Showing 201001 words to 204000 words out of 259215 words
Chapter 68 - Kuskuren Baya Complete by Aisha Bagudu .txt
koshin lafiya bana ma tsammanin zan shige wasu wa’adi batare dana koma ga ubangijina ba dady ka taimakeni..”
Tai shiru kuka ya kwace mata “Tanwer har kullum ina tunatar dake matsayinki sannnan da halin balain da zaki shiga idan kika bari aure ya shiga tsakaninki da wannnan yaron ,aurenki dashi nakasu ne a rayuwarki, zai gurgunta miki rayuwa da mummunar qaddara, kullum kuma kina cikin tashin hankali da faduwar gaba , ina son kiyi duba da makomarsa shi fa ba kamar kowa bane sai dan fashi mai barna ,
ina hasko miki mummunar rayuwar da zakiyi idan kika aure shi karki manta ke fa kina da kyawawan halaiya yayinda shi bashi dashi ,ke mai ilimi ce shi kuma jahili ne aurensa shine zai kawo miki cikas a rayuwarki .”
“duk fa halin da yake ciki a yanzu nasani kema da duk halin da kike ciki ko zuwanki gidansa ma jiya da kikayi nasani ina jin zafi da radadin kasancewar ki dashi ban sabar miki da wahala ba amman kin jefa rayuwarki cikin mummunar rayuwa ,ban san ta fuskar da zan bullo miki ba bazan iya sabawa Kaina alkwarin dana yiwa kaina ba tanwer kiyi hakuri kawai ki bari idan Ibrahim ya dawo ki aure shi ,”
“wallahi shine yafi dacewa dake na tabbatar zai zame miki miji na gari ,zai baki kulawar fiyye da wanda kika taso ciki ,shi ba dan maye bane bare idan ya sha yazo ya dakeki, bazaki tagyaraba a hannunsa ba yana kan samun lafiya nan kusa zai dawo kuyi aure
ita gbdy ta manta da wani ibrahim a rayuwarta bama ta son ta tuna shi adnan kawai a gabanta “kayi hakuri dady ka aura ma adnan ni ka kuma mana fatan alkhairi arayuwarmu na zamo silar shiryarsa “Kiyi min biya tanwer ki daure ki samar da farinciki mai daurewa a tare dani .” ya ajiye maganar cikin wani irin yanayi ya tsura mata ido yana kallonta .
“Dady duk wani biyayyarka bazan fasa ba tunda bani da wanda yafika amman matsawar ba adnan na aura ba karka yi tsamanin zan samu farincki agidan aurena domin kuwa aurena da Ib bazai kawo farinciki a rayuwata ba a bincikena na gano mahaifinsa shine yasa akawo maka farmaki har adnan ya samu damar tafiya dani .”
“nasani nasan shine “
“tunda kasani banga amafnin rike alkwari ba ya kamata bangon alkwarinku ya ruguje yadda adnan yake mai laifi haka mahaifin Ibarahim yake baka jin tsoro nayi zuria dashi su dauko halinsa wallahi babu farincikin da zanyi dady kowa ma fa mai laifi ne inda zaa yi kwakkwarar bincike hatta shima ibarahim din mai laifi ne tunada yana biye biyen matan banza amman saboda shi mai galihu ne ka gwamaci kabashi aurena sau nawa yana kokarin keta min haddi acikin gidan nan kodan ban taba fitowa na fad’a maku ba tana kaiwa nan ta tashi da sauri ta bar gurin ta shige dakinta tana matsanancin kuka dady yayi tsai da ransa yana bin maganganunta dake dake yayi shiru yabi kofar dakinta da kallo tabbas tana dan gskiya wai ma me yasa bazan hakura na barta ta auresa ba “saboda bai dace bane da rayuwarta ai gara rayuwar zina data dan fashi agurinsa zina tsakaninka da mahalincika ne shi fa daukar bindiga ya tara rudani dayawa “?
