Showing 90001 words to 93000 words out of 153964 words

Chapter 31 - BAYAN NA MUTU Book Original By Aisha Shafii.doc

30 Aug 2025

3805

da dad'i musamman k'azafi irin wannan na kisa. Kotu ta gode sosai da wannan gudunmawar taki."

Ya juya ya kalli Adam.

"Your witness..."

Ga mamakin kowa sai ya mik'e a hankali ya karaso gaban Habiban da zuciyarta ke dukan casa'in- casa'in kamar ta na shirin fasowa daga kirjin nata ne a kowanne lokaci.

"Habiba.."

Yadda ya kira sunanta da wannan malalaciyar muryar tasa yasa wani abu ya tsarga mata har k'asa, taji tana k'okarin sakin fitsari a tsayen da take.

"A yadda rahoton yake babu wanda ya san Hajiya ta rasu har sai da aka kaita asibiti, ta yaya ke daga jin hayaniya kika lek'o akace miki Hajiya ce ta rasu? Sannan waye ya gaya miki?"

Habiba ta tsure ta rasa me zata ce, don ita har ga Allah ta manta ma ta fad'i hakan, to zancen da ba gaskiya ba.

Kotun tayi shiru, kowa ya tsira mata ido jiran amsa, ganin haka yasa kutama ya mik'e da sauri.

"K'orafi ya mai shari'a, Lauya na k'okarin tursasa...

"K'orafi bai karb'u ba."

Alkali ya katse shi tun kafin ma ya k'arasa, sai ya koma ya zauna zuciyarsa cike da haushi. Adam ya lumshe idonsa akan Habiba sannan ya sake cewa.

"Ya akayi kika san Hajiya har ta riga ta rasu a lokacin bayan ba wanda ya fad'a miki ma dalilin mutuwar, sannan waya ya shaida miki cewa ta rasun?"

Habiba bata da mafita sai wata k'aryar saboda haka ta hadiye wani tarin yawu a bakinta sannan tace.

"Ba zan iya tuna waye ya gaya min ba, sannan tunda aka fita da ita kowa ya gane cewa guba aka bata tunda kumfa nata fita ta bakinta."

Ga mamakinta sai ya gyad'a kansa kawai sannan yace.

"Mun gode Habiba."

Ya juya ga Alkali.

"Bani da wata sauran tambaya ya mai shari'ah."

Da haka ya koma ya zauna, Habiba ta sauke wata ajiyar zuciya mai nauyi tana godewa wayonta, bata san cewa rami ta hak'awa kanta ba, don Adam ya riga ya gama abinda zaiyi ya d'aure ta da harshenta ba tare da ta sani ba, don yadda shaid'an ke shagaltar da bawa ga ayyukan zunubi ba tare daya farga ba haka Adam ke d'aure mai laifi da harshensa a kotu ba tare daya fahimta ba.

Shaida ta gaba da kutama ya kira Kawu Yahya ne, kamar sauran shima yazo ya gwamutsa k'arya da gaskiyarsa irin yadda suka shirya hakan tun a gida.

"Your witness.." Kutama ya fad'a sanda ya gama dashi amma sai Adam ya girgiza kansa alamun bashi da wata tambayar da zaiyi masa.

Ba sauran jama'ar kotun ba, hatta Fadeelah sai da ta d'ago ta kalle shi a lokacin, idanunta na haska tsantsar mamaki na rashin sanin inda ya dosa, ko kuma ma yana da tabbas cewa ya kama hanyar dosar wani wajen.

"Kotu ta d'age sauraren k'ara nan da ranar sha takwas ga wata, wato kwana uku masu zuwa, sannan kotu ta bada umarni a rik'e Habiba har zuwa sanda shariah zata daidaita."

Alk'ali Bashir Ali, ya shaida hakan sanda zaman kotun yazo k'arshe. Da wani irin sauri Kutama ya mik'e.

"Ya mai girma mai shariah, Habiba bata da laifi...."

"Baka da hurumin k'alubalantar abinda kotu ta yanke Barrister, sannan kuma baka da hurumin k'alubalantar laifin wani!"

Da wannan hukuncin wani mai zak'in murya ya kawo k'arshen zaman ta hanyar d'aga muryarsa yace.

"Koooootuuuuu!"

***

"Me kake yi ne haka Adam? Ka san cewa su Sadiya duk da suka tsaya a wajen nan k'arya suke fad'a, don me yasa su baka k'alubalance su ba?"

Kawu Ibrahim ya tambayi Adam a lokacin da ya same shi daga can bayan harabar wajen bayan yayi iya k'okarinsa wajen gujewa 'yan jarida da kuma tarin mutanen dake tururuwar jin ta bakinsa game da shari'ar. A hankali ya sauke muryarsa k'asa sannan yace.

