Showing 150001 words to 153000 words out of 153964 words

Chapter 51 - BAYAN NA MUTU Book Original By Aisha Shafii.doc

30 Aug 2025

3783

so a wannan lokacin illa in kalle ki kawai."

Ya sake yin shiru yana murza yatsunta cikin nasa, itama kuma bata cewa komai ba tsawon wucewar wani lokaci.

"Daga nan me ya faru?" Zuwa can muryarta ta tambaya a hankali alamun tana son jin cigaban.

Sai ya sunkuyo da kansa daidai satin nata ya had'a goshinsu, abinda ya fad'a na gaba ya sauka kamar ruwan sama akanta, kowacce kalma ta tab'o can k'asan ruhinta.

"May be na samu sa'ar samun numberki a wajen Sa'id, then we talk. May be kuma na fara aiki ke kuma kika cigaba da karatunki, amma muna tare da juna kodayaushe, we talked about almost everything, all those little and silly things but there never sound silly to me saboda dasu nake iya rayuwa a kullum. An then one night... Na gaya miki cewa ina sonki!"

Bata san lokacin da wani murmushi mai kama da dariya ya sub'uce mata ba, don har sai da fuskarsu ta jijjiga a tare, dama ace so samu ne...

"Zaki k'arasa?" Ya tambaya cikin husky muryarsa.

A wannan lokacin ne kuma ta kasa iya rik'e kanta, taji ba abinda take son irin itama ta fallasa mata sirrin tata zuciyar, ta fad'i kalaman da har yanzu bakinta bai gama tsara su ba, don kowacce jijiya a jikinta a matse take da zumud'in hakan. Ta d'ago da kanta a hankali ta kalle shi, shima ita yake kallo, idanunsa d'auke da wani abu daya k'ara dulmiyar da tunaninta. Ta d'aga masa kai a hankali kafin tace.

"Nima ina sonka Adam, na dad'e ina sonka... na soka tun a lokacin da nake tunanin na tsane ka, lokacin da ban ko ni wacece ba, sannan na so ka har a lokacin da rayuwarta ke cikin hargitsi, kuma insha Allah zan cigaba da sonka fiye da yadda duk wata mace zata so ka a duniyar nan, na karbi rahmar da Allah yayi min ta bani kai, insha Allah zan zama abin alfaharinka kuma ina rok'on Allah ya bani ikon da zanyi maka biyayya da dukkan iyawata."

Bata kai ga rufe bakinta ba Adam ya jata cikin jikinsa gabad'aya, ya jata zuwa wata duniya da ba san da wanzuwarta ba tsawon rayuwarta, hannayenta suka shiga rawa sannan kwakwalwarta ta rud'e, Ta dai ji sanda yayi magana amma bata iya fahimtar komai a cikin abinda yace ba sai kalamai uku kawai.

"...an bani ke!"

Bayan haka ba abinda take iya fahimtar sai yadda bakinsa ke motsawa akan nata, yana kissing d'inta kamar bazai daina ba, kamar iya wannan lokacin kad'ai suke dashi a rayuwarsu, kamar babu wata sauran magana da ta rage a duniya.

Hawaye mai d'umi ya gangaro daga idanunta sanda tattausar muryarsa ta furta akan bakinta.

"Ina sonki Fadeelah..!"

***

BAYAN NA MUTU!

BAYAN WATANNI TAKWAS!

Babban gida a cike yake da mutane fal maza da mata wanda duk wanda ka gani jini na gidan, don banda matattu hatta wad'anda ba'a fiye gani a gidan ba da wad'anda suka dade basa garin aka fara mantawa dasu kowa na nan.

Taro ne na farko irinsa da aka tab'a had'awa a gidan bisa kokarin Adam da kuma Sa'id, don sune umul'abaisin haddasa shi, kuma ba karamar wuya suka sha ba kafin hakan ya tabbata, don babu wanda aka gaiyata ta waya, da kansu ska dinga yawo gari-gari duk inda wani jinin gidan ya yada reshe har suka samu had'o kan kowa.

Babban falon Kawu Da'njuma cike yake da dattijai magidanta wad'anda sune 'ya'ya kad'ai na gidan, in ka d'ebe matansu kuma da suka taru a b'angaren gwaggi Ramatu, bayan gaka kowacce kusufa-kusufa ta gidan a cike take da jikoki da 'ya'yan jikoki har da tattab'a kunne ma suna ta wasa da tsalle-tsallensu, kowa cikin shiga yake mai kyau kamar yau take sallah. Don babu wanda zaka gani kaga fuskarsa babu annashuwa.

