Showing 42001 words to 45000 words out of 153964 words

Chapter 15 - BAYAN NA MUTU Book Original By Aisha Shafii.doc

30 Aug 2025

3779

nesanta da juna, ashe k'addara ta tanadi wata hanyar, don ta d'auki wannan zuwan nasa a matsayin k'addara duk da cewa aikin gabansa ne ya kawo shi... k'addarar da take tunanin zata saita ta a yanzu da iya kokarinta.

Ta jera dukkan abinda ta gama soyawa a tray sannan ta fita dasu falo, Tv a kunne take tana nuna labaran BBC yayin da Daddy ke zaune a kujerar dake fuskantarta, a gefensa Al'ameen ne shirye cikin wata hadaddiyar gray suit kamar an auna ta a jikinsa, ya fito a kamanninsa na matashin lauya, hasken safiyar ya haska mata kyawun fuskarta da bata gani gabad'aya a daren jiya ba, kyawun fuskar daya rud'e ta a baya ta fad'a tarkonsa cikin wannan watan guda d'aya!

Magana suke yi da alamu mai muhimmanci, don ya sunkuyar da kansa kad'an yana kallon Daddyn, amma fitowarta yasa ya wulkito da idonsa ya kalle ta tsaye daga kofar kitchen d'in, sai ta juya da sauri ta nufi dining ta ajiye tray d'in sannan ta koma, haushin kanta taji sosai yadda ya kamata tana kallonsa.

"Deelah, fito da dankalin daga cikin fryer nan."

Mami ta fad'a har a lokacin tana waya, sanda ta koma falon babu kowa don haka ta shiga jera warmers d'in data d'auko a gefen sauran kayan kan tebur d'in.

Motsin tsayuwarsa a kusa da ita taji ba tare da taji sanda ya taho ba, ta rufe idonta a hankali had'e da guntuwar addu'a don bayan gaisuwar jiya, bata so ko kad'an wata magana a kusa ta k'ara had'a su, sai dai ga mamakinta bai ko kalleta ba wata 'yar guntuwar sannuki da aiki' kawai yace sannan ya jawo kujera d'aya ya zauna ya fara k'ok'arin d'aukan plate.

"Aunty deelah, ga spoon d'ina nan baki saka ba."

Muryar Iman ta katse ta sanda ta fito sanye cikin uniform d'inta, saboda haka bata amsa masa ba ta ajiye cokalin Iman daga cikin na hannunta sannan ta koma kicin, sanda ta kawo plate d'in Daddy ta k'ara juyawa ne muryarsa ta katse ta.

"Uhm, Fadeelah..."

Zuciyarta ta buga da nauyi, ya Allah! wai ta manta ne cewa ya iya fad'ar sunanta haka? bata juyo ba yace.

"In akwai tea bag na lemon ki taho min dashi dan Allah."

"Baza'a rasa ba kam, ki duba cupboard d'in can gefe daga sama."

Mami ta sake katse amsawarta sanda ta k'araso ta ajiye k'arin wani flask na ruwan zafi, Iman ta juyar da kai game da kokarin tab'e dogon hancinta.

"Mami k'amshin man suya kike yi da yawa."

Bata san me Mamin tace ba, amma tana jiyo dariyarsu daga kitchen d'in har da Al'ameen, wannan dariyar tasa da ada take saka ta nishadi kamar me.

K'arfe bakwai dai-dai sanda kowa ya fito aka zauna cin abincin, Al'ameen yana ta hirarsa da dariya musamman shi da Faruq wanda ke ta bashi labarin abubuwa da ya sani yanzu a Nigeria, har Zahra itama ta shiga hirar tana gaya masa cewa ita kanta yanzu da za'a koma America to banda ita, Sai dai yadda ka san Allah bai halicci Fadeelah dake zaune a tsallaken kujerarsa ba, haka bai ko kalle ta ba, balle yayi mata magana.