yayi shiru yana saka maganganu acikin ranshi tsananin tausayinta ya kamashi amman bazai taba biye mata ba .duk maganrsu acikin kunne mumy sukayi shi ta mike tsam ta fito ta wuce dady ta nufi dakin tanwer cikin sanyin jiki ta kalleta tanwer ta dago kanta ta kalleta shabe shabe da hawaye bisa kuncinta “ki kwantar da hankalinki mamana ki tashi kiyi adduar inada yakinin zaki samu sausauci
saboda ina ji ajikina zaki auri adnan fatana allah yasa aurensa ya zame miki alkhairi arayuwarki ta
karasa maganar tana kuka “kiyi hakuri mumy nasan saboda ni kike kuka ko ?" inshallahu zan canza, ta girgiza mata Kai tare da riko tafin hannunta cikin nata cike da tausaya mata .”
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
KUSKUREN BAYA
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
PAID BOOK
WRITING BY
AYSHA .A BAGUDO
WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukata karanta shi ya tura 500 ta wannan account number din 1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan an tura sai a turawa wannan number+234 703 534 8686alert domin tabbatar da an tura ko wadan nan number's din 09136918331 or 08059623096 Idan Kuma vtu za'ayi sai a tura ta wannan number 09136918331 domin sauraran littafaina a tuntubi Channel dina ta Hausa bakwai.
🅿️36
……….Sai da sukayi kuka mai isarsu sannan mumy ta zare hannunta acikin na tanwer tana kokarin fita daga dakin tana goge hawaye tana tunanin yadda zata sake fuskantar mijinta da wannan matsalar , Tanwer tayi shiru zaune tana kallon bayan mumy cike da matsanancin tausayawa har mumy ta karasa ficewa daga dakin idanunta na kallon kofa yayinda
wasu hawaye masu zafi suka zubo mata tare da wani azababben ciwo kai mai tsanani .”
saukowa tayi daga kan katifa jikinta a matukar sanyaye ta zauna akan kujera kushin guda daya dake dakin hawaye na cigaba da zubo mata ,har ga allah yadda take d’aga hankalin mahaifiyarta abun baya mata dadi amman ya ta iya da qaddarar soyayyar data caki zuciyarta ta hana gangar jikinta da ruhinta sukuni? “wai me yasa bazata hakura da adnan ba ta hutawa ranta tare da dawo da farinciki da kwanciyar hankalin iyayenta ?”wadan nan tambayoyin ta dingawa zuciyarta sai dai nan take zuciyarta ta shiga hasko mata moment dinsu dashi tana kwance ajikinsa shi kuma yana shafa laulausar sumar kanta ita kuma tasa hannunta ta sakalo wuyansa ta cusa hannunta cikin tauttausan sumar kanshi dake kwance a keyarsa tana tafiya da hannunta acikin sumarsa nan take ta fara jin wasu abubuwa suna mata yawo a sansar jiki suna zaga jinin jikinta yarrrrrrrr taji gbdy tsigar jikinta
sun mike taji ina bazata iya hakura da dashi ba arayuwata ,da zata iya da tayi ko dan kwanciyar hankalin iyayenta .”
Kai tsaye mumy hanyar dakin dady ta nufa dan lokacin ya tashi a parlour ya koma dakinsa cikin tsananin zullumi da damuwa mara iyaka ,har cikin uwar dakansa ta sameshi zaune abakin gadonsa yana nazarin rayuwa da maganganun tanwer ,ta samu guri ta zauna akan kujerar dake fuskancesa sai dai kallo daya zaka mata ka fahimci ranta a bace yake idanunta sunyi jawur alamun kuka, muryarta na rawa ta soma magana “na sake dawo wa gareka a karo na sau babu adadi , na bika na baka hakuri na durkusa maka da gwiwowina na baka hakuri ,nayi kuka duk akan cikar burin tanwer kaki ka fahimceni har ta kai ga ta sameka da kanka amman still kaki “a gaskiya a halin da muke ciki yanzu yakamata kayi wani abu akai dan gara muyi hakuri mu aura mata yaron nan ko acikin satin nan ne tunda taji kuma taga zata iya rayuwa dashi a aura mata shi kawai a wuce gurin , ita shiriya fa ta allah ce ina ji ajikina zai gyaru ya zamo mutumin kirki “.