Filin dake harabar wajen Kawu D'anjuma shine inda aka kawata da rumfuna da kuma tausasan dardumai a matsayin inda za'a zauna, sannan ga tarin cima nan kala-kala da Adam yasa akayi ordering daga wani babban gidan abinci dake cikin garin Zariya. Abinci ne fal! Kuma kala-kala da duk yawan mutanen gidan babu hangen zasu iya tashinsa.

A wannan lokacin Fadeelah na b'angaren Aunty Hassanah ita dasu Mairo da kuma sauran wasu daga cikin sa'anni irinsu, suna ta kokarin packaging wasu 'yan souvenirs ne da suka yi shawarar a rabawa 'yan mata da kuma matan aure.

Wani maroon lace ne a jikinta da yasha adon fararen duwatsu, anyi mata d'inkin riga da skirt mai bud'ewa sosai, fatar jikinta tayi wani haske alamun hutu da nutsuwa da kuma d'an jaririn ciki.

Duk aikin da suke, Afra na mak'ale a kusa da ita don yanzu kusan ta zama 'yar gidanta. Wata Nafisa 'yar wajen Gwaggo Hajiya tana ta nacin taje wajenta amma tak'i, don haka takanas ta tura kasuwar rana aka siyo mata wata k'atuwar 'yar tsana, ai kuwa tana ganinta ta tashi da sauri har tana fad'uwa ta nufi wajenta, aka yi ta dariya.

A yanzu Fadeelah ta sake da 'yan babban gida sosai, don Adam ya taka muhimmiyar rawa wajen kawo ta akai akai har komai ya fara yin sauk'i a ranta, wannan fargabar da take yi akansu ta shud'e.

"Kin san Kawu sulaiman ne ya shigo yana tsokanata wai munyi wariyar 'yanuwantaka mun ture maza a gefe in ba haka su ina nasu k'ullin."

Mairo ta fad'a mata lokacin da suke k'arasa shirinsu a cikin d'akin Aunty Hassana bayan an gama aikin kayan.

"Kin san nima kwanaki da muka zo haka yayi ta jana da hira har yana ce masa wai ai zai zo ya kawo min babbar 'yarsa ta min hutu."

Mairo ta gyad'a kanta kafin tace.

"Ina ga shi da sauki ma tunda 'yan kewaye-kewayensa yake tayi, amma gwaggo Lami jiya fa bayan kun fita da Aunty Hassanah aikowa tayi wai a kai mata su Afra su gaisa, wallahi kasa rufe baki nayi saboda mamaki."

Duniyar kenan! Fadeelah ta ayyana a ranta, a da wace irin kiyayya ce mutanen nan biyu basu gwada mu ba, Kawu sulaiman yana d'aya daga cikin wad'anda suka haddasa tsanar innarsu a zukatan 'yan Babban gida, sannan takakkiya yayi har Abuja don ya d'auko ta a gurfanar da ita gaban shari'a, innarsu kuwa wace irin bak'ar wuya ce bata sha ba a wajen gwaggo lami.

Hirarsu ta katse lokacin da Ummi 'yar gidan Aunty Hassanah ta lek'o ta sanar dasu cewa an aiko cewa mata su fito.

Sanda suka isa harabar wajen da kowa ke ta hayaniyar samun wajen zama tare da makusantansa, zuciyar Fadeelah tayi mak'il da farin ciki ganin d'imbin al'umar da gabad'ayansu ke amsa sunan 'yan uwanta, ta tuno wani lokaci can baya daya wuce sanda take ganin kamar ita kad'ai Allah ya halitta a duniya bata da kowa a duniya sai su Mami kawai, Hakika dukkan wani farin cikin duniya in zaka dubi asalinsa yana komawa ne ga DANGI!

Taron ya tafi kamar yadda aka tsara komai, anyi zumuncin daya zama mak'asudi, anyi nishad'i, anyi raha kuma anci an k'oshi. Bayan nan Kawu Danjuma da wasu daga cikin dattijan gidan sunyi nasiha mai k'arfi akan muhimmanci zumunci da kuma irin k'alubalen da suka fuskanta a baya na rashin samun fahimtar juna tsawon shekaru, an yiwa wad'anda suka rasu addu'a, an yiwa Habiba fatan samun waraka, an sake jan hankali da nuna illar abinda Sule ya aikata, sannan kuma anyi fatan wannan taron zai k'ara had'in kai tsakaninsu kuma za'a yi k'okarin d'orar da hakan. Kawu Bashir kuma ya tsara cewar kafin zuwan wani taron za'a sanar da wad'anda ya kamata don kowa ya kawo gudunmawarsa ba kamar yanzu da kusan komai ya ta'allak'a akan Adam kad'ai ba.

