Showing 1 words to 3000 words out of 130520 words

Chapter 1 - MAKWABTAKA COMPLETE DOCUMENT BOOK Writing by Jamila Umar Tanko .txt

13 Dec 2024

8008


MAKWABTAKA
FARKON LABARI
A cikin jerin dogayen gininnikan da suke kan titin
Maharjalele, Kaula Lumpur babban birnim
Malaysia.
Da misalin karfe takwas na safiyar litinin, ga
sanyin safiya, ga sanyi daga gandun dajin da
yake gefen gidajensu yana kadowa. Iskar da ke
kadawa ta yi dai-dai da yanayin garin saboda
zafi-zafin da ake
yi. Nan da nan sai mazauna garin suka sami
nishadi da walwala a wannan safiyar.
Motoci na gani na fada ne suke ta giftawa a
wannan titin, yayin da wasu jama'a da yawa suke
ta wurwucewa da kafafuwansu. Halittar Ubangiji
kala-kala, Allah daya gari bam-bam, kowacce
kasa
da nata yanayin haka da irin kalar halittunta.
Matansu sanye suke da riga da siket na yadi
(material) mai kama da atamfa, sai dan guntun
hijabi iyaka kirji, wasu kuwa riga da wando suke
sakawa (jeans da blause), sai su saka hijabi ko
dankwali babba. *Yan mata *yan gayu kuwa
gajeren wando suke sakawa iya cinyarsu da *yar
shimi. Mazansu kuwa sukan daura zani da riga
ko riga da wando da hula mai kama da Pakistan
launin bakake ko wasu kalolin. *Yan gajeru ne
yawancinsu, farare tas-tas masu
gajeran hanci da luhu luhun idanuwa, suna da
gashi mai tsayi da tsanani laushi da baki. Kusan
gaba dayansu musulmai ne kadan ne suke yin
wani addinin. Amma duk da haka ba sa shari,ar
musulunci, kowa yana holewarsa yadda yake so.
Akwai bakaken indiyawa wadanda asalinsu bayi
ne aka kawo su suma yanzu sun zama *yan
kasar suna addinin Hindu. Sunan kudinsu Riggit,
yana da daraja sosai idan aka hada shi da Naira
dan har ya fi Saudi Riyad daraja.
Umaimah Bello tsaleliyar budurwa matashiya
wacce shekarunta basu wuce ashirin da biyar ba.
Bakar fatace *yar Africa amma tafi wasu fararen
fatar kyau nesa ba kusaba. Fara ce sosai idan ta
shiga cikin fararen ba dukka ba ne zasu nuna
mata fari ba, haka hanci, idanuwa masu kyau,
baki dan madaidaici gani da gashi mai tsawo da
laushi. Kirar jikinta kuwa ba kowacce mace ba ce
ta sami irin wannan kirar. Umaimah doguwa ce
ba tsawo tsololo ba, marar kiba amma ba
bushashshiya ba.
Tsaye take akan barandar gidanta, bene hawa na
goma sha tara, tana kallon kasa tana shakar
daddadan yanayin garin. Daga gani babu
tambaya ta sami nishadi saboda annurin da yake
kwaranya a fuskarta. Matsatstsan lemon zaki ne
ta matse a kofin tangaran (fresh orange juice) a
hannunta.
Idan ta leka ta kalli titi, sai ta kurbi lemon nan
mai sanyi.
Kallon kowannensu take daya bayan daya, ta ga
suna tafe a nutse cikin nishsdi. Sabanin yadda
*yan
kasarta suke Nigeria, kowa yana tafe a zabure kai
ka ce koro shi aka yi, wasu suna tafe suna
lissafin
kudin cefane saboda masifa da suka sha mana
kai.
Sai tausayi ya rufeta har kwalla ta cika mata ido,
musamman da ta tuno danginta na karkara Fulani
masu kiwon shanu.
Ta fada a bayyane, ''Allah Ka kawowa kasata
Nigeria agaji, mu ma mu samu ci gaba kamar
*yan
kasar Malaysia.
