Showing 3001 words to 6000 words out of 130520 words
Chapter 2 - MAKWABTAKA COMPLETE DOCUMENT BOOK Writing by Jamila Umar Tanko .txt
don
haka ta fara tunanin hawa tasi wacce zata kai ta
har
kofar gida zai fi yi mata sauki don idan ta ce zata
bi jirgi zata sha wuyar hawa da sauka benaye.
Don haka saita tsaya a titi ta tsayar da tasi ba
tare da bata lokaci ba, ta shige ita da kayanta
dukka. Ta
sanar masa inda zata je, ya danna meter suka
nausa. Da suka isa unguwar sai ta dinga nuna
masa
hanya har bakin get din gidan su. Ta biyashi
Riggit 10 ne cif-cif, sannan ta jido ledojinta ta
fito mai tasi yaja motarsa ya tafi abinsa.
Kamar daga sama ta ji wata murya wacce ta ke
kokarin gusar mata da farin cikin da ta kunso
daga BB Plaza.
Kalmar ''MAYE'' ta ji ya ambata, Ta waiwayo a
fusace Abdul-Sabur ne ya nufo ta da farin cikin
sa. Ta ji kamar ta kifa masa mari, sai tayi tsaki
ta juya da sauri yayin da nauyin ledojin hannunta
suke rinjayarta.
Cikin harshen Turanci ya ce, ''Maye, taimakonki
da leda daya, saboda naga kayan sun yi miki
nauyi.
Ba ta amsa masa ba, sai ta ci gaba da tafiya, ya
kai hannu zai karba ta daka masa tsawa.
Cikin harshen Hausa yau ma ta yi masa magana.
Kai ! Ka kyale ni, dole ne?
Duk da ba ya jin yarenta ya ga alamar fushi a
fuskarta, ya san fada take yi masa. Don haka sai
ya
sakar mata ledarta ya tsaya cak yana kallonta
har ta haye branda, ta ci gaba da jan Ledojinta
sannan ta shige lift ta haye sama.
Masu suna daga zaune suna kallonsa daga
dukkan alamu suna tausaya masa saboda
kacaccalawar da ta yi masa. Ya wuce gidansa
ransa ba dadi, babu
abin da bai saka ba a ransa game da Umaimah,
ya kudira har karshen rayuwarsa ya daina kula
ta.
Tunda Umaimah ta shiga gida ta rufe dukkan
wundunanta da kofofinta ta kashe fitulun dakunan
falo da korido, kicin dinta ne kawai da fitila. Ac
da talabijin ce kawai a kukkunne. Wanka, Salla,
cin abinci, karatu bacci da kallo kawai ta ke yi
acikin gidannan ita kadai, sai da ta shafe sati
guda cur ba ta leka wundo ba ma balle ta fito
baranda ko ta fito waje.
Tana ta kallon yanda ake ta bukukuwan kirsimeti
a talabijin, ba ta damu ta ga kowa ba kamar
yadda ba ta so itama aganta. Dama a ce ba sai
ta fita makaranta ba za,a dinga turo mata
darasin da za a koya mata ta computer, ba dan
dole ba ba zata sake lekowa waje ba, don ita
wannan rayuwar ta ita kadai ta fiye mata dadi.
A ranar ne da daddare misalin karfe goma na
dare, ta ji ana buga mata kofa. Mamaki marar
misaltuwa ne ya rufo mata, don tunda ta ke a
gidan nan ba ta taba yin baki ba, ba ta da kowa
a kasar nan. *Yar karamar shimi ce a jikinta da
gajeran wando nan
danan ta yayimi zubulelen hijabinta ta saka tana
sanda ta zo ta leka ta hudar da ke jikin kofa. Sai
ta ga wata mace duk da batasan sunanta ba,
tasan MAKWABCIYARTA ce, sun sha haduwa a lift
ko a bakin get amma basa magana. Kawar Abdul-
Sabur ce, don tana yawan ganin su tare, wato
Dr.Faduwa.
Sai taki budewa, kuma har yanzu Dr. Faduwa ba
ta daina buga kofar ba gami da danna kararrawa
ba kakkautawa.