Adam. Shi da Sa'id sun sha d'imbin godiya a wannan ranar da addu'a da kuma fatan alkhairi, kowa ya yarda cewa zuwansa cikinsu alkhairi ne mai d'imbin yawa, don duk yawan jama'ar babban gida babu wanda za'a d'ebe da zai ce bai tab'a samun alkhairinsa ba, shi kad'ai ne amma kuma yana da hannaye da yawa, yasha d'imbin godiyar da in har tana yawa a wannan ranar za'ace tayi, don tun yana iya amsawa har ya zama sai murmushi kawai yake yi.

Fadeelah na iya hango yadda yake lumshe idanunsa daga inda take zaune rik'e da Muhammad da yayi bacci a kafad'unta, yadda kyallin idanunsa ke tafiya tare da murmushin.

A cikin 'yan watannin nan rayuwarta ta canja, ta samu wani irin farin ciki da bata san dad'insa ba sai a yanzu, Adam ya cike rayuwarta da soyayyarsa, ya nuna mata kala-kala na ma'anar kulawa ta yadda ko a murmushinsa idanunsa na gaya mata cewa yana son ta, tana ganin wata gaskiya a cikinsu kullum dake sawa ta yarda cewa ba zai tab'a rabuwa da ita ba, idan kuwa ya rik'e hannunta tana k'ara yarda cewa tana cikin kulawarsa ne kuma har abada ba zai tab'a bari ta fad'i ba.

Zata yini tana jin maganganun mutane amma duk lokacin da take tare dashi, kewayenta nutsewa yake cikin wani ruwa mai zurfi, bata tab'a iya fahimtar komai sai shi kawai da kuma al'amarinsa, wanda itama a yanzu ta koya don bata shakkar nuna masa nata b'angaren k'aunar, rayuwarsu tana tafiya daidai manne da wani malik'i daya had'e zuciyoyinsu guri d'aya.

Zuwa can yamma bayan komai ya natsa an kammala taron ne ta samu wayar Mami.

"Mami tun safe nake ta kira shiru, d'azu kuma hayaniya ta hana ni sake gwadawa."

"Yi hakuri Deelah, naje makarantarsu Iman ne zancen lesson d'inta, ya kowa da kowa? Munyi waya ai da Aunty Saratu jiya take ce min bakya gida lokacin."

"Ina jin sanda muka je cikin gari ne, dama tambayarki zanyi kayan k'amshin na nawa za'a siyo?"

"Na 3 thousand ma ya isa, sannan idan zaki iya a taho min da daddawa ta 1 thousand."

Sarai ta san me Mamin take nufi da idan zata iya, tana nufin idan warinta ba zai takura ta ba kenan, don Mami ce ta farko duk duniya data fara ganewa tana da ciki kafin ma ita kanta, kuma tun daga wannan lokacin kulawar da take mata ta ninku akan da.

"Insha Allah Mami za'a taho da ita. Yauwa dan Allah ki gayawa Zahra tayi wa mai k'unshin magana idan mun dawo jibi zamu je."

"Au yanzu baku hak'ura da wannan k'unshin ba, tunda baku samu ba har anyi taron an gama ba sai ku bari sai wani lokaci ba."

Sai ta girgiza kai kamar Mamin na kallonta tace.

"A'a Mami dan Allah, zamu je dai."

A yadda Adam ya kwallafa ransa tayi k'unshin nan ta yaya zata iya ce masa ta fasa? Watakila Mami ta fahimci zancen nata ne shi yasa suka yi sallama akan hakan ba tare da ta sake cewa komai ba, kuma kafin Mamin ta kashe, tana iya jiyo muryar Iman wadda ke kwalo mata ihun 'Aunt deelah yaushe zaki dawo?'_ Taso sunyi magana don alkawari Iman d'in a mata cewa zata zo tayi mata weekend in ta dawo, karo na farko kenan da Mami zata barta tazo sa kwana don koyaushe sai dai suzo suyi mata yini kawai su tafi.

Da daddare bayan komai ya tsagaita ne text d'in Adam ya shigo wayarta.

"Babeim (Turkish; My baby) zan iya ganinki dan Allah?"

