Showing 171001 words to 174000 words out of 306755 words
Chapter 58 - YAR DANDI CEH COMPLET BY SAADATU BINTU ABDULLAHI.txt
Masha ALLAH yakeyi yanata yabawa da kyaunsu amma yafi yaba na hilwah inyazo knta ita kadai kuma seya kira sunanta se yace tayi kyau sosai, AB'ILAL dake zaune yana jinsu yana shan farfesun naman kan shima tini ya gama cin tuwon, kawai yaji farfesun ya fita a ransa jin yabon Alhasan ga hilwah yayi yawa, tin yana daurewa har ya kasa, yaji duk ya tsani farfesun , zuwansa ma side din seda yy nadama , ya tashi ya fara kokarin barin falon, sbda ba karamin sosa masa rai alhasan keyi ba na yabon hilwah da yaketa karayi. Duk suka bishi da ido ganin ya tashi yana niar barin falon, hilwah ce kawai bata kalli inda ma yake ba, ta kauda fuskarta gefe amma taga tashinsa a kn kujerar da yake zaune. "Ina zakaje?'' Cewar hajiya maryam. AB'ILAL yasan da shi take mgnr dan hk yace " A zanje side dina ne... Ba tare daya juyo ba yy mgnr amma ya dakata daga tafiar da yakeyi. ''Inason inyi mgna dakai..." Cewar Hajia maryam. AB'ILAL ya juyo yace "ok Auwal hubb, zuwa gobe?'' Amihh ta watso masa harara tace "Yau ba gobe ba...'' AB'ILAL yace "ok...'' Ba tare daya jira cewarta ba ya fice a side din. Amihh ta bishi da ido ta basar kawai, abun nashi se shi, se ita kuma data zama uwarsa, wani abun dole se uwa zata iya shanyeshi ga yaronta. Suka ci gaba da hirarsu, har wuraren 9:20am hilwah da salwah suka nufa dakin salwah, suna shiga dakin hilwah ta fada barhroom,ba jimawa ta fito daure da bathrobe peach color. salwah dake zaune gefen bed ita ta riga ma tasa kyn baccinta maroon riga da wando ne a jikinta dayake tayi wanka tinda zatayi sallar isha'i. ta zubawa hilwah ido ba karamin sha'awah fatarta ke bata ba, kullum cikin kyau take, kuma ta kula bata shafa komi kawai hk Allah ya halicceta. "Madam kizo ki tafi side din mijinki fa..." Hilwah ta kalli salwah tace "aah ni a nan zan kwana ai..." Salwah ta zaro ido tace "ki rufamin asiri da Amihh, knsan halin Amihh se tace ma ni ke zugaki..." Hilwah tace "toh nide a nan zan kwana..." Tana fadar hkn ta nufa drower din kayan baccin Salwah ta bude ta dauko wata riga me mugun kyau dark peach me digo digon laces me shape din heart ba karamin kyau rigar ta mata ba, tanada gidan nonuwa wato breast cup aiko nonuwanta suka cika rigar taf taf harma suka bulluko ta saman rigar sbda nonuwan nata sunfi girman cup din bra din, iya cinyoyinrta rigar ta saya, color din rigar ya dace da skin dinta, Ta kamata sosai rigar ta mata kyaun da bakina baze iya misaltasa ba, ta saki sumar kannan nata wadda keta walwali har zuwa gadon bayanta, Salwah ta bita da ido ganin yadda rigar ta kameta ya bata mamaki sbda ita rigar ta mata yawa amma inka gnta kaga hilwah a zahiri zakasha Salwah tafi hilwah kiba sbda salwah nada garin jiki, ita kuma hilwah barawon jiki gareta. Shape ne hilwah tafi salwah ba jiki ba, ita jikinta dan dai-dai ne komi ta saka seya mata kyau sbda jikin nata daukar kaya garesa. Salwah