Umaimah tana jikin kofar tana kallonta ta ki ta
bude, fiye da mintina goma. Daga karshe Dr.
Faduwa ta zaro wayarta ta kira Abdul-Sabur cikin
harshen turanci ta ke shaida masa tana ta
bugawa
ba,a bude ba, da alama dai babu kowa a gidan.
Ba ta ji amsar da ya bata ba, sai taga ta kashe
wayar ta
ci gaba da kai-kawo a koridon. Ba jimawa sai ga
Abdul-Sabur ya bayyana, sanye yake da doguwar
riga jallabiyya fara da carbi a hannunsa, daga
dukkan alamudai daga masallaci ya ke.
Ya hau bugun kofa da karfi, yana danna
kararrawa shi ma kamar yadda Dr. Faduwa ta yi
ta gaji ta bari.
Umaimah na labe tana kallonsu ko kwakwkwaran
numfashi ba ta yi balle ta yi tari. Banda haushin
su
ba abin da ta ke ji, ta rasa dalilin shishshigin da
suke yi mata, sun takurawa rayuwarta. Saboda
takura ta baro kasarta ta zo inda ba,a taba
saninta ba. To saboda me za su saka mata ido,
dole ne a yi mutuncin?
Ta ci gaba da saka yadda zata bullowa Abdul-
Sabur ya kyale ta, ta yi rayuwarta ita kadai,
yadda ta tsarawa kanta.
Nan dai ta ga su Abdul Sabur suna tsaye suna
shawarar yadda za su yi. Sun yi shawara kala-
kala, sun yi shawarar kiran jami,an su zo su balla
kofar su gani, ko suje makaranta su fada, ko
kuma su
sanarwa masu gadin gidan (security).
Shawarar da suka tsaya mafi sauki, ita ce su fara
sanarwa masu gadi. Nan da nan taga sun juya
sun nufi lift ta tabbatar bakin get suka tafi. Ta
ruga daki da gudu ta je ta saka kayanta, wata
doguwar rigar leshi ce (gown) ta saka da dan
karamin hijabi ta dawo bakin kofar ta tsaya tana
jiran wanda Allah Zai kawo.
Ba jimawa sai ga security guda biyu a bakin
kofarta, hannayensu cike da makullai suna kokarin
soka makulli a jikin kofar gidanta, sai ta yi wuf ta
bude ta bayyana a gabansu cike da mamaki a
fuskarta.
Cikin harshen Turanci ta tambaye su, ''Lafiya me
yake faruwa ne? Sai suka yi cirko-cirko suna
kallonta amsa daya ta gagare su. Da kyar dayan
ya bude baki ya ce.
''Makwabtanki ne suka lura sati guda ba sa jin
motsinki, kuma ba,aga fitarki ba, sun buga ba ki
bude ba, shine suka sanar mana za mu bude
gidan mu ba ko lafiya? Ta hade rai tare da
yamutsa fuska, ta ce, ''Ina nan, lafiyata kalau. Sai
dai inaso ku jawa wadannan makwabtan nawa
biyu kunne, mace da namiji su fita daga harkata,
musamman namijin yana
takurawa rayuwata. Ku fada masa ba shi ba ni,
ya rabu da ni tunda ba zamansa nake yi ba. Suka
amsa mata da, ''To zamu sanar musu...
Basu rufe bakinsu ba, sai ga Abdul-Sabur da Dr.
Faduwa sun taho da sauri hankalinsu a tashe
suka nufo su. Kafin su karaso Umaimah ta ce da
ma'aikatan ''Good night.
Ta shige gida ta banko kofa ta datse ta ci gaba
da lekensu ta jikin hudar kofar. Dr. Faduwa ta
tambaya a dimauce, ''Kun bude
gidan, tana nan lafiya?
Sai suka shaida musu duk abin da ya faru, kuma
suka dora da sanar da su sakon da ta bayar a
fada musu. Dr. Faduwa ta dubi Abdul-Sabur
shima ya dube ta, sai ya sunkuyar da kai kasa
cikin jin kunya ya rasa abin da zai ce.
Ma'aikatan suka wuce suka barsu a nan a tsaye
suna ta kallon kofar gidan Umaima.
