Showing 99001 words to 102000 words out of 259215 words
Chapter 34 - Kuskuren Baya Complete by Aisha Bagudu .txt
ππππ
ππππππ
PAID BOOK
FREE PAGE
WRITING BY
AYSHA .A BAGUDO
WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukata karanta shi ya tura 500 ta wannan account number din 1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan a tura sai a turawa wannan number+234 703 534 8686 alert domin tabbatar da an tura ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za'ayi sai a tura ta wannan number 08059623096 kada ayi vtu a number MTN ,domin sauraran littafaina a tuntubi Channel dina ta Hausa bakwai.
π
ΏοΈ19
Da misalin karfe tara na daren ranar laraba tanweer tana bathroom tana wanka jaguwa ya shigo d'akin hannunsa rike da tabar wiwi yana zuga a hankali cikin kwarewa ,warin bai tsaya iya d'akin ba har sai daya iskota bayi , abinda tafi tsana kenan ta gansa yana shan wiwi Kuma ta lura ya fahimci bata son hakan shi yasa cikin kwanakin dan iskanci idan zai shigo sai ya shigo mata daita yana sha ,Idan ta kulle kofar d'akin ya zama balai . "
cikin fushi ta fito sanye da doguwar riga hannunta rike da towel tana cewa "dan darajan Allah ka daina shigo min kana Shan wannan abar bana son warinta "kana da ilimi amman kullum kamar dabba kake abubuwanka, tsabar shagala kullum cikin aikata abinda Allah ya haramta kake , wallahi Koni da bani da wani sani akan naka ba zanyi lalacewa irin taka ba, Kaine Zina , Kaine sata , Kai ne sha......."
Wani gigitacen mari ya wanka mata yana huci ta dafe kuncinta daidai Inda hannunsa ya sauka tana dubansa Ido fal da hawaye "akan na fad'a maka gaskiya shine ka mareni ?" to karya ne baka sata ,baka bin mata , baka..."a tsawace yace " Kada ki sake fad'a min maganar banza idan kika sake fad'a min maganar banza wallahi zanyi miki abinda har ki mutu ba zaki manta dani ba ko ubanki bai Isa ya Kalli idona ya fad'a min maganar da kika fad'a min ba bareki" .
tayi shiru tana kallonsa ta kasa cewa komai kafin daga bisani tayi kasa da muryarta ",Allah ka saka min " ya sake d'aga hannu zai sauke mata wani marin tayi saurin kaucewa ta dube shi Ido cikin Ido "da gatana da komai amman ka d'aukoni ka rabani da gatana ka maidani jaka to wallahi na barka da Allah duk abinda ka min ka jira sakamako " tana gama fad'ar haka ta juya zata bar d'akin ya biyota ya shakota ",Ina zaki ki dawo ki gama tsine min ",ni ka sakar min wuya ,bazan saka ba muddin kina son zaman Lafiyarki a gidan nan ki iya bakinki akan abubuwana dan wannan halin naki yana d'aya daga cikin abinda yasa na tsaneki yanzu sam baki da kunya ".
"naji kaima ka daina abinda zai sa na dinga maka rashin kunya , da kyar ta sanya gbdy karfinta ta kwaci kanta tana haki fixgota yayi ya maka akan gado yana mata wani irin kallo mai firgitarwa bayan second biyu ya sawa kofar key ya d'auki towel din data fito dashi ya wuce ya shiga bayi yana jan tsaki .
tanweer ta dafe kanta tana jijigawa "na shiga uku ni tanweer wani irin iftilai ne haka ya fad'a min ? yawon zagin ubana da yake yana mugun bata min rai kusan yafi duk wani wulakanci da yake mata ,da kyar ta rarrashi kanta ta kwanta tana tunani adadin kwanakinta a gidan a lisafinta ta share wata biyu kenan zata shiga na uku a hannunsa tana kwance lamo
ya fito kungunsa d'aure da towel yana goge jikinsa da alamun wanka yayi gajeren wondo ya d'auka ya saka ya kwanta kusa daita tana ganin haka tayi saurin ta matsawa daga kusa dashi dan har lokacin warin wiwi bai bar jikinsa ba ."