ta gaza daurewa tace "rigarnan ta miki kyau wlhy, knga yadda ta amsheki kuwa..." Cewar Salwah. Hilwah tace na gode, ta karasa ga dressing mirror ta dauki perfume dinta ta feshe jikinta dashi, (akwai perfume dinta a nan dakin salwah, kuma akwai a dakinta na side din Ab'ilal.) Salwah nata binta da ido har ta gama fesa perfume din, ta karaso ta rabe gefen salwah ta haye kn gadon ta shige cikin duvet salwah dake zaune ta saki baki tace "duk wannan rigar da kk saka amma ki kwana a nan, ai wlhy ki tashi ki tafi side din Yah AB'ILAL..." Hilwah ta marairaice kwayar ido tace " korata kkyi kou? Shikenan bari in tashi .." Ta karashe mgnr tana yunkurawa ta tashi zaune, Salwah ta mayar da ita ta kwantar tace "Ah'a ni bn koreki ba my, ki koma ki kwanta nasan Amihh se tazo ta koreki, itade tafiso kiyita zama a side Dincan me cike da kunci...." Hilwah tayi murmushi a ranta tana tunanin ta yaya salwah tasan side din AB'ILAL na cike da kunci. "Ni de plx dea ko Amihh tazo kice nayi bacci dan ALLAH." Hilwah tayi mgnr da muryarta me cike da shegen ddh hadi da shagwaba da karyayyen harshenta, salwah data tashi ta dauko system dinta ta dawo Ta zauna ta kwalalo dara daran idonuwanta tace "kikace?'' Hilwah ta kara maimaita mata abinda tace. Salwah tace "Tab ba ruwana... Ni amihh da yah AB'ILAL tsoratani sukeyi, sun cika fada fada, yah ab'ilal ma ita ya biyo a fada, a.ma ya fita jaraba ..." Hilwah tayi Murmushi kawai. Tace ''ni de ki ce wa Amihh nayi bacci plx sister in kkyi min hk zan baki wani labari me ddh gobe..." Salwah uwar yan son labari cikin zakuwa tace "tom zan fadi, promise zaki bani lbrin?'' Hilwah tace "I Promise..." Salwah taji ddh sosai ta bude system dinta ta fara dubata Hilwah na kallonta, salwah na danna keyboard din system din tace "Dea in tambayeki wani abu?'' Ta karashe mgnr tana juyowa ta kalli Hilwah wadda ta daga mata kai alamar e . "promise me zaki gayamin koma meye plx?" Hilwah ta kara daga mata kai alamar eh. Salwah ta gyara zamanta sosai da zaman system din dake jikinta tace "Amma de ke ba bahaushia bace kou?'' Hilwah ta daga mata kai alamar Eh. Salwah tace "haba shiyasa hausarki ba irin tamu ba, amihh ba bahaushi bace amma ta iya hausa sosai itama datayi mgna zaka fahimci ba bahaushia bace, ita indians ce, ke wani yare ce?'' Hilwah tace "nima na mnta yarena....'' Salwah ta hade rai tace "bawani baza ki gayamin bane, amma de wata rana ai zamuje nida ke gidanku kou?'' Hilwah tayi jim ta zubawa salwah ido ba tare data bata amsa ba, a karshe ta sakar mata murmushi hadi da juyawa tace "gobe zan gaya miki E ko Ah'a..." Tana fadar hkn ta kudindine knta cikin duvet din tayi shiru kmr tayi bacci nan ko duniar tunani ta afka na iyayenta salwah ta sosa mata wani ciwo a zuciarta ada yadda take da iyayenta baza ka taba cewa wai zata iya tafiar 2days ba ta barsu sbda so da kauna, amma ynzu ita ce kusan shekara daya da rabi batasa iyayentaba a kwayar idonta , gashi ynzu ko picture babu, da shi take gani taji ddh. Salwah ta bita da ido kawai bata kara takurata ba da tambayar dukda tana cike da tsananin son sanin wacece ita, taci gaba da duba system dinta dake kn cinyarta.
