
haka sai ya fasa.
Ya juya zai koma gida sai ya ji ba zai iyaba, ya
sauko gidan Dr. Faduwa da yake kasan na
Umaimah a hawa na goma sha takwas ta ke. Ya
ci sa,a ma kofarta a bude don ita mace ce mai
jama,a ta yi baki, wasu mata ne guda biyu *yan
Indiya suna ta hira.
A yadda ta gan shi ta san ba ta jin dadi, saboda
ba ya walwala, sai ta shiga tambayarsa ko
lafiya?
Ya yi murmushin karfin hali ya gaishe ta da
kawayenta, sai ya roki Dr. Faduwa ta fito waje
suyi magana. Ta biyo shi a gigice, yayin da
zuciyarta ta ke ta kadawa don fargabar abin da
zai fada mata.
Cikin zumudi ta ke tambayarsa, ''Lafiya?''
Ya girgiza kai, magana ya ke cikin marairaciyar
murya.
Ya ce, ''Faduwa, ki yi hakuri, ki taimaka min ki
taimakawa addininki, ki yi don bin sunnar Manzon
Allah (S.A.W) ki yi don hakkin MAKWABTAKA''
Sai ta dafe kiriji ta fara hawaye nan da nan ta
rikice daman rikirkitacciyar ce, ma,ana tana da
saurin gigicewa.
Nan da nan Larabci ya hautsine bakinta ta manta
ma Abdul-Sabur ba ya jin larabci.
Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Abdul-Sabur
ishfi?
Ya girgiza kai ya fada cikin harshen Turanci, ''Ki
yi mini turanci don na fahimce ki. Ki kwantar da
hankalinki, ba wani abu bane illa matsala ce ta
faru ga makociyarmu. Waccan yarinyar ta hawa
goma sha tara. Ina ga kwana ta yi a kwance ba
ta da lafiya, ina jin ta kasa ta shi ta bude kofa.
Ina tsoron ka da ta mutu a cikin gida ita kadai
don ba ta da lafiya sosai.
Dr. Faduwa ta murtike fuska, tare da aika masa
harara, ta tabe baki yayin da ta yi saurin goge
hawayen da ya cika mata ido. Ta murje idanuwan
radau ta dube shi.
Ta ce, ''Tunda nake a rayuwata ban taba ganin
mutum mai laushi da rashin zuciya irinka ba.
Haka tunda nake ban taba ganin mutum mai
taurin da bakar zuciya ba irin na wancan yarinyar,
fitsararriya ce marar kunya, wacce ba ta son
mutane, mai bakar aniya. Ko a cikin satin nan na
hadu da ita a bakin get ta harare ni da *yan
uwana ta wuce. To ni kuwa me zan yi da ita?
Shawara ta karshe da zan ba ka Abdul-Sabur
shine, ka koma gidanka ka shige ka rufe, abin da
babu ruwanka dadin kallo gare shi. Idan ta mutu
tarube ta yi wari masu gadi za su gaji da warin
su
balla gidan su dauke ta su binne. Idan da *yan
uwanta anan a sanar musu, ballantana ma ba ta
da *yan uwa ko kawa, balle saurayi saboda bakin
halinta. Ni dai kaga shiga ta gida, ina da abun yi,
ba zan kare a wannan yarinyar ba.
Ta juya a fusace zata shige.
MAKWABTAKA 6
Ya yi sauri ya tari gabanta yana magiya cikin
wata marainiyar murya mai tafe da tsananin
damuwa, magiya da tausasa lafazai.
Ya ce, ''Faduwa, ki yi taimako don Allah ba don
niba, ba don ita ba, ba don halinta ba. Ki yi don
cika hakkin MAKWABTAKA, kina da ilimi, kin san
yadda Ubangiji Allah (S.W.A) Ya yi magana a
alkur'ani mai girma akan hakkin makwabci akan
makwabcinsa.
Manzon Allah (S.A.W) ya ce, a lokacin da
Mala'ika Jibrilu ya ke isar masa da wahayi akan
hakkin makwabci akan makwabcinsa ya ce, ya
zaci za'a ce makwabci zai iya gadar
makwabcinsa.