Can Dr. Faduwa ta nisa cikin kufula. ta ce,
''Abdul tsayuwar me muke yi anan? Mu koma
gidajen mu mana, ai maganinmu kenan da shiga
shirgin da babu ruwanmu. Kai duk ka jawomin
harna fara baccina mai dadi ka ishe ni da waya in
zo in duba ta. Ashe duk bugun nan da
muke tana jinmu don tsabar rainin hankali ta
kyalemu saboda tsabar tsana. To ma ye ya yi
zafi zamu zauna muna wulakanta kanmu, muna
yar da girman mu akan *yar yarinya karama
kamar wannan? Allah Ya gani mun fita hakkin
MAKWABTAKA.
Abdul-Sabur ya gyada kai ya ce, ''Kin fadi
gaskiya Faduwa, ki yi hakuri da na jawo miki,
insha Allah bazan kara jawo miki irin wannan ba.
Sai suka juya suka tafi, yayin da Umaimah ta
jingina ajikin kofar ta dade a tsaye, ita kanta ta
rasa dalilin da yasa ta ji aranta ba dadi. Ta san
tabbas bata kyauta musu ba, ai wanda ya kulaka
ya damu da hakin da kake ciki mai kaunarka ne.
Amma ba laifin ta ba ne, zuciyarta ne batason
makwabtaka. Ba ta so adinga bada hakkin
KAKWABTAKAR.
****************************************
Gaba dayansu jarabawa suke yi, don haka
kowannensu ba ya zama a gida, gari na wayewa
sai su fice makaranta, sai da magaruba kuma.
Wasu lokutan Umaima tana rigasu dawowa, tana
daga kan barandarta ta ke hango dawowar su,
sai tayi sauri ta koma cikin gida, don kada ma
Abdul-Sabur ya hau sama ya bude barandarsa ko
wundo ya ganta.
Shi ma ya sha hangenta tana tafiya, ko tana
dawowa daga makaranta, amma bai sake
marmarin saukowa su hadu ba. Ya cika da
mamakin dalilin da yasa ta ke wannan muguwar
zuciya kamar ba musulma ba, harya fara tunanin
kilama ba musulma ba ce, hijabin dai kawai take
sakawa don ta saje da *yan kasar kamar yadda
wasu baragurbi ke yi idan suna son su cimma
wasu manufofi nasu.
A haka suka ci gaba da zama har suka gama
jarrabawar semester, aka rufe makarantu. Da
yawa daga dalibai suna ta shirin tafiya gida hutu,
saboda yana da yawa yayin da wasu irin su
Umaimah suka
mike kafa ba in da za su je.
Abdul-Sabur ya yanki tikitin jirgin sama na
komawa kasarsu Ghana don yin dogon hutun nan.
Haka Dr. Faduwa ita ma a satin zata tafi kasarsu
Egypt. Don ta shekara ba ta je ba.
Ranar da Abdul-Sabur xai tafi harya saka
kayansa a tasi sai ya garzaya gidan Umaima ya
sakale wata
farar takarda a jikin kofarta, ya juya da sauri ya
tafi.
Jirginsa na dare ne dan haka kwana da yini suka
yi a hanya ya isa Accra babban birnin Ghana. Sai
bayan tafiyar Abdul-Sabur da kwana uku Umaima
ta fito zata je Bukit bin tang za ta yi cefane,
sai ta razana da ganin doguwar wasika a jikin
kofarta, alhali bata da kowa, kuma ba ta san
kowa
ba a kasar.
Ta dade tana tofa addu'o'i kafin ta taba takardar,
sannan ta dangwala hannu a kikin takardar, ta yi
sauri ta cire hannunta alamun tsoro, kai ka ce
wuta ce ta done ta. Ta sake mika hannu a karo
na uku kamar mai tsantsani, kamar wacce zata
taba kashi ta zaro takardar ta bude a tsorace.
Marbass Dan Aunty...
MAKWABTAKA 4
Ba komai ba ne a cikinta illa zankadeden rubutu
cikin wani kayataccen turanci. Ta fara karanta
saman, sallama ce cikakkiya aka yi mata.