Wanda kuma saboda son zuciya, sai? rashin kulatan yasa taji ba dad'i kad'an, son zuciya mana! in ba son zuciya ba ta manta abinda tayi ne? ta manta abinda tayi shekara guda data wuce? ta manta abinda tayi masa a tsakiyar makarantarsu?

Fadeelah ki tsaya ki saurare ni dan Allah, I want to talk to you, kin hana ni ganinki tsawon lokaci... kin san yadda nake ji kuwa?

Babu maganar data rage tsakaninmu, na gaya maka kayi hakuri ba zai yiwu ba.

Komai ya riga ya yiwu Fadeelah, saboda na riga na fara sonki kuma na san ke ma kina sona, saboda haka ki bani damar da zan nuna miki duk wad'annan dalilan naki na shirme ne basu isa su tsaida mu ba.

Ta rufe locker data d'ebo litattafanta sannan ta kalle shi, yana tsaye dab! da ita yadda litattafan ne kawai suka yiwa jikinsa da nata katanga, sai ta matsa baya kad'an.

Ni a wajena babu shirme a cikinsu Al'ameen, in kana tunanin kwakwalwata tana da matsala ne shi yasa ka fad'i hakan...

Ya katseta ta cikin d'imbin hayaniyar d'aliban dake wucewa a bayansu.

Kin san ba haka nake nufi ba Fadeelah, abu mai muhimmanci anan shine muna son junanmu, me yasa zamu wahalar da kanmu...

Ban fad'a maka ina sonka ba Al'ameen.

Da na san bakya sona babu abinda zai sa in damu kaina tsawon lokacin nan, kuma har na biyo ki nan...

Fargabarta d'aya a lokacin kar su Melissa su k'araso su gansu tare, don tunda ta yanke duk wata alak'arta dashi bata son k'arin wasu mutane a rayuwarta su san dashi.

Bana sonka Al'ameen, idan baka yarda da abinda na fad'a a baya ba, ka gayawa zuciyarka wannan ka fita daga rayuwata.

Maganar ta dake shi, amma sai yayi murmushi kad'an sannan yace.

Kinyi kokari, kin fad'i abinda ni ba zan tab'a iyawa ba, duk don ki cutar da kanki...

Haushi ya fara kamata, me yasa ne wai ba zai fahimce ta ba? ta d'ago da idonta ta kalle shi.

Hanyar lafiya nake kokarin nemowa kaina Al'ameen, kaine yanzu kake kokarin cutar dani ta hanyar da zaka amfani kanka kai kad'ai.

Kamar yaya?

Zuciyarka ta gaya maka tana sona, saboda haka kana k'okarin bata abinda kake so ne kawai ba tare da tunanin halin da ni zan shiga ba.

Na gaya miki...

Baka gaya min komai ba Al'ameen sai son zuciyarka kuma na fahimce ka sarai saboda haka nima ka fahimce ni ka fita daga rayuwata, na fad'a maka bana sonka kuma bana sonka a cikin rayuwata.

Tayi maganar ne da k'arfi cikin hasala kuma da harshen turanci, saboda haka mafi yawanci d'aliban dake baya da kuma gefensu suka juyo suka kalle su sannan wasu suka fara dariya, wannan dariyar ita ta keta zuciyar Al'ameen gutsi-gutsi, ransa ya b'aci, yaji ya muzanta a tsakiyar yaran da kowannensu bai kai sa'an k'aninsa mai bi masa ba, da ace yana dashi d'in kenan, sannan wata irin kunyar kansa ta kamashi a gaban 'yar k'aramar Fadeelan da shashashar zuciyarsa ta jawo masa raini a wajenta.

Abinda ta fad'a a gaba shi yayi sanadin guntule alak'arsu tun daga wancan lokacin.

Idonta na kallon cikin nasa tace.

Wallahi bana sonka Al'ameen, kuma bana tunanin zan tab'a sonka!