dauke idanunshi yayi akanka ya mayar wani gefe zuciyarsa na zafi da tafarfasa dan ya gaji da jin wadan nan zantukan daga bakinta ,ganin yayi shiru yaki cewa komai sai ma dauke kanshi da yayi ya tunzurata dan haka ta cigaba da magana a fusace “wallahi idan wani abu ya samu yarinyata bazan yarda ba dan ita kadai gareni kai kuwa ko yanzu ka bukaci sake haihuwa zakayi nifa?“.
Yayi tsaki yana kallonta “kar allah yasa ki yarda amman wallahi bazan yi abinda ke da ‘yarki kuke bukata dani ba ,domin shi fa wannan d’an fashin ba daina fashinsa zaiyi ba , da na bashi aurenta gara ta mutu na san mutuwa tayi na binneta da hannuna ,ke yanzu da kike cewa bazaki yarda ba wannan maganr data fito daga bakinki ba abun kunya bane agurinki ace surukinki dan fashi da makami ne ?
Tayi shiru tana zubar da hawayen bakinciki “ke kuwa uwar arziki ce zainba?wallahi ina dauting cewar kina da hankali bare aje batun hangen nesa.” a matukar firgice mumy ta dago idanunta tana kallonsa “yes ki kalleni da kyau bazan canza magnta ba,domin kuwa akwai ciwo a kwalkwaluwarki dan duk mai cikakken hankali bazai so hada zuria da wannan tsinannan yaron nan ba wanda tsakanina dashi allah ya isa ne “. yayi maganar yana tsaida idanunshi akanta sannan ya numfasa kana ya cigaba da magana cikin tsananin bacin rai“bazan dauki diyata na bawa dan fashi ba dan “kafin ya karasa maganar ta katse shi tare da mikewa tsaye cikin tsananin fushi tana girgiza kai “ban taba tsamanin haka daga gareka ba ,yanzu har na dawo wannan matsayin “? ni zaka kalla kace ni uwar arziki kuwa“? wallahi ka bani kunya abubakar banyi tunanin haka daga gareka ba wallahi nayi danasani aurenka a rayuwata yau nice mai ciwo a kwakwaluwata ?.”tayi masa tambayar tana zubar da ruwan hawaye .
Dady yayi shiru kawai yana kallonta domin shima bai tsammaci wannnan maganr daga bakinta ba akan just common criminal take data sanin aurensa ? to ma me yayi zafi akan gsky dan haka shima ransa ya qara baci sai dai bai ce daita komai ba dan yasan idan ya cigaba da magana babu mamaki a kokarinsa na ganin ta fahimcesa abun zai zamo rikici da zai kaisu ga jin zafin juna .”
“Idan ma baka bashi aurenta a matsayinsa na dan fashi ba ai ka bawa d’an wanda ya zamo shugaba agaresu?still shiru yayi yana kallonta da sauraronta “me ye bambamcinsu da Ibrahim ?akwai bamba ci sosai a tsakaninsu domin kuwa shi Ibrahim rayayye ne da’aka fitar daga cikin matacce dan shi ba gurbatacce bane ,shi din mutumin kirki ne kuma kema ki sani sai dai yanzu idanunki sun rufe akan cikar burin diyarki kiki fadar gsky ,idan Ibrahim ya zamo siriki agareki zakiyi Alfahari dashi da alfaharin hada zuria dashi ,shi fa wannan gurbataccen ? da wani ido zaki kalli kawaye da mutane gari dashi ?“Wannan tabo ne da har abada bazai gogu ba ,wallahi wannan abun kunya kike yi zainba ke da ya kamata mu hada karfi da karfi mu yake tanwer shine zaki goya mata baya dan kuga bayana to wallahi baku isa ba , kuma ba kece zakiyi da kinsanin aurena ba nine ya dace nayi danasani dana aureki kika zamo silar haifar min diyar da take kokarin kunnawa zuciyata wuta “. yana gama fadar haka ya fita fuuuuuuu ya bar mata dakin ..”