ganin abinda tayi yasa haushi ya kamashi cikin fushi ya fixgota jikinsa da karfi ta sake janyewa
ya sake rikota sosai "ke kin isa na kwanta kusa dake ki tashi ? "dame kike takama dashi ? ta bud'e idanunta sosai "bana takama da komai Amman gaskiya ka daina taba min jiki dan ni ba matarka bace sannan ba karuwa bace da zaka dinga had'a jikinka da nawa bazan iya irin wannan rayuwar ba, kawai ka kyaleni idan bazaka maidani gidanmu ba zan hakura na zauna amman bazan iya wannan shirmen da haukan ba wallahi idan baka farga ka tuba ba ka jira mako.." "ya Isa ! ya isheki haka jaguwa ya fad'a a fusace "ke ni zaki gayawa maganar banza akan abinda isana ya bani dama ba".tayi saurin tashi daga jikinsa ta zauna tana dubansa tace "ban fahimceka ba ? menene Isan naka ya baka ba ? Yayi mata kallon banza kana yace "ke mana ni gani nake kin zama mallakina duk da bana sonki kuma dole nayi abinda na gada dama dake ".ranta ya dugunzuma a fusace tace "wallahi karya ne , wiwin da kasha ya fada maka karya baka Isa kayi abinda kaga dama dani ba, Kuma daga yau ka daina taba koina a jikina har sanda zan bar gidan nan tunda bana Uba.. ..."
Ji tayi ya zabga mata mari a fusace tare da durowa daga kan gadon Yana dubanta" Ina gargadinki da ki iya bakinki da furta min duk Kalmar da kika ga dama domin idan ba haka zan miki rashin mutunci dan ni ko kusa ban d'auki mace a komai ba illa abun bukatata ki sani Ina da halin da zan aje irinki guda hamsim idan naso dan ma Kinga na barki haka batare da na aikata wani abun asha dake ba shine zaki kawowa mutane salo ?
"to ni Ina ruwana idan kaga dama ka cika gidan nan makil da karuwai wannan matsalarka ce ni dai karka tabani ".
Ya Isa Inda ya ajiye wayoyinsa ya d'auki daya daga ciki ya duba lamba pretty ya kira ya sa a handsfree ringing biyu muryata ta fito tana cewa "Allah ya taimaki jaguwa uban gidana , jaguwa yace "pretty kina Ina ? Ta lankwashe murya kmr tana gabansa tace "Ina gidansu ogechi yanxu muka shigo gida "kuzo ku duka bai gama maganar ba tanweer ta k'araso ta fixge waya hankalinta a matukar tashe da abinda ke Shirin faruwa, a gabanta zai kira karuwarsa wannan wacce irin rayuwa ce ? "Wacce irin rayuwa ya saka kanshi "ita da wasa tace ya cika gidan da karuwai shine zai kirasu wayyo Allah na shiga uku " akansa an kirata da Kalmar karuwa ,yanzu km zai gayyato karuwai zuwa gidan "to me zai hana ka maidani ka samu damar yin iskancinka da tushe tunda shine a gabanka ? tayi maganar a matukar tsorace dan tunda ya fara da maruka tasan duka ma bazai masa wuya ba.