"Baba, na san duk abinda suka fad'a k'arya ne, amma da ace na tashi na k'alubalance su, da duk cikinsu babu wanda zai bar kotun nan a yau, Habiba ita kad'ai nake hari a lamarin nan, shi yasa ita kad'ai na k'ulle!"

***

Baku tambayi ina Mairo ba, Mairon Bintu, Mairon Sadiq! Ya akayi har aka fara shari'ar nan babu labarinta?

Waye yarda cewa Adam ya kware a aikinsa???=??=??=??

Ina lawyers d'ina? Ya kuga zaman mu na farko?

Sai mun had'u a zama na gaba!


BAYAN NA MUTU!

?AYSHA SHAFI'EE

(&_&)

Mairo ta bud'e idanunta a karo na barkatai, don bata san iya adadin sau nawa tasha bud'e su tana komawa cikin mayen data kasance a cikinsa ba.

Cikin taimakon ubangiji wannan karon sai bata ji irin jirin dake sake maida ita duniyar data fito ba saboda haka ganinta ya tsaya akan wasu Nurses guda biyu dake tsaye a gaban gadon dake fuskantar nata, tun a baya kwakwalwarta???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~? ta fahimci a asibiti take, amma bata yi tunanin cewa har a yanzun zata farka ta ganta a cikinsa ba, duk da cewa kuwa ta san abinda ya sameta ya cancanci hakan.

Bugawar zuciya, ba ciwo ne da rana d'aya za'a sallameta ta koma gida ba, amma tsawon kwanaki nawa kenan take nan? Idonta ya juya kan agogon d'akin, k'arfe hud'u da 'yan mituna ya nuna, matsalar shine bata san wace k'arfe hud'un ba ta dare ce ko kuma ta rana? Amma a take kwakwalwarta ta shaida mata cewa idan har k'arfe hud'un dare ne wad'annan Nurses d'in da take gani a tsaye ba lallai ne a same su ba.

Saboda haka ta yunk'ura ta mik'e zaune, tana jin kowacce gab'a ta jikinta tayi mutuk'ar nauyi wanda hakan ke nuna cewa lallai ne ta dad'e a kwance.

"Sister Hawwa, 185 ta farka."

Muryar d'aya daga cikin Nurses ta fad'a sanda ta juyo tana kallon gadon nata dake d'auke da wannan number. A lokaci d'aya suka yo kanta gabad'aya, wadda aka kira da Hawwa ta d'ora bayan hannunta a k'asan wuyanta sannan tace.

"Sannu ya jikin naki?"

"Da alamun sauki, tunda a file dinta babu high blood sugar."

D'ayar ta fad'a, Mairo kallonsu kawai take yi ba tare da ta fahimci me suke cewa ba, don hankalinta yana kan wayar dake hannun wadda aka kira da Hawwa d'in, kamar kuwa ta karanci zuciyarta sai ta ajiye kayan hannunta har da wayar a gefenta ta juya ta shiga tab'a wani monitor dake gefen gadon nata.

Mairo bata jira komai ba tasa hannunta ta d'auki wayar ta danna ta, hasken daya kawo a screen ya nuna mata lokaci da kuma kwanan wata na ranar.

Laraba, sha biyar ga wata.

Kwakwalwarta ta shaida mata hakan a daburce, abin ya d'aure mata kai, taji kamar a cikin mafarki take, don gani tayi kamar jiya ne ta fad'i a band'aki Sadiq ya d'auko ta ya kawo ta asibitin nan cikin mawuyacin hali numfashinta na kakkatsewa... Bayan hakan abinda zata iya tunawa kawai shine an shigar da ita CCU (coronary care unit.) Likitoci da yawa suka taru akanta daga nan akayi mata wata allura da ta janye ta daga cikin tunaninta.

Amma duk da haka yaya za'ace har anyi kwana uku da hakan?

"Kawo wannan mu gani, hannunki akwai allura." D'ayar Nurse d'in ta fada tana kokarin karb'ar wayar hannun nata.

Sai dai ga mamakinta tana karb'ar wayar Mairo tasa d'aya hannunta ta cisge allurar drip d'in dake shiga jikinta, sannan tasa d'ayan kuma ta cisge wayoyin monitor da aka manna a hannunta.

"Ya salam.. Meye haka? Ina zaki?" Ta tambaya da tsananin mamaki ganinta diro daga kan gadon.