Fashewa tayi da kuka zuciyarta na zafi kamar zata fito waje ,a hankali ta mike ta fito ta nufi dakinta ta kwanta akan gado amman har karfe biyun dare mumy bata runtsa ba tana tunanin wulakamcin da dady yayi mata gbdy damuwa tayi mata yawa but halin da Tanwer take ciki shine worst da yafi damunta dan tasan idan har dady yaki amincewa ta auri adnan zata iya rasa rayuwarta.”
Mumy tayi kuka har taji babu dadi duk sanda ta tuna bakaken maganganun minister sai sabon kuka ya kufce mata ,tana kwance tana matso ruwan hawaye daga cikin idanunta ya shigo dakin yyi kokarin tabata don ya rarrasheta ya kuma sake fahimtar daita illa abinda take son biyewa tan su aikata ta goce ya numfasa sannan ya hade hannunwansa guri daya ya fara magana “zainba ki yafe min maganganuna nayi kuskure amman lokaci yayi daya dace ki fahimceni nasan kina da right akan tanwer amman ta wannan bangaren sam bai dace ki goya mata ba da wannan hadin ba ,wallahi babban ciwo ne atare damu ,duk yadda dady yaso mumy ta fahimcesa amman ina hakan bai samu ba dan kuwa bata sauraresa ba sai ma wani mugun kallo take masa cike da tsana da bacin rai “me kuma zaka fada min nida ba uwar arziki bace ?har kana dauting ina da hankali bare aje batun hangen nesa ,ni da bani da cikakkiyar hankalin da ciwo acikin kwalkwaluwata ta yaya kake son na fahimceka yanzu ?.Yayi shiru yana cigaba da dubanta domin yasan wadan nan maganganun sun fi sauran tsaya mata arai da mata ciwo “am sorry zainab kiyi hakuri amman duk kece sila kina tunanin wani abu zai samu tanwer ne akan rashin aurensa ? “ wallahi babu abinda zai sameta idan ta gaji da kanta zata ma kanta nasiha ta hakura dashi .”
“Ba abinda zaka ce min insaurareka ko in fahimceka tun tuni ya kamata na fahimci cewar yanzu kai baka damu damu ba sai kanka da Ibrahim kake tunani,ka daina damuwa dani da diyata tun randa adnan ya shigo rayuwar tanwer yanzu baka damu da rayuwar kowa ba baka damu da farincikinmu ba ,baka damu da lafiyarmu ba sai kanka data Ibrahim , yarinya tana fama da ciwo acikin zuciyarta amman baka damu ka tausaya mata ka nemo mata magani ba bayan duk kai ne silar faruwar komai ka shuka abinda sakaya ta koma kanta bata ji bata gani ba , alhj tahir yaci amanarka amman duk da haka ka lashi takobin sai ka hada zuria dashi mutumin da yana nan baa nemeshi an rasa ba da zai iya kawo karshen numfashinka at any moment tunda ya iya turo maka yan fashi ai komai ma zai iya yi yaga bayanka,wallahi abubakar kaci amanarta da diyar cikinka …”
“Ki fahimceni zainab Ibrahim dabam mahaifinsa dabam idan kuma kema bakya son Ibrahim ki fad’a mata ta kawo min wani amman banda wannnan mutumin dan …”nima bance Ibrahim bashi da karki ba yana da daidai nashi amman ka duba ciwon da diyarmu take dauke dashi tanwer na dauke da ciwon soyayya wanda at any moment zata iya rasa ranta nidai tunda tace bata so Ibrahim ga wanda take so mu bata mu taimaka mu sa hannuwanmu
mu janyosa jikinmu mu inganta rayuwarsa ya bar sanaar “kina ganin idan shi ya bari sauran abokan sana’arsa zasu bari ne ko kuwa dukkanin su zamu taru mu inganta rayuwarsu dan son rai irin naki?