Tana daga ido ta kalli ginin gidajen da suke
fuskantar gidanta, sai ta yi arba da mutumin nan
mai nacin kallonta shi ma a tsaye yake a
barandarsa. Daman ta ji ajikinta ana kallonta
kamar yadda ya saba.
Ta galla masa harara, ta ja dogon tsaki ta shige
gida cike da tsananin takaici, musamman yanda
ya ganta daga ita sai *yar yaloluwar rigar bacci
koriya iya gwiwarta, kanta babu dankwali. Ya yi
murmushi yana shirin ya gaishe ta sai ta koma
cikin gida da sauri. Tana shiga falonta sai ta
daga labule ta leka barandar ta ga baya nan,
daga nan ta tabbatar daman don ita yake fitowa
ya tsaya da ta koma shi ma ya bar wajen. Ta
kuduri niyyar shirya masa rashin mutunci muddin
ya ci gaba da takura mata da hana ta sakewa a
farfajiyar gidanta.
Bakar fata ne, amma daga ganinsa ba dan Nigeria
ba ne. Koma dai dan wacce kasa ne yana da
kyau da kyawun sura, dogo ne sosai mai dan
kiba kadan, fari ne sol, mai hanci da gwarza-
gwarzan idanuwa, mai yawan fara,a gami da
fararen hakora a jere reras a cikin bakinsa
madaidaici. Daga
ganinsa yana da tsafta dan dan gayu ne na
karshen zamani. Tun daga gashin kansa zuwa
gemunsa zaka gane tsaftarsa koda yaushe zaka
ga suna sheki, kamshin turarensa kuwa tun daga
benenta take fara jiyowa.
Ta daga ido ta kalli agogo, karfe takwas saura
kwata. Tana da darasi (lecture) karfe tara don
haka sai ta hanzarta fadawa wanka, kan ka ce
kwabo ta gama shiryawa ta fito tsaf sanye da
riga me dogon
hannu launin ruwan hoda (pink blause), wando
(jeans) baki da takalmi (cover shoe pink) sai dan
hijabinta baki iya kirji irin na *yan kasar Malaysia.
*Yar karamar jakar (computer laptop) ta ratayo a
kafadarta ta rufo gidanta, ta fito. Ta hadu da
jama,a da yawa a lift (*yan Malaysia, Chinese,
Indian) da sauransu, amma ba su ishe ta kallo ba
balle ta yi musu murmushi saboda bata sha,awar
ta saba da
MAKWABTANTA. Tana isa kasa ta fito daga lift ta
kama gabanta sannan ta nufo get din fita. Abun
mamaki sai ta ci karo da mutumin na mai nacin
kallonta, wanda gidansa yake saitin gidanta
shima
a hawa na goma sha tara yake, amma gininsu
daban sai dai get dinsu daya saboda duk gida
daya
ne.
Nan danan ta sake tsuke fuska ta kara daga kafa
tana sauri, domin taga ya fara mata wannan
murmushin nasa. Yana da niyyar ya gaisheta, ita
kuma bata bukatar hakan. Saurin da take ya
wuce misali, don haka nan da nan ta bace masa,
sai da ta waiga ta ga ba ta hango shi ba, sannan
ta rage tafiya ta ci gaba da tafiyarta a
nutse. Tana hawan matattakala zata tsallaka
gada zuwa daya hannun kasancewar kasashen da
aka ci gaba ba,a tsallaka titin mota sai dai su bi
ta gada. Hawan matattakala da wuya sai ta ji ta
gaji likis, kasancewar hawan da yawa. Kwatsam
ta ji wata lallausar murya a gefenta cikin harshen
turanci ana yi mata sannu da aiki.
Ta waiga da sauri, sai ta ga mutuminta,
makwabcinta. Ta yi mamaki da ganinsa saboda
ta dade da tsere masa, sai dai idan ta lunguna ya
biyo ba ta titi ba, don ta waiwaya ba ta ga kowa
na biye
da ita ba.
Cikin harshen turanci yake magana, sai da ya jero
mata tambayoyi har guda uku ba ta amsa masa
ko guda daya ba, harya fara tunanin ko ba ta jin
turanci ne?
Sai ya shiga yi mata maganar gwarawa ya fara
kacaccala Turancin yadda ko dan koyo zai gane.