***

"Ranar ashirin ga watan september a shekaru biyar da suka wuce kamfaninku yasa hannu akan yarjejeniyar had'in kai tsakaninku da kamfanin Dibbons P.C dake America a birnin Washington. Daga cikin k'aidojin yarjejeniyar akwai dokar data had'a da cewar zaku dinga turo 40% na ribarku a kowacce shekara.

A shekaru biyun farko da suka biyo baya kun aika da ribar, amma daga nan kowacce shekara sai ku kawo uziri na matsalolin da kuke fuskanta da suke hana ku samun wata kwakkwarar riba, don haka a yanzu kamfanin ya turo mu, mu ma'aikatansa da kuma wasu daga cikin lauyoyin kamfanin don mu tabbatar da dukkanin hujjojin da kuke bayarwa kuma muga komai da idon mu."

Mark Bowden, d'aya daga cikin ma'aikatan da Al'ameen yazo yiwa kamfaninsu aiki ya fad'a yana kallon jerin mutanen d'aya kamfanin da suka zo bincike akansu k'asar Nigeria.?A yanzu farkon fara aikinsa dole ne ya rik'e matsayin Solicitor (lauya mai bincike a waje) kafin ya kai matsayin Barrister da zai dinga aiki tare da organization kawai, kamar yadda tsarin ma'aikatarsu yake.

Fatansa ma shine ya had'a biyu, ya rik'e muk'amin da ba kowa ke iya rikewa ba wato matsayin Solicitor da kuma Barrister kamar wani kwararren lauyan daya gani abokin kamal, duk da b'angaren da yake da nasa yasha banban amma yana fatan shima ya iya kawo hakan cikin aikinsa.

Matashi ne kamar shi, amma yana da wani irin k'ok'ari da hazak'a da yawan ma'aikatu irin nasu na lauyoyi suka san dashi, a d'an iya sanin da yayi masa daga nesa zai iya cewa shine role model d'insa a yanzu, ya yardarwa kansa cewa yana son zama irin ADAM STEVE a aikinsa, don shi d'in daban ne a cikin lauyoyi masu irin matakinsa.

A lokacin wata mace daga cikin mutanen d'aya kamfanin ta mik'e don yin bayanin dake cikin file d'in hannunta, ya kalli mayafin data yafa, irin kalarsa Fadeelah ta d'aura a kanta yau sak! tayi wani d'auri mai kyau yana reto a gefe d'aya.

Yaja tsaki a k'asan numfashinsa, shi ya san har yanzu bai yarda da zuciyarsa akanta ba, shi yasa tun farko baiyi niyyar sauka a gidan ba sanda aka had'a har da sunansa a masu tafiyar, amma zuwan Daddy ya tsaya akan cewar babu hotel d'in da zaije ya sauka alhali suna gari d'aya.

Fatansa d'aya ne a yanzu, kar yawan ganinta a kullum yasa alkawarin daya d'aukowa mahaifiyarsa ya kwance, don kamar yadda Fadeelah ta fad'a masa a baya ne, haka itama ta biya masa kuma tasa ya haddace cewar...

Abinda yake tunani tsakaninsu ba zai tab'a faruwa ba!

Saboda haka a yanzu yana yin komai ne bisa tsarin da ta kafa masa tun lokacin da taji Daddy ya kafe sai a gidansu zai sauka, yana bin duk maganganunta d'aya bayan d'aya.

Matsalar shine... bai tabbatar in hakan zai d'ore ba.

***

"Gobe zamu je sayayya dasu Sahla." Zahra ta fad'a da yamma tana tsaye a gaban mudubi tana taje gashinta."

"Me zaku siyo?" Iman ta tambaya daga k'asan gado inda ta baje litattafanta tana homework.

"Kayan da zamu yi decoration na class party mana, kin san ni aka nad'a caretaker."