Abdul-Sabur ya surnano da hawaye mai yawa. Ya
ce, ''Allah Shi ne Sabur, ma,ana Mahakurci, na
kasance Abdul-Sabur bawan Allah mai yawan
hakuri. Bana rama tsiya da tsiya, sai da alkhairi.
Haka bana fushi sabida darajar sunana.
Faduwa yarinyar nan tana da hakki a kanmu a
matsayinta na musulma, kuma makwabciyarmu.
Mu cika hakkin daya rataya a kanmu ko da ita ta
ki, zai yuwu jahilci ne ke damunta, rashin sani ko
kuma wani dalili nata na daban saboda shirmen
yarinta da yake damunta. Tana cikin halin wuya,
ciwo mai tsanani tun cikin dare ba ta runtsa ba,
ina jiyo rakinta.
Dr. Faduwa ta yi kasake tana dubansa, domin ya
daure ta da jijiyoyin jikinta.
Ya fada cikin sassanyar murya, ta ce, ''Kana so
na taimake ta ko? To ta ya ya zan iya taimakon
yarinyar da ta kulle gidanta, kuma ta ce a ja
mana kunne kada mu sake shiga harkarta?
Abdul-Sabur ya marairaice, ya ce, ''Wajen masu
gadi za mu je, mu sanar musu su debo mukullai
su bude ta ta baya a ga halin da ta ke ciki.
Sannan a matsayinki na likita kije da akwatinki na
taimakon gaggawa (first aid box) ki taimaka mata
kafin a kaita asibiti.
Dr. Faduwa ta ce, ''Kaje ka sanar musu idan an
bude gidan an tabbatar ba ta da lafiyar da gaske,
kuma ta amince na zo sai ka kirani a waya na
taho da akwatina.
Abdul-Sabur ya dukar da kai kasa, ya yi godiya
ya hanzarta sauka kasa wajen masu gadi, don ya
sanar musu.
Yayin da Dr. Faduwa ta shiga gida ta fara korowa
kawayenta labarin abin da ya ke wakana
tsakaninsu da Umaimah. Sun fusata dajin haka
suna masu roko, magiya da ba wa Dr. Faduwa
shawarar cewa ko Umaimah zata mutu kada ta
taimaka mata. Ya yin da haushin Abdul-Sabur ya
rufe su, suka yi ta Allah wadai da irin wannan
rashin zuciya tasa. Bayan mintuna goma wayar
Faduwa tayi kara, ta na dubawa ta ga sunan
Abdul-Sabur ne, sai ta dubi kawayenta ta yi
murmushi.
Ta ce, ''Ga shi nan inajin zancen zai yi min.
Suka ce ''Kada ki amsa, ki kyale su can su
karata.
Faduwa ta ki amsawa, sai kira yake yana sake
maimaitawa amma ta ki dagawa.
Kwatsam suka gan shi a gabansu, yayin da ya
dubi Faduwa ya dubi wayar da ke kan cinyarta
tana ruri,
ma'ana amsawa ne kawai ba zata yi ba.
Ya girgiza kai cikin rashin jin dadi, ya ce, ''Ashe
Faduwa ba ki aminta da ayar da na kawo miki ba,
game da hakkin makwabci akan makwabcinsa? A
cikin suratul Nisa'i Aya ta 36 Allah Ya yi magana
akan makwabta.
''Kuma ku bautawa Allah, kada ku tara shi da
kowanne abu.Ga mahaifa a kyautata musu kuma
ga ma,abocin zumunci da marayu da matalauta
da makwabci ma,abocin kusanci da makwabci
manisanci da abokin gefe da hanya da
abubuwanda hannuwanku na dama suka mallaka.
Lallaine Allah baya son wanda ya kasance mai
takama mai yawan alfahari. Sadakallahul azim.
Faduwa ta dubi kawayenta, ta ce, ''Kunji yadda
yake daure ni da jijoyoyin jikina ko? Ai dole na je
na duba yarinyar nan.
Kawayenta suka hautsine da hayaniya suna cewa,
kada ta je.
Abdul-Sabur ya dube su a nazarce, ya sake
tabbatarwa ba musulmai ba ne, kana ganinsu
zuryan ka ga Hindu.