Ya ce, ''Are you from Sudan? Libya? Egypt?
Ethopia? Or Mali?''
Sai ta harare shi ta kawar da kai ta ci gaba da
tafiya. Har yanzu dai yana biye da ita yadda ta ke
sauri
haka shi ma yake yi.
''What is your name?
Yasan dai dole tasan wannan kalmar, sai ya sake
ganin wata sabuwar harara daga gare ta, ta kalle
shi sama da kasa , cikin takaici ta ce, ''MAYE
kawai, sai nacin tsiya !''
Ta yi murmushi ya ce, ''Your name is Maye? Wow
nice name. A zatonsa ta ce sunanta maye. Ya
bita yana ta bayani cukin harshen Turanci, duk
magana daya sai ya ambbaci sunan nan ''MAYE.
Sai takaici ya sake karuwa a zuciyar Umaimah ta
rasa yadda zatayi dashi, kalmar karshe da ya
fada mata ita ce. ''My name is Abdul-Sabur''
Da ya ga da gaske ta kufula sai ya kyale ta, ta
wuce ta nufi hanyar makarantarsu ko tantama
babu a
FTMS GLOBAL COLLEGE ta ke yi, don ya ga ta
nufi hanyar makarantar. Idan kuwa *yar jami,ace
ya za a yi ta ce ba ta jin Turanci? Sai dai idan
idan ba ta da niyyar amsa masa ne, wannan
hujjar mai karbuwace.
Tunda ta sunkuyar da kanta kasa tana tafiya ba
ta kara dagowaba balle ta waiwayo bayanta. Ba
ta
tsaya a ko'ina ba sai a cikin ajinsu, a inda ta
sami kujera ta zauna. Zamanta ke da wuya sai
Malami ya
shigo ajin ya fara yi musu darasi akan abin da ta
ke karantawa, wato soft ware engineering.
****************************** *********
Washe gari misalin karfe goma na safe Umaimah
ta sake fitowa ta nufi makaranta sanye ta ke da
bakar abaya, sauri ta ke saboda tana da test
karfe goma sha daya. Yau ma a bakin get ta ci
karo da mutumin nata Abdul-Sabur, shi ma zai
fita. Sanye yake da wata nakar (suit). Sai da ta
yi da gaske ta gane shi,
don ya sauya taga ya kara kyau.
Ya yi mata murmushi sannan ya yi mata sallama
gami da dorawa da ambaton sunan nan da yake
zaton sunanta ne, wato, ''MAYE''.
Nan da nan ta ji ya bata mata rai, ta harare shi
ta wuce ba tare da ta amsa masa ba. Sai ya
shiga mamakin yadda *yar musulma ta ke da
bakar zuciya haka ko sallama ba ta amsawa. Ba
shi kadai ta ke yiwa haka ba,daga dukkan alamu
harda sauran MAKWABTAN, don ya ga yadda ta
ke tafiya a fusace ba ta ko kallon inda suke.
Tunda yaga Dr, Faduwa ta wuce ba su gaisa ba
ya san tabbas abin ya fi karfin Dr. Faduwa,
watakila ta gwada sau daya ta ga babu riba, dole
ta kyale ta don ba don haka ba ya san yadda ta
ke da matukar son mutane, gata da fara,a ko ka
ganta ko ba ka ganta ba zata yi maka magana.
Ya tsaya suka gaisa da Dr. Faduwa, sannan suka
dunguma su uku suka yi bakin titi. Umaima na
gabansu su biyu suna baya suna ta hirarsu cikin
harshen Nasara (English).
Dr. Faduwa balarabiyar Egypt ce. Allah Ya yi
halittarsa anan saboda ko a larabawan ma kafin
ka sami mai kyauwu irin na Faduwa sai ka
bincika.
Bata da tsayi kuma tana da *yar kiba amma a
dire take, hanci dogo, ga manyan idanuwa, da
lallausan gashi har yana taba cinyarta dan ma
koda yaushe tana cikin yanke shi. Gata *yar
gayun gaske ce tana
shiga suturunta na larabawa a mutunce, kallo
daya zaka yi mata ka tabbatar likita ce dan
sana,ar ta
dace da surarta.
