Showing 129001 words to 132000 words out of 153964 words

Chapter 44 - BAYAN NA MUTU Book Original By Aisha Shafii.doc

30 Aug 2025

3809

ta manta da hakan don a lokacin ta k'okarin farfad'owa take, sai kuma rasuwar Sadiya da zancen rashin lafiyar Adam tazo ta danne maganar a zuciyarta.

Saboda haka yanzu ta fahimci zancen na Mami, k'okarin shirya tafiyar su Zahra can Washington take yi saboda bikin nasa yazo.

A lokaci guda taji kwarin jikinta na neman guduwa kamar an zare mata laka, amma bata ga dalilin da zai sa taji hakan ba don ana shirin bikin Al'ameen... mutumin daya yaudareta, ya kuma tilastawa Mami akan ta taya shi b'oye cewa zai aure ta ne ba da izinin mahaifiyarsa ba, Allah ya sani bata ji haushin Mami na yin hakan ba ko kad'an, saboda ta san irin yadda ta d'auki Al'ameen kuma watak'ila a lokacin ta fahimci itama tana son shi. Sai ta mik'e daga wajen gabada'ya ta koma cikin d'akin Aunty Hassanan ta kwanta.

Tunaninta ya gangara kan maganar da ta tab'a gayawa Al'ameen a America, lokacin daya fara cewa yana sonta.

Zuciyarka ta gaya maka tana sona, saboda haka kana k'okarin bata abinda kake so ne kawai ba tare da tunanin halin da ni zan shiga ba.

Na gaya miki...

Baka gaya min komai ba Al'ameen sai son zuciyarka kuma na fahimce ka sarai saboda haka nima ka fahimce ni ka fita daga rayuwata, na fad'a maka bana sonka kuma bana sonka a cikin rayuwata.

A yanzu ta kuma yarda Al'ameen son zuciyarsa kawai ya sani, baya tab'a duba halin da waninsa zai shiga illa tabbatuwar abinda yake so kawai, sanda ake shirin bikinsu, bai damu da yaya mahaifiyarsa zata ji ba in har ya aureta ko kuma ita kanta ta yaya zata iya rayuwa a inuwar wadda bata k'aunarta.

Duk abinda ta gaya masa a wancan karon gaskiya ne, abu d'aya kawai da tayi k'aryarsa shine da tace bata sonsa, wannan k'arya ne, ta so shi a wancan karon kuma ta so shi a lokaci baya kad'an saboda iya mu'amala da kuma kyawunsa, amma banda yanzu... Yanzu data shiga duk wani nau'i na kalar rayuwa ta fito harda kuwa wanda ya sata a ciki.

Ta ja guntun tsaki kafin ta janyo hijabin Mairo dake gefe ta rufe fuskarta dashi.

Alak'arta da yayarta ta gyaru tun daga ranar da aka sallame ta daga kotu, a ranar data fahimci cewa ba wai abinda kake dashi ne a rayuwa mai muhimmanci ba, illa wanda kake dashi a rayuwarka.

Don haka a yanzu kullum tare suke kwana suke tashi cikin tarin labaran da basa yankewa akan abubuwan da kowannensu ya shiga bayan zamanin da suka rabu, sai dai hirar bata tab'a gangarawa kan shari'ar da aka gama da kuma d'an zaman kurkukun da tayi, ta fahimci Mairo na k'ok'arin tallafota ne don ganin ta farfad'o ta saki jikinta sosai, saboda ko zancen fasa aurenta sau d'aya ta tab'a yi mata shi da fatan Allah yasa hakan shine mafi alkhairi ya kuma bata wanda yafi shi. Sannan itama bata fiye yi mata zancen mijinta ba illa na 'ya'yanta kawai, kuma hakan ya taimaka sosai wajen wanke zuciyar kowannensu daga uk'ubar da suka fito.

Kawu Ibrahim yace zata koma wajensu Mami in al'amura sun natsa amma ita gani take yanzu ba zata iya tafiya tayi nisa da Mairo ba. Aunty Hassanah ta gaya mata dukkan irin abinda ya faru da mijinta da kuma irin zirga-zirgar wahalar da yake yi na ganin ta koma, wanda har yanzu bai samu kwakwakwaran mutum d'aya da zai tunkara a Babban gida ba hatta kuwa shi Kawu Ibrahim d'in, daga shi sai su Saminu masu taimaka masa ke ta bulayinsu har yanzu.