Ko waye mai wasikar nan cikakken musulmi ne,
don haka ta sami kanta da kosawa ta karanta
abin da ya ke cikin takardar. Cikin nutsuwa ta
hanzarta karanta cikakken sunan marubucin
wasikar
Abdul-Sabur Abdul-Rashsid, wannan ne ya sa ta
yi kokwanton ko ba ita aka yi wa takardar ba,
kuskure ne aka samu don ba ta jin ta taba cin
karo da mai irin wannan sunan. Ta manta a
lokacin da mutumin nata mai kiranta da MAYE ya
fada mata sunansa.
Ko da ta fara karanta layi na biyu daga cikin
wasikar sai ta ga kalmar 'MAYE' ta bayyana, don
haka ta tabbatar ta tabbatar wasikar ta ta ce,
daga makwabcinta ta ke. Sai ta ji ranta ya baci,
ta yi kwafa ta gyada kai saboda takaici. Ta
yamutse fuska ta fara karantawa a shelake.
Ta gyara tsayuwarta, ta gyara gilashin idonta
sosai ta ci gaba da karantawa, nan da nan taji
kafarta
kamar ba zata iya daukarta ba, saboda sagewa
hade da tashin hankali. Sai ta ji ba zata iya fita
ba kuma, ta koma cikin gida ta zauna a gefen
gadonta tana karantawa. Ta na sake maimaitawa,
yayin da
taji kanta ya yi mata nauyi, zuciyarta tana ta
bugawa kamar zata fashe. Ta jji ta shiga damuwa
marar adadi, ta ji kamar an zare mata lakka. Wai
shin me yake faruwa? Me Abdul-Sabur ya rubuta
mata ne da ya ta ba zuciyarta haka Oho?
Allah Shi Ya barwa kanSa sani.
Har ta kwanta cikin dare ta ji maganarsa tana yi
mata yawo a kwakwalwarta, sai ta laleba fitilar
da ke gefen idonta ta kunna ta sake jawo wasikar
a karkashin filonta ta karanta, ta sake
maimaitawa.
Hakika maganganun gaskiya ne, amma tana
ganin ba zata iya bin gaskiyar nan ba, don zata
takura.
Daman masu magana suna cewa, gaskiya daci ne
da ita.
Abin da ya rubuta kuwa ba wani abu ba ne illa
aya ce guda ya dauko sukutum don ya
wa,azantar da ita, don yana tunanin jahilci ne
yake damunta.
Da Turanci ne amma ga fassarar kamar haka:-
Assalamu alaikum warahamatullahi wa
barkatuhu.
Ya *yar uwata musulma 'MAYE' ina matukar jin
ciwon halayenki a matsayinki na musulma. Shin
ko kin san MAKWABCI a musulunci?
A'a ba ki sani ba,
don da kin sani da kin dinga amsa sallamar
MAKWABTANKI. Idan ni namiji ne kina zargin zan
cutar da ke. Dr. Faduwa fa?
Ki yi tunani ki gyara halayenki. A cikin arba,una
hadis, hadisi na goma sha biyar Manzon Allah
(S.A.W) ya ce, ''Duk wanda ya zama
ya bada gaskiya da Allah da ranar lahira, to ya
kyautatawa makwabcinsa.
Ki sani makwabci ba karamin hakki gare shi akan
makwabcinsa ba. Daga karshe ina yi miki sallama
na tafi kasata Ghana. Allah ya kaddara
saduwarmu, amin.
Daga Abdul-Sabur Abdul-Rashid.
****************************************
Dr. Faduwa ma ta tafi kasarta Egypt, bayan
tafiyar Abdul-Sabur da kwanaki uku. Sun tafi sun
barwa
Umaima gidan sai ta yi ta leke-lekenta ita kadai
babu mai kulata bare ya takura mata. Tama
yawan
tsayawa baranda ta yi ta kallon titi, idan ta gaji
da tsayuwa akan baranda, sai ta jawo doguwar
kujera (stool) ta zauna, idan ta fara gyangyadi
sannan ta tashi ta shiga cikin gida, ta kwanta
akan doguwar kujerar falonta, ko kuma ta wuce
daki kan gadonta. Ba ta cika yin girki ba, sai dai
tayi ta shan
shayi da biskit, ko lemo (juice) da biskit abincinta
ke nan.