ta juya cikin sauri ta bar d'akin zuwa bayi tare da fashewa da kuka "a she zata tsinci kanta cikin makauniyar soyayya irin haka , hakika so bai mata adalci ba daya rasa Inda zai Kai soyayyarta sai gurin mutumin da bai san darajan mace ba bata San tsawon lokacin data dauka ba a zaune a toilet tana ayyana abubuwa da dama akan rayuwarta " bazata taba yarda tsoransa yayi tasiri a zuciyarta ba muddin soyayyar da take masa ta gaskiya ce ya dace tayi komai dan ta rabashi da irin rayuwar da yake, zata rabashi da kowacce karuwa acikin rayuwarsa ta yunkura da kyar ta mike ta fito haniya ta dinga Jiyo sama sama aranta tace "sun zo kenan ? ta fito ta nufo babban falon gidan Inda tafi tunanin suke ta iske mata zaune kusan tsirara domin kowaccesu daga ita sai pant da bra shi Kuma jaguwa yana nan sanye da gajeren wando ajikinsa , hayakin taba kawai ke tashi da kwalayen taba burjiki akan tebul din gabansu Sam basu lura da fitowarta ba har sai data karaso har gabansu ta kira sunansa da fusatacciyar murya "Adnan !" duk sukayi hanzarin suka tsaya cak suka bude idanunsu suna dubanta Shima din idanunshi ya zuba mata cikin mamaki da fushi yace "me ya fito dake ?
"Ko nace ki fito ne "a fusace tace ban sani ba wato kana tunanin zaka kawo karuwai cikin gidan nan alhalin Ina cikinsa in amince wallahi tallahi baka Isa ba , bazai yiwu ba sai dai kayi daya cikin biyu ka mayardani gidanmu ko ka bani damar na fita a gidan nan na kama gabana amman muddin Ina cikin gidan nan an daina alfasha da kawo yan iska kana badala dasu sai dai kaje waje kayi iskancinka ta k'arasa maganar tana fashewa da kuka ",wallahi bazan yarda ba ya zama dole su bar gidan nan kuma a yanzu ..."
Pretty ta sheke da wata mahaukaciyar dariya tana dubanta , jaguwa kuwa har lokacin duban tanweer yake cike da Jin haushin abinda tayi masa , a natse ya mike zuciyarsa na suya ya riko tsintsiyar hannunta ya soma tafiya daita "baki Isa ki bata min moon din ba Ina bukatar naci mace Kuma dole naci ko dan Kinga Ina raga miki ? "ni agurina sun fiyye min ke sau dubu tunda zan kusancesu yadda nake so batare da Jin haushi ko rashin kunya ba wad'an ko cewa nayi su kashe mutun zasu bi umarnina kuma wallahi idan baki bini a sannu ba sai kinyi kuka da idanunki bai tsaya koina ba sai a d'akin daya sauketa yayi wurgi daita "ki daina takamar banza domin baki da wani mahimmanci a gareni da kike ikirari su bar gidan nan naki ne ? Tayi shiru tana kallonsa qirjinta na dokawa "ko akwai kwadala ko kwayar bulo na ubanki aciki da kike cewa mata bazasu shigo ba ? dan Isa har kina fad'ar sai sun fita sun bar gidan Nan " still shiru tayi hawaye na zuba mata shima shiru yayi yana kallon kwayar idanunta nan Kuma zuciyarsa tayi rauni sam bai ji dadin abubuwan da yayi mata ba a daren ba amman ya zai yi duk bakinta ne ya janyo mata ?
" yayi ne dan yana son ya nuna mata iyakarta ne da jikinta da take takama dashi , kuma kar ta d'auka yana sonta ne dan shi kyawun mace baya rud'arsa Kuma baya d'aga masa hankali.
dan shi mata ke bi suna kuka tunda ya had'u da pretty yau shine karon na farko daya kirata a wayarsa kullum itace ke hauka akansa dan ya quntata mata ne yasa ya kirata yau Kuma idan da hali ma a gabanta zai kwanta daita ta hadiye zuciya ta mutu dan yasan tana mugun sonshi daman Kuma shi haka yake.