“Nice ma nake da son rai ?
“Kwarai kuwa zainba kina dashi ke nifa na soma tunanin ba kece kika haifi tanwer ba ina bukatar gwada jinina da nata domin na tabbatar da cewar tanwer diyata ce wacce na diga ko kuma akasin haka kawo min ita a matsayin diyata ban sani ba .”ya karasa maganar a fusace yana dafe goshinsa daya ji yayi masa mugun sara da karfi ,a matukar firgice take kallonsa kafin daga bisani ta fara magana cikin zafin rai da zuciya “gsky ne tunaninka yayi daidai , tanwer ba diyarka bace nima ba diya bace kaga sai ka daina takamar banza akan diyar da bata ka ba ,
kuma kasa ido ka gani zan tsaya mata ta auri adnan inshaallahu kuma zai zama mutun kirki har ma kayi alfahari dashi wata rana.”
jikinsa da hannunsa rawa suka kama ya kasa cigaba da tsayuwa adakin ya fito waje yana kai kawo tausayinkansa dana matarsa dana diyarsa ya kamashi ya kife kansa a bangon falon yana kuka yayinda yake ganin laifinsa ne domin dai yasan shine silar komai shine ya kawo alhj tahir gidansa da har yasan sirrinsa , sannna alhji tahir shine silar da dan fashi ya dasa mugun ciwo azuciyar diyarsa har adalilin haka ake shegenta masa diya ,ya sake fashewa da wani kuka “ya allah kawowa tanwer saukin abinda take ji akan yaron nan ,tanwer ko ba diyar cikina bace ta zama tawa har abada bazan iya rabuwa daita ba bare ma nasan karya ne babu wanda zai kalli yatsun kafafunta yace masa ba diyarsa bace fuska da tsarin jiki ne kawai na mahaifiyarta amman hatta hakoranta irin nashi ne .”
Ranar dai a gidan minister babu wanda ya runtsa daga mumy har dady da tanwer.”
Washegari gidan ya kasance tamkar anyi mutuwa babu wani jin dadi gabdayansu suna daki ,ruky ce kawai ke kai kawo a tsakanin masu aiki ,ta shiga dakin mumy bakinta dauke da sallama yayinda hannunta ke rike da flaks din abincinta ,ta ajiye akan center table ta karaso ta tsaya gabanta “sannu mumy ga abincikinki dan allah ki daure kici wani abu “.kai kawai ta daga mata sannan ruky ta fito ta shiga dakin tanwer ita kanta ta shiga damuwa sosai sakamakon ganin yanayin mumy “sister karki damu inshaallahu komai zai daidaita amman karki yarda ki bata da iyayenki akan wani nmj can wanda zai iya juya miki baya .” tana zaune a dakin tanwee tana kwantar mata da hankali dady ya shigo dakin bakinsa dauke da sallama ya tsaya akan tanwer rukayya ta gaishesa ya amsa mata sannan ta fita ya kalli tanwer ya girgiza kai ita kanta tanwer din sai data sha jinin jikinta da irin kallon da yake mata sai daya numfasa sannan yace “Shikenan tanwer kin hadani fada da matata ? ta girgiza masa kai alamun”a’a !
“Wallahi da Kinsan tarihin haduwarmu da zainba har zuwa lokacin da muka sameki da bakiyi abinda zai kawo tashin hankali a tsakaninmu da zainab ba ,bamu taba samun matsala da zainba sai akanki ya fada yana furzar da iska sannan ya cigaba da magana na fada mata ta fada miki idan baki son Ibrahim ki kawo min wani zan baki shi amman banda wannan dan Iskan yaron ai tana jin haka “tasa masa kuka da karfin gaske “dady ya zanyi wallahi bani da karfin zuciyar da ina da karfin zuciya da zan iya kawar da komai a zuciyata na hakura dashi “
“Dan allah ki ka min dan iskan baki wallhi matsawar kika auri