Bata ko saurare ta ba, idonta ya shiga bin d'akin da kallo, hijabi ko mayafinta take nema amma sai ta tuna ai daga cikin toilet d'in nan da ta shiga alwala haka Sadiq ya d'auko ta ba mayafi.

"Mijina yana nan?" Ta tambaya tana kallonsu su duka biyun.

"Yana nan, yazo harda sauran 'yanuwanki ma, yanzu ki koma ki zauna zamu kira miki su."

Sai tasa duka hannayenta biyu ta kwance d'ankwalinta ta maida shi yanayin yafe.

"Ina zaki je? Kinga ki dawo ki zau..."

D'aya daga cikinsu tayi kokarin rik'eta amma ta fincike hannunta da karfi ta nufi k'ofa. Ta san sun biyo ta amna hakan bai dame ta ba ta kama hanyar fita waje da iya saurin da zata iya, don sunfi shekara biyar da yin rijista da asibitin, ta riga ta san kowanne lungu da sak'o na cikinsa.

"Sister Rabi'a dan Allah taimaka ki tsaida ita." Muryar Nurse d'aya ta fad'a daga bayanta, amma kafin Nurse d'in dake gabanta ta fahimci me suke nufi ta wuce ta da sauri ta nufi hanyar matattakala ta sauka k'asa.

Benen na kallon waiting area don haka tsaf idanunta suka gane mata wanda take nema, Sadiq na tsaye jikin ginin receiptionist d'in wajen yana magana da ita, hannunsa na hagu d'auke da Muhammad.

Bata jira komai ba ta nufi wajen nasa sanda Nurses d'in dake biye da ita su kai ga cimmata, zaune a waiting area, mahaifiyar Sadiq ce da k'annesa mata biyu da kuma wasu daga cikin danginsu duk mata, sai 'yarta Afra dake ta 'yan wasanninta. Kusan awarsu d'aya kenan a wajen saboda tun bayan zuwansu ranar da aka kwantar da ita, aka ce ba wanda zai iya ganinta sai zuwa yau daya kama kwanaki uku.

Mairo duk bata lura dasu ba, don idanu dama hankalinta na kan Sadiq da ya juya bayansa don haka bai ga tahowarta ba, sai Recieptionist d'ince mai suna Amina ta zare idonta cike da mamaki tana kallonta.

"Ai gata nan ma ta fito, har an sallame ta ne?"

A lokaci d'aya ya juyo da tsantar mamaki daidai sanda ta k'araso itama ta shige jikinsa saboda saurin da ta taho dashi.

"Maryam yaushe kika farka?"

"Sadiq mu tafi gida."

Dukkkansu suka yi maganar a tare, kuma lokaci guda. Hakan yasa ya sake saurin tararta.

"Me kika ce?"

"Ikara zaka kaini." Ta fad'a tana kallonsa da idanunta wanda suka kad'a suka yi jawur alamun tana cikin ciwo har a lokacin.

Sadiq yaji duk wani tashin hankalin duniya ya dira cikin kansa a lokaci d'aya sannan mamaki ya k'ulle bakinsa.

"Yallab'ai yi hakuri wallahi fitowa tayi..."

D'aya daga cikin wasu Nurses guda uku da suka iso ta fad'a lokacin da suke kokarin rik'e hannunta, amma ga mamakinsa Mairo bata ko juya ba ta fizge hannunta da wani irin k'arfi da bai tab'a sanin tana dashi ba, a lokacin kuma Muhammad ya kwallara kuka mai d'agawa na alamun gane mahaifiyarsa da yayi, ya shiga mik'o 'yan hannayensa gare ta, amma Mairo bata ko kalle shi ba, idanunta a tsaye ta sake cewa.

"Sadiq gida zaka kai ni." Muryarta na d'auke da wani irin kaushi mai cike da ciwo.

"Subhanallahi, Sadiq me yake faruwa haka?"

Yayar mamansa ta fad'a sanda dukkaninsu suka taso daga waiting area d'in, k'anwarsa Zakkiya ta k'araso da sauri ta karbi Muhd d'in dake ta kuka a hannunsa ta shiga jijjiga shi, amma zillewa kawai yake yana mik'a hannu wajen uwar da yayi kewarta tsawon kwanaki, uwar da bata ma san yanayi ba, don bata kallon kowa a wajen, idonta na kan Sadiq kawai da ta shige cikin jikinsa kuma ta rik'o da kwalar rigarsa har sama, rik'o irin na alamun rok'o.

"Har ta farka? An sallame ta ne?"

Da yawansu suka had'a baki wajen tambaya.

"Wallahi Hajiya ba'a sallame ta ba, farkawa kawai tayi ta fito, kuma tak'i bari a maida ita."