mace ma tana kuka akanshi Ina ga ita da babu abinda bai ta'ba ba ajikinta ba ,ya murza dukiyar fulaninta ya kusanceta duk da bata cikin hayyacinta amman yasan dole zata ji fellings akanshi a haka ma kenan Ina ga tana cikin hayyacinta da kuka zata dinga masa ya aureta . tsaki yaja kana yace "Yana da kyau ki gane kyawunki bazai ta'ba rud'ata ba dan hk ki shiga hankalinki ,ki tsaya iya matsayinki idan kika qara min shishigi na rantse da Allah sai naci ubanki Kuma dan Allah ki bari naga kafarki a falo madadin nayi having sex dasu dake zan kwana Ina yi idan kince karya ne go a head yana gama fad'ar hk ya fita daga d'akin."
zubewa tayi akan bed tana wani irin kuka shi kuwa yana dawowa falon kudi masu yawa ya mikawa pretty ya sallamesu da kawayenta ta kwa'be fuska "haba jaguwa ya zaka min haka nifa gaskiya a bukace nake da Kai mun kwana biyu bamu hadu ba "raina a ' bace yake bazan iya komai ba ya fad'a tare da juya wa ya barsu nan , kwa'be baki sukayi sannan kowacce ta d'auki jakarta ta rataya suka fito",gskiya gayen dan wulakanci ne nifa gbdy na kwadaitu dashi dan yadda kika bamu labarin dadinsa har Allah Allah na dingayi mu had'e "uhm ai bakisan halin jaguwa bane rowar balai ne dashi amman bafa rowar kudi ba rowar jijiyarsa idan bai so ba komai zakayi bazai ci ba amman idan yaso zaki san kin hadu da nmjn duniya ,Inda kikasan an zauna an koya masa yadda zai ci mace ne ya iya bin mace lungu lungu sako Sako bare ya dauraki a saman jijiyarsa uhmmmm Abu sai Wanda ya dandana " kawai muje mayi maleji da wasu "wayyo Allah wallahi naso naji wannan dadin suna tafe suna maganarsa har suka k'araso bakin jection Inda zasu shiga mota ."
****"
Washegari da misalin karfe biyu na rana IPO na zaune sai ga anas ya fito d'aga cikin part dinsu Kai tsaye boy's quarter ya nufa ,ya bisa da kallo kafin a hankali ya tashi yabi hanyar daya bi adaidai lokacin anas ya shiga wani d'aki daya lura suna yawon shiga ,Kuma babu shamaki ga kowannensu suna shiga Kai tsaye, Kuma kowannensu nada extra key a hannunsa dayazo budewa yake yana Jin alamun anas na ΖoΖarin fitowa yayi saurin ja da baya ya boye yana sauke naunayen ajiyar zuciya cikin sauri anas yaxo ya wucesa yana ΖoΖarin saka key abayan wandonsa aka kirashi a waya , cikin tsautsayi key din da yake k'okarin turawa byn wandonsa ya fadi ya wuce yana amsa wayar .ya wuce da kamar minti biyar IPO ya fito daga maboyarsa ya tsugunna ya d'auki key " da alamun zamana ya kusan karewa a gidan tun bai yi kwanakin da aka bashi ba ya fad'a a cikin zuciyarsa , cikin sauri ya k'arasa ya bud'e kofar ya tsaya yana kallon cikin d'akin kafin daga baya ya shiga ,
d'akin duhu dan ko tafin hannunka baka gani duk da kasancewar safiya ce
a hankali ya Ciro wayarsa ya qunna wuta haske ya gauraye d'akin nan yaci karo da fuskokin mutane kala dabam dabam fuskokin sunfi guda dari uku zube a kasa .
Cike da rawar jiki ya k'arasa sosai yana kallonsu d'aya byn daya kafin daga baya ya d'auki d'aya yana dubawa domin bambamcewa "shin na mutane ko kuwa akasin haka ?ya tambayi Kansa dan bashi da maraba dana mutane har gashin Kai da kunne da Ido komai na bil adama ne, sai dai a kallon kurrilla da yake wa fuskokin ya fahimci na