Nan falon Amihh da Alhasan suka ci gaba da hira, se 9:43am Alhasan ya bar gidan zuwa gidansa, be samu damar tsayawa a side din AB'ILAL ba sbda kada dare yayi masa sosai dan hk yayi tafiarsa zuwa gida da niar zuwa gobe Ze samu abokinsa kn abinda ke damunsa a rai a kn hilwah, sbda abun na cinsa sosai. Bayan tafiar alhasan Amihh ta nufa bedroom dinta tayi wanka ta shirya cikin kayan baccinta duk tanajin jikinta na mata rashin dadih, sbda gjyr Aiki, ta daura hijjabinta a kn kayan baccin dake jikinta masu dankaran kyau, ta fito ta nufa dakin salwah. Ta tura kofar dakin ta shigo, har lokacin salwah na zaune tana duba system dinta hilwah tana kwance ta kudindine. "Hilwah tayi bacci ne?'' Itace kalmar data fito daga bakin Amihh ta karaso cikin tsakiyar dakin. Salwah na ganin ta shigo ta rufe system din sbda respect kana tace "A tayi bacci Amihh..." "Bacci kuma a nan bayan mijinta na nan, batan kai tayi kou, ke kuma kina ganinta tayi baccin kenan, to yy kyau, tasarmin ita, muje side din mijinta...." Cewar Amihh. Salwah jiki na rawa ta hau tattaba kafafuwan hilwah dmn tasan se amihh taga lefinta dan ita bata wankan tsarki daga lefi. Har bacci ya dan fara figarta sbda bataji ma shigowar amihh ba dakin. Kawai sede taji ana tabata dole ta tashi hadi da bude fuskarta da duvet din data rufe knta dashi, ta juyo taga Amihh tsaye ta tashi zaune Amihh ta zuba mata ido tace "wayace kiyimin bacci a nan , maza tashi mu tafi side din Mijinki...." Badan hilwah taso ba, sedan bata iya ma Amihh musu ta sauka daga kn bed din jiki a sanyaye .... Amihh ta bita da ido, tana kallon irin halittar da ALLAH yama yarinyar kasannan ya cika fam, har yama fi samanta cika, ga cikinnan nata a shafe kai kace ma babu hanji a cikinata, ga uban suma har gadon baya, tako ina yarinyar ta cika 100% akwai diri da cikar zati. Zira slifas dinta tayi me laushi ta dauko hijjabinta na sallah ta saka tama salwah seda safe Amihh ta matsa mata ta shige gaba ta fice a dakin Amihh ta biyota a baya suka fice a falon zuwa side din AB'ILAL. Hilwah ta fara tura kofar falon ta shiga bakinta dauke da Sallahma, Amihh ta biyo bayanta, hnyar bedroom dinta ta nufa Amihh tace "Dawo nan ki zauna, ai mgna zanyi daku keda AB'ILAL...." Hilwah jiki ba laka a ranta tana me tunanin wacce mgna amihh zata musu kuma ita da wannan mugun, dawowa tayi ta zauna kasan carpet din tsakiyar falon, tayi kasa da knta. Amihh ta tsaya ta dan zuba mata ido , ba karamin son yarinyar takeyi ba da ganin martabarta sbda dagani ta samu tarbia in har ta umurceta abu ko bataso tanayi sbda tana ganin mutumcinta ba ita ba duk na gaba da ita tana ganin mutuncinsa, kuma sam bata da hayania. Juya kai amihh tayi ta nufa hanyar dakin AB'ILAL tana me yabon halin Hilwah a ranta. Ta karasa bakin kofar dakin nasa, takai hannu ta fara knocking din