Iman ta tab'e bakinta.

Dama ai in kina musu wannan iyayin naki dole ne a baki.

"Me kika ce?" Ta tambaya tana kallonta ta cikin mudubin.

"Cewa nayi ke ya kamata dama a bawa."

Sai tayi murmushi sannan ta cigaba da taje gashinta.

"Dama duk me suka sani sauran 'yan class d'in, ke dai bari ai za'ayi decoration d'in da ba'a taba yin irinsa ba a..."

Duk hirar da suke hankalin Fadeelah baya kansu, tunda ta idar da sallar la'asar ta nemi guri ta kwanta don ranar bata da lectures ko daya, sai dai baccin da take ganin kamar tana jinsa yak'i zuwa ko kad'an, saboda haka ta lalubo takardun lesson d'inta da Adam ta shiga bitar kowacce question d'aya data riga ta haddace ta.

A jikin wata tambaya guda d'aya idonta ya gano wasu kalmomi da suka sa kwakwalwarta tunani.

Da sauri ta mik'e zaune tana k'ara kallon rubutun kafin ta d'ago ta kalli Zahra.

"A ina mukullin store yake?"

"Yana jikin k'ofar d'azu na rufe." Ta bata amsa tana tand'e bakinta da take sawa janbaki.

"Yawwa Aunty deelah nima zan duba wani abu da nake tunanin na saka a cikin kayanki muje tare."

Iman ta fad'a sanda ta biyo bayanta ta nufi hanyar k'ofa.

Cikin k'aton kwalinta na store d'in tayi ta bincikawa har sai da ta d'auko tsohuwar jakarta ta makaranta da take amfani da ita a America. Hannunta na rawa ta zuge wani d'an k'aramin zip a gefe ta zaro wata siririyar takarda, takardar da tun daga ranar data ajiyeta bata k'ara tunawa da ita ba sai yau.

Ta warware ta da sauri sanda tsararren rubutun jiki kamar an buga shi ya baiyana.

Ya jikin naki?.

Aka rubuta daga tsakiyar paper sai daga can gefe kuma.

Mr. Hawkin's yana nemanki.

A hankali ta kara ta da rubutun Adam na paper lesson d'insu... kamar an tsaga kara, iri d'aya sak!

Kenan Adam ne ya rubuto mata paper a lokacin? a ranar data koma makaranta bayan rashin lafiyar da tayi? ya akayi ya san bata da lafiya? tun a lokacin ya san matsalarta kenan? Shi yasa ya tambayeta tun sanda zasu fara lesson d'in nan? shi yasa ya nemi jotarta don ya nuna mata ya san me take ciki?

Ta rufe idonta a hankali tana tunanin wane irin mutum ne shi daya iya mu'amala haka? waye zaiyi ta binta a hakali ta laluma haka?

"Aunty Deelah Id card d'in waye wannan?"

Muryar Iman ta fad'a a kusa da ita, ta bud'e idonta a hankali sannan ta karbi id card d'in da take nuno mata.

WASHINGTON STATE BAR
1111 East Main street, Suite 819
VA 2356-4318

Barrister Adam Steve
Status: Active
ID Number: 54217
Issued: 01/08

A gefen duk wannan bayanin, Hoton Adam ne cikin wata bak'ar suit, gashinsa da kullum yake a barbaje yanzu a kwance yake luf! cikin wani hadadden style, sannan yana da wani kwantaccen saje daya had'u ya zagaye da gashin baki wanda ya k'arawa kamaninsa mutukar kyau ba kamar yadda ta sanshi a makaranta ba, abu d'aya daya tabbatar mata da cewar Adam d'in data sani ne a hoton shine wad'annan lumsassun idanun nasa!

Bakinta ya furta sunan da kwakwalwarta ta kasa fahimta cike da rud'ani.

BARRISTER ADAM STEVE?!

Adam lauya ne?!