Ya juya ya dubi Faduwa cike da takaici, ya ce,
''Har zaki tsaya kina sauraron Ahlul-kitabi,
wadanda ba
musulmai ba, ana miki maganar Allah da Manzon
Sa, maganarsu har tafi maganar mahaliccinki?
Haba
Faduwa kada fa ki bata a sanadiyyar wannan abu
ki rasa imaninki. Abu kalilan sai ya kai bawa
aljanna, haka abu kankani sai yakai mutum wuta.
A sanadiyyar taimakon yarinyar nan da zaki yi, ki
ceto ranta za ki iya samun rahamar Ubangiji...''
Bai rufe bakinsa ba Faduwa ta yi cimak ta mike
tsaye ta shiga daki ta dauko akwatinta, suka fice
yayin da kawayenta suka bisu da harara babu
abinda suke ji sai haushin Abdul-Sabur da ita da
Faduwar da ta biye masa.
Lallai Umaimah ta galabaita, bakinta ya bushe ko
makwarwar ruwa babu a makoshinta. Ta tuje
gashin kanta, haka rigar barcin da ke jikinta duk
ta kanannade saboda burgima. A karkashin gado
ma aka zakulota saboda burgima,, ta wahala har
karfinta ya kare, don haka ko yatsanta bata iya
dagawa balle ta bude ido ta kalli wanda ke kanta.
Daga ta bude ido sai ta rufe luuu kamar
sumammiya. Nan da nan tausayinta ya lullube
zuciyoyin duk
bil'adaman da yake gurin, scurity uku, Faduwa da
Abdul-Sabur.
A gigice Faduwa ta bude akwatinta ta dauko
allurai da magunguna ta fara aiwatar da ayyuka
irin na kwararriyar likita. Abdul-Sabur ya ruga
kicin ya bude firij ya dauko ruwan sanyi ya kawo
ya mikawa Dr. Faduwa. Ta ce, ''A,a kada a ba ta
ruwan sanyi sai dai abu mai dumi kanar shayi ko
Coka oat.
Don haka Abdul-Sabur ya sake garzayawa kicin
ya jona ruwan zafi a butar lantarki (kettle), ya
bude
lokokin kicin din sai ga komai a jere reras wajen
kayan abinci daban, kayan shayi daban
kwanuka,kofuna,cokula. Kicin dinta a tsare ya ke
ga tsafta ko ina.
Ya dauko kofi da cokali ya sake daurayewa
sannan ya zuba sukari kadan, milo da madara,
sannan ya
zuga tafasasshen ruwan zafi akai, ya jujjuya ya
dauko ya kawo.
Dr. Faduwa ta karbi kofin ta dago kan Umaimah
akan cinyarta ta dinga tarfa mata da cokali, sai
sha
take sabida tsananin yunwa da kishirwar da ta ke
addabarta.
Dr. Faduwa ta dubi security ta ce, ''tana bukatar
karin ruwa da gwaje-gwaje a gano kan ciwon,
dole a kaita asibiti.
Sai suka gaggauta kiran wayar asibiti suka
bukaci da su turo da motarsu (ambulance) za,a
dauki mara lafiya.
Abdul-Sabur ya bude durowar kayanta yana
dubawa, ba tare da ya san wanda zai daukar
mata ba. Kaya ne a goge a linke sanka-sanka,
sai kamshi suke yi, daga baya ya riguna da
bangarensu, siket, abayoyi, mayafai da dai
sauransu.
Ya jawo wata doguwar riga ja (abaya) da dan
kwalin ya hada ya mikawa Faduwa, ya ce ta saka
mata. Ya roki masu gadi da su fita falo su bari
mace ta shityata.
A falo ne ya isa kan teburin cin abinci a in da ta
dora laptop dinta da takardunta, ya shiga
babbankadawa, a nan ne ya ke ganin sunanta
ajikin takardun, ta rubuta UMAIMA BELLO, a she
ba sunanta MAYE ba? To me kalmar MAYE take
nufi?