Ita kanta bata son Mairo ta koma wajen mutumin daya cuce ta, amma Aunty Hassanah tace komawar tata shi yafi ko don k'ananan 'ya'yanta da ba'a san hannun wa zasu fad'a ba in har ta dage dole sai ta rabu dashi. Zuciyarta ta cigaba da sak'e-sake cikin duhun hijabin da yayi mata dad'i a fuska kafin a yaye shi.

"Tunanin me kike yi?"

Mairo ta tambaya tana zama a gefen gadon.

Ta d'ago da idonta ta kalle ta daga kwancen, bata san yaushe tayi wanka ba amma ta canja hijabin jikinta zuwa wani sea green daya k'ara haskata, Allah ya sani dole ne mijinta ya nace da bibiyar ta koma gidansa don Mairo tana da kyau, irin kyawun da ta tabbata koina zata shiga a fad'in duniya babu wanda zaiyi mata kallon daban, saboda irin wannan kyan ne da d'aid'aikun mutane kawai Allah ke zab'a cikin jinsi ya azurta su dashi..

"Wai nace tunanin me kike yi?"

Ta sake katse ta da alamun damuwa a fuskarta.

"Ba komai..." Ta amsa tana k'ok'arin cire wani guntun farce a yatsanta na hagu.

"... Kawai tunaninsu Afran ki nake, ina son in gansu ko suna kama dake."

Da jin haka sai ta janyo hijabin da ta cire a fuskarta ta shiga ninkewa.

"Kar ki wani damu kanki da wannan tunanin, d'azu Saminu yazo yake ce min Babansu yace zasu zo tare da 'yanuwansu suyi gaisuwa."

Sai ta tsaya daga k'ok'arin cire farcen.

"Da gaske? Yaushe zasu zo?"

"Ban sani ba gaskiya, zancen da nazo gaya miki ma daban ne, Saminun yace min wai an sallami Adam daga asibiti, an maida shi gida yanzu."

Adam. Asibiti. Kalaman suka yi nauyi a cikin zuciyar Fadeelah, yau kwanaki uku kenan, tun ranar da aka sami labarin rasuwar Sadiya, Sa'id yayi waya cewar Adam ma ya tashi da wani irin zazzab'i har asibitin da suka je sun rik'e shi, don haka tun wannan ranar mutane ke zarya daga wajen makokin zuwa cikin Zariyan dubo shi. Bata samu tayi magana dashi a ranar da aka sallame ta ba don bata ma k'ara ganinsa ba tun bayan da aka gama zaman kotun, tayi tunanin zuwa dubo shi itama amma ta san Kawu Ibrahim ba zai bari ba.

Don tun sanda suka shigo b'angaren Aunty Hassana a daren da k'afarta ta tako cikin Babban gida bayan tsawon wasu shekaru, bata lek'a koina ba, ko mutanen dake zuwa ganinta ma kad'an ne saboda rasuwar Sadiya data d'auke hankalin kowa, kuma hatta manyan babu wanda yayi wata magana har yanzu.

"Ya warke kenan?" Ta tambaya a hankali tana kallon Mairon wadda ta girgiza kanta.

"Saminu yace a yadda ya ganshi jiya dai yana jin jiki, watakila saboda zirga-zirgar dubo shin da ake yi ne ya matsa sai ya koma gida. Kin san wanda ba bahaushe ba ba lallai yaso wannan jelan na mutane ba."

Sai ta gyad'a kanta a hankali tana k'ara tuno gutsirarrun labarin Adam wanda Mairo ta tsinta itama ta gaya mata. Komai ya bada ma'ana a cikin labarin, abinda kawai bai bada ma'ana a cikin kanta ba shine me yasa daya ganta yak'i nuna ya santa? Don ko sama da k'asa zata had'e baza ta tab'a yarda cewa ba shine Adam d'in data sani a America ba.

"Wallahi da Kawu zai yarda, da gobe Saminun ya kaimu munje mun dubo shi, mutumin da yayi maka babban taimako ai ya wuce irin wannan uzurin ya hana ka dubo shi."

Cewar Mairo, ta cigaba da cewa.

"Bawan Allan nan yana da kirki Bintu, d'an zamana a gidan nan baki gayadda yake hidima da mutane ba, yanzu haka fa komai na d'awainiyar b'angaren nan shi yake yi, sannan Aunty Hassana tace min yanzu duk mai wata buk'ata a Babban gida Sa'id kawai ake samu a fad'awa, da ya gaya masa shikenan wallahi ko nawa ne zai bada, shi kansa Kawu D'anjuman ba k'aramin sauk'in abubuwa ya samu ba da zuwansa, bashi da kyashi ko kad'an irin na al'adarmu."