MAKWABTAKA 2
Umaimah ta haye matattakala ta haura gada,
yayin da su biyu suka tsaya a bakin titi suna jiran
tasi, a
inda Abdul-Sabur zai tafi makarantarsa Inti
College da ke unguwar Subang Jaya, ita kuma
tana Sun Way University, don haka mota daya ma
zasu hau, idan aka sauke ta sai a wuce da shi.
Ba jimawa suka sami tasi suka bude suka shiga
gidan baya su dukka biyun. Bayan sun
zaiyyanowa
direba inda suke so ya kai su, sai ya danna meter
ta fara kirga musu kudinsu ba sai anyi dogon
ciniki ba, kana tafe kana ganin kudin da kaci.
Nisan tafiyarka yawan kudinka.
Dr . Faduwa ta dubi Engr. Abdul Sabur ta ce,
''Yarinyar can karama da ita sai fadin rai, ba ta
gaisar da mutane, haka ba ta amsa gaisuwa idan
an
gaishe ta. Na dauka ko don ta ganmu farar fata
ne ya sa bata amsa mana, sai yanzu kai bakar
fata ma dan uwanta ba ta amsawa. Ni kuwa
naga ba gwara
ta dinga gaisawa da mutane ba saboda halin
mutuwa ko ciwo. Ita kadai a gida babu uwa ba
uba ba miji, MAKWABCI ai shi zai fara taimakonka
musamman da yake mu ma musulmai ne *yan
uwanta. Ko ya ya ka gani Abdul?
Ka yi mata yarenku ko zata fahimce ka.''
Ya yi murmushin karfin hali ya ce, ''Wa ya fada
miki tana jin yarena? Ai ba kasarmu daya ba ko
kin zaci duk bakar fata suna jin yaren juna? Ai ba
abin da zan iya yi, sai dai na yi mata addu,a Allah
Ya sa ta gane.
Daga nan suka sauya akalar hirar dan basu saba
da gulma ba irin tamu anan ayi ta cin naman
wanda
baya nan, da aka isa makarantar su Dr. Faduwa,
wato Sun way university ta sauka, zata biya
kudin
mota Abdul-Sabur ya ce ta bari zai hada ya biya
dukka, suka yi sallama tare da yiwa juna fatan
alkhari. Ta shaida masa ba zata dawo gida yau
ba sai gobe, saboda akwai gwaje-gwajen da zasu
yi.
Direba ya fisgi mota ya ci gaba da tafiya bai
tsaya ko'iba sai a Inti Subang Jaya, inda meter
mota ta nuna kudinsa Riggit 35 ne, ya yi dai- dai
da kimanin naira dubu daya da dari bakwai. Ya
zaro ya biya, ya shiga makaranta. A inda ya ke
hada karatunsa na masters.
*Yan Nigeria sun cika kowacce jami,a da ke kasar
Malaysia, musamman jami'o'in kudi, ba kamar ta
gwamnati ba, duk da suma na gwamnatin duk
wacce ka leka zaka gansu burjik.
Wata jami'ar idan ka leka sai ka rantse a Abuja
kake saboda yawan *yan Nigeria. Hausawa da
inyamurai sunfi yawa, ko ba,a fada maka ba ka
san za,ayi rashin ji.
A lokacin da jami'an tsaro wato *yan sanda da
Immagiration suka gane cewar, ba gaba dayansu
ba ne dalibai, sun dai bi hanyar cuwa-cuwa ne
sun sami visa irin ta dalibai amma ba karatun
suke yi ba, sai suka shiga kame ba dare ba rana,
mai gaskiya da marar gaskiya a nufinsu duk
dalibin gaskiyar da suka kama makarantar da
yake zata je ta karbe shi,
wanda kuwa ba ya karatun daman ba,a san shi
ba a makaranta babu mai belinsa.
Don haka zaman gidan kaso (prison) ya kama
shi, har sai ranar da jaki yai kaho. Saboda
Malaysia ba kamar Saudiyya ba ce, wacce idan
aka kama takari za,a sako su ajirgi kyauta a
dawo dasu kasar su,
gobe idan suka hada kudi su koma a sake kamo
su a dawo da su gida kyauta. Su ba sa haka ba
zasu yi
amfani da ko sisinsu wajen kawo ka kasarka ba,
idan na *yan uwanka ba ne suka zo za su tafi da
kai, sai dai ka dauwama a nan.