Ya karanta a baiyane, ya sake maimaitawa, sai
yau yasan sunanta. Ya ci gaba da bankada
durorwoyinta da suke falon, takardu ne kala-kala
duk na makaranta. A jikin durowar Talabijin stand
ya ga wata *yar karamar jaka ya bude ya ga
himilin
hotunanta ne. Ya fara budewa cikin sauri yana
dubawa, ya ganta ita da danginta mata da maza,
yara da manya, da kuma tsofaffi. Wato iyayenta
da kakanninta.
Ya cika da mamaki da ya ga wasu hotunan, gashi
babu wanda zai iya tambaya a yi masa bayani.
Bai gama kallo ba ya ji jiniyar mota (zmbulance),
kan kace kwabo sun hayo da gadonsu, suka shiga
dakinta cikin gaggawa, suka dorata akan gadon
mai taya suka turota a shassheme kamar gawa
sai numfashi ta ke yi sama-sama.
Abdul-Sabur ya shiga dakinta da sauri ya bude
jakarta ya fara bincikawa yana neman I,D card
dinta bai gani ba, sai dai yaga passport dinta. Ya
yi sauri ya bude ya duba, ya ga hotonta da
sunanta
radau, sai yau yasan kasarta ashe yar Nigeria ce?
Ya zakulo *yar karamar jaka (wallet). A cikin
jakar ya bude anan ne ya ga I.D card dinta na
makaranta wato FTMS, da wasu kuma na wasu
makarantunta
na can Nigeria. Ya hada ya mikawa malaman
asibitin.
Shi da masu gadin gidan ne suka kukkulle mata
ko ina a gidan, sannan suka watse. Dr. Faduwa
ta koma gidanta, security suna rike da makullin
gidan suka koma dan dakinsu a bakin get, yayin
da Abdul-Sabur ya koma gidansa.
Umaima kuwa na can akan gadon asibitin ana
ceto rayuwarta don ta galabaita, bata ciki
hayyacinta.
Daga asibitin aka yi wa makarantarta waya suka
tura malamai mata guda biyu, su ne za su dinga
zama da ita.
Ya kasa zaune, ya kasa tsaye, balle ya kwanta,
babu ma maganar cin abinci a wajen Abdul-
Sabur, ya shiga damuwa sosai, saboda tausayin
rai.
Babban abun tausayin ma shine rashin hakikan
*yan uwanta a kusa ga babu waya balle a buga a
sanar musu. Ko saboda hakin mutuwa.
Addu,a yake, Allah Ya sa ta rayu kada ta mutu,
ba ya son ta mutu duk da ta tsane shi, ba ta ki
ta ga ba
ya doron kasa ba. A daddafe ya bari gari ya
waye,
da sassafe ya shirya ya fito wajen masu gadi, da
suka gaisa sai ya tambaye su adireshin asibitin
da aka kai Umainah.
A rubuce suka bashi kamar haka:- Sime Darby
Medical Center Subang Jaya Jalan SS12/1A
47500 Selangor Darul Ehsan, Malaysia.
Babu wata matsala yasan ma asibitin, ba shi da
nisa da makarantarsu. Sai ya yi musu godiya ya
nufi asibitin. Yana hanya yana fargaba guda biyu.
Na farko yana fargabar yadda zaiga jikinta, sauki
ko tsanani. Sannan na biyu yana fargabar yadda
za ta yi idan ta ganshi, farin ciki ko takaici?
MAKWABTAKA 7
Ko ba a fada masa ba, yasan ta tsane shi, ba
mamaki idan ta ganshi ta disga shi. Shi dai koma
mai zai faru ya ji ya gani sai ya je ya saka a
ransa duk abin da yake yi yana yi ne saboda
Allah, kuma a wajenSa yake neman sakayya.
Ya isa asibiti a reception, ya yi musu bayanin
suna da yanayin ciwonta, na da nan suka fada
masa
hawa na uku ta ke, da lambar dakin da ta ke. Ya
yi godiya ya nufi dakin, yayin da fargabar da yake
ciki
ta sake tsananta. Yana ta addu'a dai har ya isa
kofar dakin, ya kwankwasa a nutse gami da yin
sallama,
sai yaji muryar wasu mata sun amsa masa
sannan ya tura kofar ya shiga.
Aka hau kallon-kallo tsakaninsa da matan biyu,
daya *yar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login