Nurse d'in nan ta fada.

"Sister Nafisa, jeki d'auko Diazepam?(allurar saka bacci.)"? Nurse Hawwa ta bawa d'ayar umarni.

"Sadiq gida nake son zuwa.." Mairo ta k'ara maimatawa tana jijjga shi, da alamu bata ko fahimtar abinda ke faruwa a bayanta.

"Bari inje in gayawa Dr. Haruna, ina ganin ba zamu iya rik'e ta ba.."

"Bibty gida zani...."

"Me ya same ta haka me ya faru?" Wata likita da tazo wucewa ta tambaya.

"Kana jina? Ka kaini gida..."

"STEMI patient ce kawai ta farka ta fito." Nurse Hawwa ta bata amsa.

"Bibty dan Allah..."

Kwakwalwar Sadiq ta hargitse a lokaci d'aya don ya rasa me zai d'auka ya fara aika mata, magiyar Maryam, kukan Mahammad, hayaniyar Nurse d'in, ko kuma tambayoyin dake ta fitowa daga bakin 'yanuwansa... Yaji ya zama tamkar wani mutum-mutumi ba abinda yake iya fahimta sai yadda hannayen Mairo ke jijjiga kwalar rigarsa da dukkan k'arfin da zata iya.

Bai farga da komai ba, sai sanda wannan Nurses d'in ta dawo d'auke da allurar da aka aiketa, bai san amfaninta ba amma ya tabbata idan ta shiga jikin Mairo zata sa ta k'ara fita daga haiyacinta ne, saboda haka yayi saurin had'eta da cikin jikinsa bakid'aya sannan ya juyar da ita gefe.

Sai hayaniyar ta ragu kowa a wajen ya tsaya kallonsa da mamaki.

"Alhaji, matarka fa bata gama warkewa ba, ba sallamarta akayi ba."

Mai rik'e da allurar ta gaza jinkirin b'oye mamakinta.

"Ba sai kun sallame mu ba Nurse, a barta haka, sauran da kuka yi ma ya isa."

"Ai ba zancen isa bane Yallab'ai, wannan patient dinmu ce a yanzu, kuma ba zai yiwu a bari ka fita da ita ba tare da sallama ba."

"Zamu tafi yanzu?" Muryar Mairo data sake magana, ta nunawa kowa a wajen cewa bata cikin hankalinta, don duk da shorun da akayi baisa ta juyo ta kalli kowa ba.

"Sadiq wai me yake? faru ne? Me ya same ku?duka biyun?"

A yanzu mahaifiyarsa ce ta fad'i hakan, ganin har yanzu sun gaza fahimtar abinda ke faruwa.

"Mama gida zan take son zuwa."

Kusan a rikici yake don haka baiyi shawara da tunaninsa ba ya fad'i abinda ya rufe su a cikinsa tsawon shekaru.

"Wane gidan, naga duk gamu mun taho."

Ya girgiza kansa yana k'ara kallonta.

"Gida can wajen 'yanuwanta nake nufi."

"Yan'uwa? Yaushe Maryam d'in ta samu 'yanuwa bamu da labari?"

"Pleaseee Bibty..."

"Ba'a dad'e ba, kuma dalilin ciwon nata kenan, shi yasa ta rikice take son tafiya."

"Don darajar ma'aikin Allah Sadiq..." Muryarta rawa take a yanzu, somi-somin kuka hakan ya d'arsa tausayinta a zuciyar duk wanda ke tsaye banda Nurses d'in nan, banda Nurses d'in nan dake hango query da zasu iua amsa in har basu maoda ita gadonta ba.

Daga inda take tsaye, mahaifiyarsa ta tsaya ta kalle ta, a shekarun zamanta kaf da Maryam ba zata iya tuna rana d'aya da ta b'ata mata rai da gangan ba, ita d'in mai tsananin biyayya ce ga mijinta da kuma su, har wasu a danginta na cewa tunda bata da 'yanuwa su ta same su ai dole ne ta rik'e su, saboda haka yadda take tsaye a yanzu ba tare da ta kalli d'aya daga cikinsu ba, kuma ta shige jikin Sadiq d'in da a gaban idonta ko hannunta bata bari ya tab'a, ya tabbatar mata cewar bata cikin haiyacin da zata fahimci komai sab'anin abinda take so.

"Abubakar ka tabbata ba matsala?"