Tana rufe baki Mami ta shigo d'akin.

"Har kin fito daga wankan? Banga wucewarki ba." Ta tambayi Mairo kafin ta sami bakin gadon itama ta zauna.

"Na fito Mami, kuna ta magana da Aunty Saratu na wuce."

Mairo ta amsa da murmushi.

"Sannu Fadeelah, ya gajiyar jikin naki?"

"Da sauki sosai, Aunty Saratu tayi min gashi jiya naji dad'in jikina."

"Toh Allah ya sawwak'e, d'azu dana shigo Kawu Ibrahim yake ce min ya kira Daddy a waya cewar muzo wani satin akwai zama da za'ayi, ya gaya muku?"

Mairo ta girgiza kai.

"Wallahi bamu sani ba, kuma jiyan nan ma muke zancen komawar tata."

"To watakila sai ranar in munzo zamu tafi tare, Deelah na d'ebo miki wasu kayan sakawar, Hassanah ta tura yaranta su karb'o miki daga wajen Farouk."

"Toh Mami, Madallah."

"Yanzu zamu tafi kuma, Farouk yace jirgin da zamu bi k'arfe uku zai tashi, kina ganin zaki iya fitowa soro ku gaisa dashi? Nayi nayi ya shigo yace wai mutane sunyi yawa."

A Babban soron shigowa cikin gidan suka sami Farouk bayan Aunty Hassanah da Aunty Saratu duk sun amince cewa taje d'in, Fadeelah ta cika da mamakin ganin yadda ya fara ajiye k'asumba a 'yan watanni kawai da ta rabu da ganinsa. Taso ta tambayeshi su Usman da harkar makaranta amma ta lura kallon da yake mata na tsantsar tausayawa ne don haka ta bar zancen sai ta koma gida tukunna.

Motar da suka d'auko ta kawo su Ikara daga airpot d'in Kaduna na tsaye a gefen hagu na k'ofar gidan kasancewar rumfunan zaman makokin daga dama suke, don haka ita da Mairon data rako ta suka lek'a kad'an har zuwa tashinsu.

Sai dai me? Motar tasu na tashi wata k'erarriyar mota k'irar Ford ta maye gurbinta, kuma kafin tayoyin motar su kai ga gama tsayawa ko kuma kafin su Fadeelan su kai ga juyawa cikin gida.. Wanda ke zaune a mazaunin direba ya bud'e k'ofarsa da wani irin sauri ya fito.

Wucewar 'yan sakanni kawai kafin idanun Mairo su daukar mata siffar Sadiq tsaye yana kallonta, bata k'ara ganinsa ba tun bayan ranar daya kawo ta saboda a haka kamar yadda yake kallonta da mamaki itama mamakin ne ya tsayar da k'afafunta daga juyawa ta koma ciki, sai da sauran k'ofofin motar suka shiga bud'ewa ne sannan komai ya tarwatse, ta juya da sauri tayi cikin gidan.

Fadeelah ta bita da kallo kafin ta dawo ta sake kallon mutumin dake tsaye a gefen bud'add'iyar k'ofar motarsa, da farko bata gane shi ba sai a yanzu data juya sannan taga kamar an saka wani abu daya zabge shekarun fuskarsa ya hasko mata shi a sanda ta sanshi... Sanda take raka Mairo bayan gari ta had'u dashi, da sanda Mairo bata fahimtar komai in ba kalamansa ba... ta gane shi sarai da sunan mutumin daya zama farkon hargitsa rayuwarsu.

Daga cikin sauran k'ofofin motar da suka bud'e, mata uku da maza biyu suka fito, a hannun d'aya daga cikin matan wani abu ne daya zuk'e duk fushin dake shirin tasiri a zuciyarta, wani d'an farin yaro tas! da kammaninsa ke baiyana cewa jinin Mairo ne sannan rik'e a hannun d'aya daga cikin mazan, yarinyar da bata wuce shekaru biyar ba sanye cikin wasu milk kaya masu kyau!

Fadeelah taji kwalla ta cika idanunta a take, taji dama tana da iko da lokaci a sannan, da ta dawo da rayuwar baya lokacin da innarsu ke raye, ta hasko mata wannan lokacin don taga 'ya'yan Mairo, 'ya'yan da rabo ya rantse akansu ya zama dole ta tsallake mahaifarta a wancan lokacin don su zo duniya, sai kawai ta k'arasa gurin matar dake rik'e da Muhammad ta karb'e shi.