Yawancinsu ko kuma na ce gaba daya Hausawan
da suke karatu a wannan kasa ba su da wannan
matsala, duk wanda ka gani karatu ne ya kai shi,
iyayensa ko kuma gwamnatin garinsu. An fi
samun matsala a wajen wasu kabilu da ba
Hausawa ba, su ne suke shiga su zauna haka
kawai ba sa karatu.
Aiki ba ya samuwa, haka babu aikin karfin da za
su yi su sami kudi, sukan sami wankin mota, sai
kuma
wannan sana,ar mai hadari, wato safarar miyagun
kwayoyi, wanda idan suka haye sun gama kudi,
idan kuma ta kwabe musu hukuncin kisa ne babu
shamaki.
Wadannan kabilun wadanda ba Hausawa ba sun fi
kowacce kabila zama a club tun daga farkon dare
har zuwa asubah, babu abin da ake sai shan giya
da neman mata, kide-kide da raye-raye. Idan sun
sha sun yi tatul fada sai ya hautsine, sai kaga
ana fasa kwalabe za'ayi cake-cake. Idan ba
jami'an tsaro suka hango ba, ba sa watsewa,
Hukumar Malaysia ta gaji da natsaniyar *yan
Nigeria sai suka shiga kwashe su don su rage
bata
gari. Duk da ba kowa ne ya hadu ya zama daya
ba, akwai dalibai na gari wadan da karatunsu ne
a gabansu.
Cikin dare Immigiration suke kai sumame a irin
gidajen da wadannan bata garin suke cika. Kama
su suke yi kawai babu ji babu gani. Saboda
tsabar razana da guje-guje har wasu sukan
dimauce su diro daga kan dogon bene daga can
kololuwa hawa na biyar ko na bakwai, ko
tantama babu farfashewa kawai suke yi, wasu su
mutu a take,
wasu su karasa asibiti, wasu kuma su jiggata har
abada sun lahanta.
Don haka suke guduwa daga gidajen su idan dare
ya yi, tunda sun fahimci da daddare jami,an tsaro
suke zuwa su kama su, sai su shige wajen ajiyar
motoci ko cikin daji har gari ya waye, sannan su
dawo gidajensu su kwanta suyi barci, daga inda
magaruba ta yi sai su fice sai kuma wata goben
za su dawo gidan. A hanya ma ba su tsira ba ana
kama su da rana, ko da kuwa ka nuna passport
dinka da Visa a jiki ba sa kyale ka, dole sai sun ji
ta bakin hukumar makarantarku. Shin sun sanka
ko ba su sanka ba?
Su na kama ka sai su tamabaye ka sunan
makarantar da kake su tuntubi makarantar. Allah
Ya kyauta, Allah Ya yi mana jagora, Ya ba wa
shuganinmu ikon gyara mana kasarmu, mu huta
zarya kasashen da suka ci gaba mu daina ganin
wulakanci da muzancin da ake mana amin.
*****************************************
Wannan kame bai zo kan su Umaimah ba, sai dai
kullum tana samun labari a makaranta, ta ci sa'a
kuwa a unguwar *yan kasar ta ke zaune, duk
rukunin gidajen ita da Abdul-Sabur ne kadai
bakake, ita ce kuma kadai *yar Nigeria.
Sai taji takaici ya rufo mata, kishin kasarta ya
kama ta, ta ji kamar ta bar karatun ta koma
kasarta talaucin ya kashe ta. Ta sake jin ta tsani
duk wata farar fata, musamman ma *yan kasar
Malaysia. *Yan Malaysia ma ta fi tsanar jami,an
tsaro da suke takurawa *yan kasarta. A wani
bangaren kuma sai ta ga ai ba laifin *yan
Malaysia ba ne, laifin
shugabannin kasarta ne Nigeria da suka ruguza
mu, suka handame mana dunbin arzikin da
kasarmu ta ke da shi.