Dama kiranshi take jira don ta san halinsa sarai ba lallai ne yaci abinci a wannan hayaniyar ba, don haka ta d'auki ledar takeaway-takeway na abincin data tanadar masa tace da Mairo wadda ke k'okarin yiwa su Afrah wankan kwanciya tana zuwa, so samu ne ace itama tayi wankan kafin ta fita, amma ta san Adam ba hakurin jiranta zai yi ba.

Babu mutane sosai a k'ofar gidan amma duk da haka motar tasa na daga can gaba hanyar wata kwana da mutane basu fiye zama ba. Sai da ta k'arasa sannan ta fahimci motar Sa'id ce bak'a wuluk mai d'auke da tinted glass a jikin tagogin, tayi kokarin bud'e k'ofar gaba amma taji ta a rufe gam saboda haka ta dawo ta bud'e baya.

Sanyin AC da kuma tsadadden k'amshin nan nasa suka fara yi mata maraba kafin siffarsa, da alama daga can guest inn d'in da suka sauka yake don yayi wanka ya canja manyan kayan daya yini dasu zuwa wani 3-quater wando sak irin socin sojoji da kuma bakar T-shirt mai laushi data kama jikinsa, Ya Allah! Ita kam tun kayan rana ne a jikinta.

Kansa a jingine yake saman kujerar ya rufe idanunsa, kuma bai bud'e su ba har bayan shigowarta, a haka ya amsa sallamar da tayi.

A lokaci guda ta fahimci akwai abinda ke damunsa, ba dai gajiya bace don ta san wannan d'an taron kawai ba zai jijjiga shi ba.

"Daga wani waje kake ne?" Ta tambaya jin bashi da alamun magana. Yayi murmushin jin muryarta kafin yace.

"Eh na koma masauki nayi wanka ne."

"Kaci abinci?"

Sai ya d'ago da kansa a lokacin ya kalle ta, amma bayan kyakkkwar fuskar ta har yanzu akwai wani jan haske da yake gani a gefen idonsa. Irin hasken da tunda yake sau d'aya ya tab'a ganinsa a rayuwarsa, watanni biyu da suka wuce, lokacin da sab'anin farko ya shiga tsakaninsa da Fadeelah.

Ranar da yana duba hotunan wayarta ya tsinci wani hoton ta tare da Al'ameen, sun d'auka ne a cikin wani library cikin sigar selfie, dukkaninsu na dariya yayin da Fadeelah ke kallon camerar amma shi ya juya yana kallonta, yana kallonta... Irin kallon da shima yake mata in yan tare da ita, a wannan ranar kwanan wayar nan ya kare don fasa ta yayi har batirinta.

Tun da yake a rayuwarsa bai taba tunanin Al'ameen d'in Fadeelah shine Al'ameen d'in da shima ya sani a America ba, duk da ba wani sabo suka yi ba amma zai iya cewa sun had'u kusan sau biyar ta hanya abokinsa Kamal daya taimaka masa a baya game da binciken asalinsa, a wancan lokacin zuciyarsa ta kwanta da Al'ameen ne kasancewarsa sabon lauya mai kokarin cimma burinsa, amma a yanzu hoton fuskarsa a k'one yake zuwa idanunsa a kullum.

Kuskuren da zuciyarsa tayi a wancan lokacin shine na kasa rik'e fushinsa har ya fasa wayarta kuma ya bari zargi ya shiga zuciyarsa na tunanin ko har yanzu Al'ameen bai gama barin zuciyarta ba, don a yadda hoton nan ya fassara masa komai, gani yake mu'amarlarsu tayi k'arfin da ba lallai har a lokacin nasa kokarin yayi nasarar cire shi a zuciyarta ba, ko don kyawun fuskarsa ma.

Don haka karo na farko aka samu sab'ani tsakaninsu har na tsawon kwanaki biyu, Fadeelah tayi fushin data daina yi masa murmushi balle dariya, bata fasa yin dukkan wata d'awainiya ta gidan ba amma komai yayi duhu a idanunsa, gidan ya zama babu haske balle nutsuwa, da kansa ya gano kuskurensa ya koma ya nemi yafiyarta. Shin irin wannan kuskuren yake son sake aikatawa a yanzu? Dukkanin wata kafa ta kwakwalwarsa ta shiga kokarin hana shi abinda yake shirin tambaya amma ya kasa danne zuciyarsa.

"Leelah waye Abdoul?"

Yana kallon yadda fuskarta ta canja a lokaci guda zuwa tunani, goshinta ta takure waje d'aya.