Mairo tayi zaman dirshan kan gadon Aunty Hassanah tana sak'e-sake a ranta, ta san cewa a wata guda daya wuce zuciyarta ta yanke mata cewa bata damu da mijinta ba, ta d'auki kudirin yanke duk wata alak'a dake tsakaninsu ta kuma yi alk'awarin cewa zata yi nesa da duk wani abu daya dangance shi, amma ganinsa kawai da tayi yanzu ya tuna mata da cewa Sadiq ne fa!

Wannan Sadiq d'in da taso fiye da komai a rayuwarta, d'an bafulatanin nan da tun gani na farko da tayi masa a bakin rijiyar da suke zuwa d'ebo ruwa taji zuciyarta ta fad'a duniyarsa... Ta rufe idanunta????? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ?  a hankali tana tuna banbancin yadda ta barshi da yadda yake a yanzu, kammaninsa sak! suke dana mutumin da yayi nesa da kwanciyar hankali.

Ya tara gemu har da gashin baki, gashin kansa babu taza sannan daga takalmi har hular kansa basu dace da dogwayen kayan daya sanya ba... A baiyane yake cewa rashinta ya tab'a shi ta kowanne b'angare don kammanin fuskarsa ma kad'ai sunfi kama dana mara lafiya. Sai dai duk da haka, ta san ko kad'an halin da yake ciki bai kamo k'afar irin halin da ita ya sakata a ciki ba.

Sallamar Mairo ta katse tunaninta, tana d'ago ido kuwa zuciyarta dake da rauni ta sake karyewa ganin Muhammad rik'e a hannunta, shima ya rame kad'an sannan yayi d'an wuya.

"Afrah tana wajen sauran, gasu nan sun shigo falo."

Fadeelah ta fad'a tana k'ok'arin mik'a mata Muhammad d'in, sai dai me yana had'a ido da ita ya juya kansa sanann ya fara kuka alamun ba zai je ba.

"Kaga fa, mominka ce." Cewar Fadeelah, amma maimakon ya fahimce hakan sai ma k'ara tsallara kukan da yayi ya shiga zillewa yana k'ara k'ank'ame jikin Fadeelan, sai kawai itama ta juyar da kanta gefe ta fara hawaye, dama ta sani cewa alhakin Muhammad ba zai barta ba, ta yakice shi daga jikinta a sanda lokacinsa bai kai ba, don haka dole ne yayi zuciya da ita.

Tayi saurin goge hawayenta sanda Aunty Saratu tayi sallama, biye da ita Zakkiyya ce da k'annen mahaifiyarsu su biyu, ta zamo daga kan gadon sanda su suka zauna akai. Afrah na ganinta kuwa ta janye hannunta daga cikin na Zakkiya ta fad'a jikinta tana fad'in.

"Mommy Oyoyo, mommy oyoyo!"

Karo na farko tun bayan rabuwarta dasu itama ta rungume 'yarta sannan ta cusa kanta cikin wuyanta ta shiga gaishe su.

"Lafiya k'alau Maryam, ya hakuri kuma?" Suka had'a baki wajen amsa mata.

"Alhamdulilah." Muryarta ta fito a hankali.

Aunty Saratu ta nuna Fadeelah tace.

"Ga k'anwarta nan, wadda aka sallama daga kotu."

Mairo tayi shiru tana saurarar rad'ar da Afrah ke mata yayin da suke barka da kuma yiwa Fadeelah jaje.

"Mommy kullum sai nace Daddy ya kawo ni wajenki amma sai yayi tace min sai gobe, kuma nace masa ya yanke farcensa yace wai bai iya ba sai kin dawo zaki yanke masa."

Tayi kokarin maida kwallarta sanda yarinyar ke tambaya.

"Momy yaushe zaki dawo? Zaki dawo?"

Har kusan yamma Muhammad bai yarda yazo wajenta ba, harkarsa kawai yake kuma duk wanda zai d'auke shi zai yarda amma banda ita, zuciyarta duk tabi ta cunkushe sannan Aunty Hassanah kuma tayi ta binta da kallon 'Me na gaya miki?'

Sauk'in da ta samu d'aya ne da su Zakkiyan suka tashi tafiya anan suka barsu da yake dama da kayansu aka zo, kuma kamar lokutan baya Sadiq bai nemi ganinta ba haka su Aunty Rabi ma basu yi mata zancensa ba, gaisuwar da suka zo don ita kawai suka yi suka tafi.