Sai jifa-jifa take dafa abinci, shima ba wani
kayatacce ba ne, shinkafa da wake da mai da yaji
ne saboda ba ta da walwalar da zata nutsu ta
shiryawa kanta abinci mai dadi.
Tana sallah ta yi addu,a sosai, haka kuma ta ke
ware lokacin da take shirgar kuka, kusan kullum
sai tayi wannan kukan saboda tuna baya. Tabbas
kawai rayuwa ta ke amma ba ta jin dadin
rayuwarta, tana iya kwana biyar bata furta kalma
daya ba, banda karatun sallah bata magana.
To idan ta yi maganar ma da wa za ta yi?
Daman da tana da waya ne ta amsa waya ta kira
ko a kira ta,
to ba ta da waya don bata bukatar asan tana
raye. Anya kuwa rayuwa zata yiwu a haka?
Ace mutum shi kadai zaiyi rayuwa a duniya, babu
dangim babu MAKWABTA, babu abokai? Kai abin
da kamar wuya wai gurguwa da auren nesa, inji
masu iya magana.
Umaimah dai haka ta zabarwa kanta, sai ta dade
tana kallon barandar Abdul-Sabur, ta ga kamar
zata ganshi amma sai taga wayam! Idan iska ta
kada wundon kabule ya kada, sai ta bude ido
tana
kallo, sai ta zaci motsinsa ne sannan taga ba shi
ba ne. Ashe dai ko ya ya mutum yake dadi ne
dashi?
Tabbas tana jin ba dadi da ta zamo babu wanda
ya san da ita. Ga shi anyi hutun makarantu balle
ta je makaranta duk da ba hira ta ke da kawaye
da abokai ba,
amma dai tana dan jin sanyi a ranta, kuma tana
rage lokaci akan dogon zaman da ta ke yi da ta
ke
yi agida ita kadai.
Dare ya ki yi da wuri, idan da daddare ne ta ga
gari ya ki wayewa da wuri. Dogon hutu ne aka
basu na tsawon watanni uku, gashi ko wata daya
ba ta cika ba, zaman duk ya gallabe ta. Tana ta
sassaka abubuwa aranta. Ta yi shawarar ko ta
tafi Negeria, amma garin da ba a taba saninta ba
ta je ta gama hutunta ta dawo? Ko
kuma ta tafi dubai ta shakata ko zata ga
abubuwan da za su nishadantar da ita, ta ga
jama,u kala-kala daga kasashe daban-daban?
Amma tana fatan kada Allah Ya sa ta hadu da
*yan kasarta *yan garinsu wadanda suka taba
saninta a rayuwa. Domim dubai ta zama
matattara, kuma cibiyar cinikayya mutane daga
kowacce kasa a duniya zuwa suke. Sai ta ga da
taje Dubai me zai hana ta tafi Saudia don tayi
umara ta fadawa Allah bukatunta duk da tasan
duk inda bawa yake ya yi addu,a Allah Yana
ganinsa, kuma Mai amsawa ne.
Yadda rayuwa ta kuntata a gare ta ina ita ina
maganar nishadi? Ai gara ta je Saudia, ta kaura
Ka,aba da Shabbaki, tunda ita a ranta ta fi
kaunar mutuwa da ace ta ci gaba da rayuwa a
haka.
Sai ta surno da hawaye zafafa a lokacin da take
binciko Passport dinta, tana tunanin yadda
rayuwa
ta cunkushe ta cakude mata cikin dan kankanin
lokaci tana karamarta. Ta fada a bayyane yayin
da ta saka gefen hannunta ta sharce hawaye.
''Alhamdu lillah alah kulli halin''. Ta fada a
bayyane.
Yadda taga dare haka ta ga rana, tana ta sake-
sake iri-iri a ranta. Kafin gari ya waye zuciyarta
ta tsayar mata da shawarar gwara ta tafi Saudia.
Gari na wayewa laraba ce, misalin karfe goma sha
daya na safe Umaima ta fito a shirye tsaf cikin
kyakykyawar shigarta, dogon hijabi ne har kasa.