kofar dakin, yana ciki yana ji amma yy kmr beji ba, kwance yake kn bed dinsa, abu yakici yaki cinyewa kawai ji yakeyi zuciarsa na masa kunci tin dawowarsa daga side Din Amihh, ya kwanta ga sha'awah na cinsa ga kunci naci masa zucia wanda besan dalilinsa ba, yasan de rabin kuncin nasa na yadda alhasan ya amshi picture dinta yanata gani ne, seya ayyanawa ransa kilama da tsinaniar shigarnan ya ganta kawai zuciarsa ta sanar dashi ai har nononta ma ya gani sbda rigar matsatstsiya ce, shi fa be gani ba kawai zuciarta ta masa wannan zanen har zanen kayan jikinta seda zuciarsa ta zana masa aiko haushi ya kara rufeshi wato de ita bazata taba dena karuwanci ba, a asibiti ma seda tayi karuwanci ina maga gida, wannan abu naci masa tuwo a kwarya, tabbas ya yadda yarinyarnan bata da kamun kai, tinda Gashi har tana nunawa alhasan picture dinta yanata gani yana yabawa da halittar da Allah ya mata, bakin ciki da tsantsar tsanar yarinyar suka kara Yawaita a zuciarsa. Daga wajen Amihh na knocking din taji shiru tasan yana jinta sbda ko bacci akeyi ya isa ace yaji wannan knocking din, bude baki tayi cikin daga murya tace "AB'ILAL! Muhammad! Muhammad!!'''' Jin muryar amihh yasashi dirowa daga kn bed cikin hnzari besan ita bace ai da tini ya amsa, shi ga zatonsa salwah ce sbda ita daya ce ke iya kusanto kofar dakinsa tayi knocking to yaci abnci shiyasa ya rasa dalilin dayasa ake masa knocking din daya ke shima dan bani na iya ne yayi bnza, daman zani ce ta tadda muje. Saita knsa yayi ya graya jallabiar dake jikinsa ya zira slifas dinsa na yan hutu ya nufa kofar dakinsa ya kai hannu ze bude, dai-dai yaji amihh ta fara spark. "Wani irin wulaknci ne wannan ! Kanaji ana mka knocking kayi shiru dan bura uba kawai!!'' Cewar amihh. Bude kofar yayi ya fito ta kalleshi taci gaba da matsifar. "Nasan kana jina, dan bura ubanka!'' AB'ILAL ya zuba mata ido kawai yace "Am sorry Auwal hubb..." Kwafa Amihh tayi iskncin AB'ILAL na bala'in ci mata turo a kwarya,tasan baze taba denawa ba, sbda tin yana karaminsa hk yake, wai a hkn ma dan tana hadawa da adduarh.. Hilwah dake zaune nan kasan falon tana jiyosu sama sama amma bata iya cewa ga abinda suke cewa ba, sbda dakin nasa ya dan shiga ta wani corridor. "Wuce muje mgna zanyi dakai da matarka...." Amihh tace da AB'ILAL ya bita da idanuwansa na rashin kunya ba tare daya daga kafafuwansa ba yace "Wacce matar kuma?'' Amihh ta watsa masa harara tace "Matar wan ubanka!'' AB'ILAL yaja bakinsa yayi shiru tayi gaba ya biyo bayanta dole kodan gudun mgnarta ya biyotan, suka karaso falon, idanuwansa suka sauka a kn hilwah wadda ke zaune a kasan carpet din tayi kasa da knta, kasancewar akwai yalwar haske a falon hkn ga bashi dmr gano color din hijjabin jikinta dark ash ne , be samu dmr ganin fuskarta ba, sbda knta yy kasa sosa dataji tafiar tasu ne ta kara kasa da knta sosai. Amihh ta karasa ta zauna a kn kujerar 3ct tayi crossing kafafuwanta AB'ILAL ya karasa ya zauna kasa gegenta na dama, yayinda hilwah