***
_!!!_

_Labarin dai yana ta warware wa!_

_Muna ta gangarawa!_

_Mun kusa kaiwa inda komai zai kwance gabad'aya!_=??


BAYAN NA MUTU!

?AYSHA SHAFI'EE

14

(&_&)

Ayyiryiryiriiiiii! Ayyiryiryiriiiiii!

Wata dattijuwar mata rangad'a zankad'ed'iyar gud'ar data cika kaftanin d'akin, duk kuwa da d'imbin hayaniyar matan da suka cika falon suna ta d'aga wasu tsantsara-tsantsaran kayayyaki daga cikin jerin akwatunan dake gabansu.

"Wallahi kaya sunyi mutuk'ar kyau masha Allah, Allah ya sanya alkhari nawa suka bayar kuma kud'in d'inki da cefanen?"

Wata k'awar Haj. Halima matar Baba habibu ta tambaye ta sanda suke duba akwatin kayan shafe-shafe.

"Dubu d'ari cif! ai wallahi munga kokarinsu, don da farko dubu talatin muka tanada tukuici sai da aka cika ashirin."

"Sun cancanta gaskiya, a sabon ma'aikaci ai yaron yayi bajinta ba kad'an ba, akwati goma fa."

"Goma kam! ni yanzu jigilar na Saifudden kawai nake hangowa, ba had'a lefen ba taronsa kamar wani bikin ne."

"Haba hajiya ku da abin gabad'aya na cikin gida ne, ku zaku had'a abinku fa ku karb'i kayanku."

"Ke dai bari, abinda kake rainawa shi yake zuwa ya baka tsoro."

Daga gefensu haj. Saddika matar Baba sani tace.

"Ai mu ya kamata mu fad'i haka ma ba ke ba, tunda a lokacin komawa gefe zaki yi ki bar mana hidimar."

Da dariyarta ta amsa mata.

"Ke da har yanzu baki fad'i matsayarki ba, ni dai ina gaya miki ne gwara ki zab'a tun yanzu kar abu yazo ya cakud'e miki ki rasa inda zaki yi.."

"Babu zancen cakud'ewa don zan iya, kowanne b'angare ina nan, ni ta amarya ce kuma ta ango."

Suka yi dariya gabad'aya ta cikin surutun dake tashi a d'akin, ko'ina ka duba mutane ne dai ke ta d'aga kaya daga wannan akwati zuwa wannan, yayin da daga can kitchen su Mami ne da Aunty Hadiza, matar kawu Isma'il da kuma wasu daga cikin 'yan uwansu makusanta ke hidimar raba irin snacks d'in da aka sallami dangin ango dasu ga mutanena cikin gidan.

A d'aki na k'arashe daga benen gidan, Rahma ta bud'e k'ofar band'akin da k'arfinta.

"Wallahi na dad'e banga 'yar iskar amarya irinki ba, kina nan kina waya ana k'asa ana bidirin kawo kayanki."

Aseeyah ta d'ago daga wayar da take yi ta kalle ta.

"Zuwa zanyi in taya su ko me?"

"Ai abinda ya rage baki yi ba kenan, ko ni duk rashin kunyata barin gidan zanyi wallahi."

"To sai gani ni kuma na dame ki a rashin kunyar."

"Ai baki burge ni ba, da kin sani da suka shigo zuwa zaki yi ki gaishe su, ki tsugunna kiyi godiya in sun tashi tafiya kuma ki taka musu zuwa mota."

Fadeelah dake gefe cikin kwalliyarta kamar kowa a gidan, tayi murmushi kawai tana jinsu hannunta na kan wayarta da take browsing wani assignment na makaranta.

"Kin san Allah in su Mama suka san kina gidan nan sai ranki ya b'aci."

"Toh ta yaya zasu sani, sai dai in ke ko munafakan yaran nan ne zasu gaya musu..."