Afrah na mak'ale da ita duk inda tayi, amma Muhammad a wajen Aunty Hassanah ya kwana don daga baya Fadeelah ma k'in yarda da ita yayi, watakila ya gano kammanin ta da mahaifiyar data wullar dashi ne.

Washegari Juma'a Saminu yazo mata da wani labari bakinsa a washe kamar gonar auduga, cewar a jiya Kawu Ibrahim yayi magana da Sadiq har kuma yace dashi yazo wani satin ranar laraba tare iyayensa. Mami bata gaya musu ranar da Kawu Ibrahim yace suma su zo ba, amma bayan ta shaidawa Fadeelah, sai dukkaninsu suka yarda cewa rana d'aya ne da sanda su Sadiq zasu zo.

Zatonsu ya kara tabbata ne da daddare lokacin da Aunty Hassanah ta dawo daga b'angaren iyayen Said, tace dasu mahaifiyar Said d'in tayi waya dashi yace mata da jibi zasu zo amma Kawu Ibrahim yace su zauna jikin Adam ya k'ara warwarewa tukunna ranar laraba sai su zo.

Haka kowannensu ya kwana a ranar da tunanin wane irin taro za'ayi RANAR LARABA?

***

LARABA, TA BAWA RANAR SA'A!

Adam ya gyara zamansa kad'an ya jawo hannun rigar Said dake gefensa, sannan ya mik'a wuyansa saitin fuskarsa yace.

"Nawa ka ciro a Atm d'in?"

"Dubu d'ari kamar yadda kace, wai kud'in meye?"

"Ban sani ba, jiya ne ya kira ni a waya yace in taho da 50k."

Har Said zai sake magana magana k'ofar falon ta Kawu D'anjuma ta bud'e, mata suka fara shigowa d'aya bayan d'aya suna zama a d'aya b'angare na d'akin, idan har Adam zai iya rik'ewa to a b'angaren da suke zaune, kusan duk wani namiji babba daya mallaki hankalinsa a Babban gida yana wajen. Bai rayu tare dasu ba amma zai iya tabbatar da cewar ba'a tab'a irin wannan zaman daya had'a da kowa da kowa a gidan ba har kuwa da mata.

Kawu Ibrahim ya riga ya gaya masa cewa zama za'ayi na gidan gabad'aya saboda haka tun da suka taho a hanya daman ya shirya samun hayaniyar mutane, ilai kuwa abinda ya tarar kenan, da wad'anda suka je duba shi asibiti dama wad'anda basu sami damar zuwa ba haka suka yanyameshi kowa na fad'in yaya ya k'ara ji da kuma fad'in cewa ya rame.

Ya kai hannu ya tab'a wuyansa kad'an, shi kansa ya san ya rame don zazzab'in da yayi mai zafi ne, kwana biyu baya cikin haiyacinsa bacci kawai yake yi a k'asan allurorin da ake masa, bayan ya farka kuma jikisa yayi nauyi da yawa don haka ya rasa k'arfi mai yawan da har yanzu bai dawo daidai ba.

Ya d'ago da idonsa ya sauke akan k'ofar da matan keta shigowa ciki, jiran shigowar Fadeelah kawai yake don ko bayan ya farfad'o daga tasa rashin lafiyar, tunani yake idan nata idanun sun farfad'o, so yake yaga ta koma daidai kamar yadda take a baya, so yake tayi jinyar zuciyarta a d'an k'ank'anin lokaci ta kuma warke, baya fatan ace ta rik'e komai a ranta don in har ta cigaba da wahalar da kanta, shima zai cigaba da wahala ne da tunanin halin da take ciki.

Daga bayan yayarta Maryam, Fadeelan kuwa ta shigo sanye da wani dogon hijabi kalar coffee daya rufe jikinta ruf! in banda fuskarta data haska cikin duhunsa. Fatansa ya karb'u sanda suka had'a ido... Ya hango wani kyalli da rabon daya ganshi a idanun nata tun sanda suka rabu a America sannan kuma kalarsu ma ta daidaita, sai kawai ya samu kansa da yi mata wani guntun murmushi, labari mai dad'i shine itama ta mayar masa kafin ta nemi waje ta zauna.

Fadeelah ta sunkuyar da kanta k'asa bayan ta zauna, rabonta da shigowa d'akin nan tun zamanin baya a wannan ranar data canja akalar rayuwarta, ranar data gudu daga Babban gida, ranar da Kawu Ibrahim ya ceto ta daga hannun su Salisu dake mata dukan mutuwa, sannan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login