Babu abin da ake iya gani a fuskarta sai tafukan
hannayenta. Ta ratayo jakarta mai dauke da
Passport dinta da kudi masu yawa. Sannan ta
hado da ATM Card dinta, don idan kudi bai isa ba
ta fitar da wani.
Tana fitowa titi, sai ta tsayar da tasi tana zama
ta ce ya kai ta, 'JALAN AMPANG' unguwar da
ofisoshin Embassy suke. Ta shaida masa
Embassy Saudi Arabia ta ke so ta je. Ba tare da
bata lokaci ba suka tafi, Riggit goma sha tara ne
dai-dai, ta bashi ashirin ta wuce ba tare da ta
karbi canjin ba.
Shigarta ke da wuya sai ta ga ma'aikata na
girmamata, sun karbeta cike da fara,a saboda
shigarta da ta burge su. Ta koro musu bayanin
cewar Visa ta ke nema zuwa Saudiyya har
tsawon
wata guda saboda tana so taga likita a can. Nan
danan aka yi ta dogon Turanci da cike-ciken
takardu aka ce ta dawo bayan kwana biyu, bayan
sun karbi Passport dinta Sai ta tsinci kanta tana
mai farin ciki tun bata tabbatar za su ba ta ko ba
zasu ba ta ba. Tana komawa gida ta kama
harhada kayan tafiya ta zuba a akwati. Kirga
awanni kawai ta ke yi don ta kagu kwana biyu ta
cika taje ta karbo Visa, tikiti kawai zata yanka ta
hau jirgi ta isa kasa mai tsarki. SAUDI ARABIA
Haka kuwa aka yi, kafin sati ya zagayo Umaimah
har ta hada komai ta isa gari mai albarka,
Madina.
Satinta biyu a Madina ta kaura kacokan
Shabbaku, bacci ne kawai ya ke dawowa da ita
dakinta na Hotel. Addu'a kawai ta ke akan
dimbun bukatunta da kuma fatan cikawa da
imani. Sannan ta dawo Makka a inda ta ci gaba
da gudanar da ibadunta. Kwana take a harami
tana dawafi, da nafilfili. Addu'a ta ke, amma fa
kuka ta ke da hawaye tana fadawa mai kowa mai
komai
abin da yake addabarta.
Takan saki nikaf dinta ta rufe fuskarta idan ta
hangi *yan uwanta bakar fata, musamman idan
ta ga *yan Nigeria ne Hausa/Fulani, saboda ba ta
so dai-dai da rana daya ta hadu da fuskar da ta
sani.
A ranar da ta cika wata guda cur a ranar kuma
zata koma gida Malaysia, da daddare misalin
karfe tara tana cikin dawafin bankwana sai ta yi
kicibus da wani abu daya firgita ta, ya ba ta
mamaki, ga shi cikin rashin sa,a ba ta saka
nikafinta ba. Fuskarta a bude take tarr ! A fili ga
hasken lantarki tamkar da rana.
Kamar yadda ta hadu da mummunan faduwar
gaba mai dauke da dimbin mamaki a bayyane a
fuskarta haka ta ga ya faru da su su ma. Ta
tsaya cak tana kallonsu yayin da suma suka
kame suna dogon kallonta.
Abdul-Sabur Abdul-Rashid na hannunsa na
sakale a kafadar wata mata daga dukkan alamu
dai matarsa ce, wacce yake matukar so da
kulawa. Sai Matar ta yi mamaki da razanar da
Umaimah da Abdul-Sabur suka yi da suka ga
junansu. Nan aka hau kallon-kallo tsakaninsu su
dukka ukun ba tare
da wani daga cikinsu ya iya furta kalma daya ba.
Umaimah ce ta fara gaggauta barin wajen, ta
kutsa cikin jama,a tun suna hango ta har ta bace
musu.
MAKWABTAKA 5
Umaimah ta sauka a kasarta Malaysia a cikin
gidanta. Tabbas addu,a ba ta faduwa kasa, Allah
Ya
na amsa addu'ar bayinSa a duk sanda suka
rokeShi. Ta riki Allah Ya yaye mata kunci da
damuwa nan da ta addabi zuciyarta. Haka kuwa
ta sami saukin damuwar nan da ta dankare mata
a zuciya. Ita kaidai agidanta amma