Ita kadai dai a cikin gidanta tana ta wasi-wasi a
zuciyarta. Ta zunbura baki kai kace fada ta ke yi
da wani, tsaki kuwa da kwafa ta yi fiye da sau
dari a cikin awa guda. Tana zaune akan dinning
table din da yake falonta,
karatu ta ke da laptop dinta, amma ba ta
fahimtar komai, daga dukkan alamu rayuwa ta
tsananta a gare ta, tabbas ba karamar matsala
ba ce ta koro ta daga kasarsu ta yiwo hijira zuwa
wannan kasa mai
tsananin nisa. Daga gani ba ta jin dadin
rayuwarta musamman da ake nunawa *yan
kasarta kabilanci
ana yi musu kora da hali. Hakika badon guguwar
da ta korota daga can ba ta fi wannan kura da ta
hakura da karatun ta koma gida.
Ta fada a bayyane, ''Ya ya zanyi da rayuwata?
Ina zan saka raina? Ba ni da kowa, bana kaunar
kowa babu mai kaunata''
Sai ta dafe kai ta surnano da wani zazzafan
hawaye mai radadi.
Ta fada a zuciyarta, ''Daga dukkan alamu wata
rana za,a zo a dauki gawata a cikin gidan nan,
saboda
bakin cikin da nake ciki. Ta yi zumbur ta mike da
sauri kai ka ce zungurarta aka yi. Ta nufi cikin
dakinta da sauri ba ta tsaya a
ko'ina ba sai cikin bandakinta a in da ta dauro
alwala don ana ta kiraye-kirayen sallar
magaruba.
A gaban gadonta taa shimfida abin sallarta, cikin
nutsuwa take gabatar da sallolinta. Bayan ta idar
da farilla sai ta dinga jero nafilfili, addu,a ta ke
Allah Ya yaye mata masifun da suka addabi
rayuwarta, tana neman Allah Ya koro mata farin
ciki a cikin zuciyarta, saboda ta kasance tana
cikin kunci tamkar zuciyarta zata buga.
Ta ci sa,a kuwa ruwan sama ake ta tafkawa
kamar da bakin kwarya, ya yi dai-dai da lokacin
da Allah Ya ke karbar addu'ar bayinSa.
****************************************
Kwanci tashi Umaimah Bello ta yi watanni uku a
Malaysia haka sun yi nisa da fara karatu saboda
a farkon September suka fara, ga December ta
kusa karewa. Duk inda ka juya babu abin da kake
gani sai jama,a musamman Turawa sun shigo sun
yi bikin kirsimeti.
Ana saura kwana uku kirismeti Umaimah ta
shirya da yamma ta fito ta yiwo sayayyar kayan
abinci,
duk abincinta ya kare, saboda tasan idan aka
shiga bikin kirsimeti manyan super market da
malls za su cika da jama,a.
Sanye ta ke da riga da siket *yan kanti (purple
color), sai dan karamin gyale baki da ta yane
kanta,
tana sanye da takalmi baki a kafarta mai tsini
kadan, ta ratayo jakarta baka. Iska mai sanyi ce
ta ke kadawa saboda anyi ruwa an dauke, ba ta
tsaya a ko'ina ba sai a tashar jirgin kasa da yake
tafiya a sama (Mono rail). Shi wannan
jirgin kasan a sama yake tafiya anyi masa
hanyarsa *yar siririya a sama, wadanda ke cikin
jirgin suna
hango mutane da titinan motoci a kasa. Jirgin
yana dauke da kujeru da yawa, amma akasarin
wajen tsayuwa ne ya fi yawa fiye da
kujerun zama, don an yi karafunan rikewa da
wasu igiyoyi a ake rikewa. Jirgin ba shi da direba
computer ce kawai ta ke tukawa, haka ba ya
ribas gaba kawai yake yi. ***************
*************************
da fatan littafin ya muku,
am gaskia ya kamata kowa ya bada contribution
na comment dinsa . Dan ina son post twins a
rana ammana sai ana samun ishashen commnt
ne shine zai bada daman yin hakan..
MAKWABTAKA 3
Manyan ledoji biyu ta cika makil da kaya,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login