A rayuwarsa kaf! Sadiq ya san sau biyu ne ta taba kiransa da Abubakar, a ranar da ta kira shi a waya yana makaranta ta shaida masa zancen rasuwar mahaifinsa, sai kuma ranar da yaje mata da maganar auren Mairon, saboda haka ya tabbatar da ta fahimci halin da Mairon ke ciki, ta fahimci cewa idan aka maida ita cikin asibitin nan tabbas su dukkansu sun zalunceta.

"Wallahi babu matsala Mama, so take yi kawai ta gansu.."

"Alhaji mu fa ya kamata mu tabbatar muku da hakan ba ku da kanku ba, don haka ku bada ita a maida ta."

Bai ko saurari Nurse d'in ba ya cigaba da kallon Mahaifiyarsa wadda ke k'ara tambayarsa sunan garin 'yanuwan nata.

"Kaje ka kaita Sadiq, amma ku tafi tare da Zakkiyya ta rik'e Muhammad, don ba'a san abinda zai faru ba... Insha Allah zuwa gobe zan turo su Umar su ga me ake ciki."

Wannan izinin na mahaifiyarsa, shi ya haddasa tafiyar da d'ayansu bai shirya mata a yau ba. Don Nurses d'in nan babu yadda suka iya suna gani likitan dake duba ta ya sallame ta da tulin magunguna, saboda yana zuwa shima? yaga halin da ake ciki yace ai dole ne ayi mata abinda take so don in ba haka ba zuciyarta zata iya sake bugawa kwatankwacin na da.

A duk abinda ake yi Mairo na rik'e da Sadiq wanda ke ta bata hak'uri da cewa zasu tafi yanzu, don duk tarin jama'ar dake kansu kaf! Shi kad'ai take gane abinda yake cewa.

Kafin a kammala komai d'aya k'anwarsa ta koma gida ta d'ebo musu 'yan kayayyakin sakawa da zasu buk'ata, kuma har a lokacin Mairo bata karbi Muhammad dake ta ihunsa ba har ya gaji yayi baccinsa a bayan Zakkiya, kowa a wajen nan ya tausaya mata don sun shaida cewa da gaske ne bata cikin haiyacinta, in ba haka ba meye zai shafe tausayin dake tsakanin uwa ga d'anta?

A waje biyu kawai suka tsaya kafin su hau kan titin express way, inda Sadiq ya tsaya ya siya musu tulin abinci sai kuma gidan mai da ya cika tankin motarsa taf.

Tunda suka d'auki hanya kuwa, idanun Mairo na kafe akan titi, bata sake cewa komai ba, kuma ko sau d'aya bata juya ta waiwayi su Muhammad dake zaune a baya ba, Shi kansa Sadiq baice da ita komai ba, don abinda ke faruwa a cikin kansa ma ya ishe shi.

Ya riga ya yarda cewa tabbas lokacin rabuwarsa da Mairo ne yazo... Ya kama hanya zai kaita inda baza ta taba dawowa gare shi ba, don ya san babu abinda zai hana ragowar asirin nan kwancewa in har tayi ido biyu da mahaifarta!

***

Akwai wani zane a hannunta irin na 'yan indiya, anyi shi da kalolin bak'i da kuma ja, duk da ba zai iya tuna yaushe a rayuwarsa ya tab'a kallon film d'in india ba, ammma yasha ganin hotunansu kuma hannunsu da irin wannan zanen na flower daya fito d'al akan farar fatarta.

Ya rufe idonsa ya sake yin baya cikin lallausar kujerar falon da yake zaune, a daren jiya baccinsa kad'an ne, don rabin daren ya shafe shi ne wajen rubuce-rubuce na fitar da yadda zaman kotun na farko ya kasance da kuma yadda zai shiryawa na biyu, sannan da yadda tsarin tasa hanyar zai cigaba da tafiya.

Bayan ya gama kuma da yaji baya jin bacci sai ya tashi kawai yayi ta sallolin nafilarsa yana rok'on Allah daya bashi sa'a a shari'ar na, sannan kamar kullum yana neman yafiyarsa kan yadda ya shafe rabin shekarun rayuwarsa yana bauta ga wani abun daban. Sai gashi a yanzu d'an baccin da yake nema kuma ya gagara, kwakwalwarsa tak'i hutun, bayan idanun Fadeelah yanzu ta bud'e wani sabon shafi kuma na tunanin hannayenta da zanen da aka yi musu.

Ya san cewa abun yayi masa kyau ne, amma kuma abu nawa ne yayi masa kyau kuma yake saurin manta shi, me yasa sai komai nata ne zai tsaya a kansa?

Motsin shigowa cikin falon yasa ya bud'e idonsa, Sadiq ne d'auke da ledoji na abincin da yaje siyo musu, yayi zaton ma Awwal ne ya fito, wanda tunda

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login