"Abdoul? Waye shi?" Ta maido masa da tambayar.

Ya d'aga kafad'unsa kad'an.

"Mun had'u dashi ne a masallacin da la'asar bayan mun gaisa sai naji yana gayawa abokansa a bayana cewa da shine zai aure ki."

Ta d'an yi shiru kamar mai nazari, bayan wucewar wasu 'yan sakanni kuma ga mamakinsa kawai sai ta kyalkyale da dariya tana kallonsa.

"Seriously Wolfie? Shine zaka cinye ni d'anya?"

Bai san lokacin da yayi murmushi ba shima jin sunan data kira shi, zai iya rantsewa ba'a kwana biyu a duniyar nan Fadeelah bata canja masa suna ba, suna nan da yawa... Big guy, boobear, bunches, captain, cowboy, charmy, heartthrob, hoshi, habibi, Oppa, Ironman, Jaan, Ma cherie.... Ba zai iya lissafo su ba.

"Allah ya huci zuciyarka tough guy, ni wallahi yanzu in zaka shak'e ni ko kammaninsa ba zan iya ganewa ba, amma dai na tuna shi abokin yaya Salisu ne daya tab'a min magana sau d'aya, amma kafin ma a samu damar da zan bashi amsa k'addara ta d'auke ni zuwa hanyar da zan had'u da kai, so cool off kaci abincinka ka daina tunanin...."

Kafin ta k'arasa abinda zata fad'a, Adam ya jawo ta cikin jikinsa ya zagaye ta da dukan hannayensa, ya riga ya samu amsar sa kuma baya son shaid'an ya sake samun tasiri akansa, a hankali idanunsa ya sauka kan bakinta. "I miss you." Ya fad'a muryarsa k'asa-k'asa.

Nan take jinin jikinta ya sake d'aukar d'umi yana neman tafasa don jikinta da zuciyarta sunyi kewarsa kamar babu gobe, kwanansu biyu kenan da zuwa Ikara ita da Mairo, tun ranar Alhamis suka taho shi? kuma sai jiya juma'a ya k'araso tare dasu Sa'id, kuma tun a jiyan waya kawai suka yi don shirye-shirye sun sha kan kowannensu, a yau kuma wayar ma bata samu ba sai hango shi kawai da ta dinga yi tare da mutane.

Ta d'ago da fuskarta kad'an yadda karan hancinsu ya had'u da juna sannan ta mik'a da hannayenta ta zagaye su a wuyansa. "I miss you too."

D'aya hannunsa ya lalubi cikin k'asan rigarta yace.

"Babyna fa?"

"Shima yayi missing d'inka like crazy."

Sai yayi wani murmushi a hankali, sautin ya fito daga can k'asan mak'oshinsa.

Fadeelah ta nutse cikin d'umin jikinsa wanda ke had'e da k'amshin sabulu da turare sannan a hankali ta rufe idanunta sanda ya sunkuyo da fuskarsa kan tata, wata wuta kamar ta lantarki ta harba tsakanin fuskarsa zuwa tata, lebbensa masu taushi da d'umi suka d'aga ta zuwa cikin gajimare.

Zuciyarta ta manta da komai ta biye masa na wani lokaci kafin kuma ta tuna inda suke, da sauri ta janye jikinta sannan ta matsa gefe.

"A mota muke fa." Tayi k'okarin tuna masa.

Sai ya jefa kansa jikin kujerar motar sannan ya zura hannu cikin gashinsa yana sauke numfashi yace.

"I'm sorry Babeim, na manta ne." Muryarsa ta fito a shagale kamar mai jin bacci ko wanda ya tashi.

Murmushi mai taushi ya sub'uce a fuskarta sannan ta juya ta d'ebo kayan takeaway d'innan, tace.

"Bismillah, time to eat."

"Yes Babe." Ya fad'a sanda ya juyo gabad'aya saitin ta ya tankwashe k'afafunsa akan kujerar motar sannan ya sake jawota jikinsa.

Ta d'ora abincin akan cinyarta sannan ta shiga bashi a baki, yana rik'e da d'aya hannunta sannan a hankali kuma wannan lallausar muryar tasa tana mata mitar yadda yayi kewar girkinta.

Idanun Fadeelah suka ciko da wata irin kwallar farin ciki da kuma godiya ga Allah, 'yan shekaru da basu fi cikin hannu ba a baya,? rayuwarta a hargitse take bata ma san wacece ita ba balle har tayi tunanin samun dad'in rayuwa haka,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login