Ai kuwa kafin ta rufe baki, su Sahla Sameera da Zahra suka banko cikin d'akin, da sauri Rahma ta rufe k'ofar, a yanayin kwalliyarsu wani zai zata ranar ake d'aurin auren.

"Mutane 'yan naci ne wallahi, sun k'i su matsa ma muga komai." cewar Sahla.

"Ni wallahi 'yan k'auyen nan da Hajiya ta gaiyato tsoro nake kar a samu masu sata, dan yaya Rahma baki ga yadda suke kallon kayan nan ba wallahi."

"Kowanne fa sai sun kalle shi sau uku-uku."

Zahra ta karb'ewa Sameerah.

"Dama a yanzu manya ya kamata su fara gani, ku da za'a bar abin a gidan ma ai har sai kun gaji da gani in dai kaya ne."

"Mun d'ebi na d'iba ba kuma." inji Sameerah.

"Eh dole, tunda ku za'a aura me zai hana ku d'iba.

Fatima ta shigo d'akin a lokacin hannunta rik'e da tray d'in snacks.

"Kun san me yake faruwa kuwa? Mami Hauwa ce fa tazo yanzun nan."

"Wacce?"

Rahma da Sameera suka had'a baki wajen tambaya.

"Wacce kuka sani in ba ta Kaduna ba? wallahi yanzu direba ya sauke ta gata can a falo ana gaisawa."

"Kai! wallahi Aseeya kin ciri tuta, kawo lefe ba biki ba matar nan ta tako k'afa tun daga kaduna tazo? fito-fito kiji sabon labari."

Fadeelah ta amsa sanda ta nufi inda Fatima ta dire tray d'in nan, ta d'auki samosa guda d'aya sanda su Sameera suka nufi k'ofar band'akin suna fad'in.

"Dama wai tana nan... Yaya Aseeya Mami cewa tayi fa kin fita... in gaya miki akwati set goma... kinga wani lace a cikin kayan kuwa..."

Fatima tace.

"Ku kwantar da hankalinku mana, in dai kaya ne sai kun ture, wani ma na hanya."

"Kayan wa kuma?"

Fadeelah ta tambaya.

"Wai baki san yaya Saifudden ne zai auri Rahma ba? har fa ana shirin kawo kud'i."

Mamaki ya kama Fadeelah, ashe shi yasa kwanaki da zasu je gidan Baba habibun tak'i binsu, da kuma sanda ta ganshi a kitchen ya tambaye ta Rahman, ita fa har yanzu bata iya maida hankali kan sha'aninsu, sai dai ta saurari iya abinda ta tsinta kawai don Mami ma yanzu ta rage hira da ita samun su Aunty Hadiza da Aunty iyami a kusa.

Ta jinjina kai a hankali, mamaki take yadda hali biyu mabanbanta suka had'u, shi miskili mara magana Rahma kuma wayayyiyar mace mai surutu da rawar kai, lallai wani had'in sai Allah.

"Kema Deelah kamata yayi kawai a had'a ki da Rahman ki fito mana da ango musha biki... ko ranar nan wani abokin Yaya Yusuf sai da yayi min zancenki."

Cak! tunaninta ya tsaya, don yau ne rana ta farko da wani mahaluki ya d'auko kalmar aure ya danganta ta da ita, saboda damuwar kowa a kanta na rashin lafiyarta ne da son jawo ta cikinsu, hatta Mami kuwa... tunaninta akanta kullum na samun lafiyarta ne kawai, sai taji kamar ta zama mutum kamar kowa ne da Fatiman ta fad'i hakan.

Duk da cewa kuwa har ga Allah bata son d'orar da rayuwarta a haka, bata son saka kanta a wata sabuwar rayuwa da guntulallen asalinta iya na yanzu, tafi son ace itama ta koma cikin 'yanuwanta kamar yadda su Mami suke yanzu, tana son samun irin wannan farin cikin da annushuwar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login