ke zaune tsakiyar carpet din, AB'ILAL ya kalleta a Karo na biyu nan take yaji takaici da haushinta sosai yayima zuciarsa dirar mashi ji yy kmr ya rufeta da duka, gabaki daya dunia haushi take basa, kuma wai se amihh ta hadasu zata musu mgna , dame tsarki da mara tsarki kenan .." Ya fadi hkn a ranta shifa dunia kara jin haushin yarinyarnan yakeyi kullum, ganinta yakeyi a mara kamun kai, koda yake ai ta saba da rashin kamun kai. Ya kara fadi a ransa. Gyaran murya amihh tayi kana ta fara mgna murya cikin dattako. "Inaso ne, in kara doraka a hanya dannaga alamar a karkace kake...." Amihh tayi mgnr kwayar idonta na kn AB'ILAL ya dago ya kalleta kawai ya sadda knsa kasa amma fa beji dadin mgnr nan data fada masa ba a gaban yarinyarnan. "Kai tinda kukayi auren nan, sau nawa ka kwana a dakin matarka?'' Amihh tayi tambayar da AB'ILAL, dagowa yayi ya sake kallonta ya sadda knsa, ba tare daya amsata ba sbda besanma amsar tambayar tata ba, haushi ya da zallar takaici ya rufe Amihh kunsan da zafi kna mgna da mutum ya mka bnza. "Bada kai nake mgna ba!'' Amihh ta kara fadi cikin tsawa. AB'ILAL da knsa ke kasa yace "nifa ban fahimci me kk nufi bane Amihh...." Hajiya maryam ta tsure sumar knsa da ido tasan ya fahimceta tsabar isknci ne, sbda cikin iskncin yy mgnr, kullum amihh na masa fatan shiriya amma ina se kara band'arewa yakeyi kai kace a tsakiyar kasuwar dunia aka haifesa. "Au baka gane ba? Zaka gane idan na zabgo maka ashar....'' Amihh ta fadi a hasale. AB'ILAL yayi shiru kawai yy kasa da knsa,. "Dan dangin ubanka nace sau nawa ka kwana a dakin hilwah matarka ..." Ta karashe mgnrta tana nuna masa hilwah da knta ke kasa tana sauraren abinda ke faruwa ba karamin takaici abinda AB'ILAL din yace ya mata ba, ta rasa dalilin dayasa taji Takaicin. Shiru AB'ILAL yayi kmr bejin me Amihh tace ba, shi abin ma kara masa haushi yy dmn da haushin a ransa. Hajiya maryam ta girgiza kai kawai tasan ba amsata zeyi ba, ya shahara a rashin kunya ita da knta ta sani. "Very soon zan saita mka yan iskan dake knka, kai ka sanni sanin idanuwanka,...dana aura mka ita an gaya maka na ajiye ta ne, dankayi ta kallonta, ko TV ce? to daga yau zata koma dakinka da kwana ko kuma kai ka koma dakinta da bacci..." AB'ILAL ya dago kwayar idonsa a razane ya saukewa Amihh su jin tace wai ta dawo dakinsa koshi ya koma dakinta, fuska dauke da alamar ayar rashin fahimta AB'ILAL yace "kmrya?" Amihh ta amshe da "Kmr yadda kaji ai inasha kanaji kana gani kou? Kanada lafiar kunde ai , to abinda kunnenka ya jiye maka shi na fada... , ko ta koma dakinka ko kai ka koma dakinta, na kara maimaita maka dan qaniarka ...." Hilwah ta dago nata kwayar idon a razane, ta zubawa amihh ita se ynzu ne ta kara fahimtar zancen Amihh, a farko ta daburce bata fahimta ba, se ynzu da Amihh ta maimaita ta fahimta sosai. AB'ILAL ya dago ya Kalli Amihh yasha mur sbda tana gaya masa abinda bazeyu ba, hade rai sosai AB'ILAL yy kna ya fara mgna cikin isa "Amihh wani irin na koma dakinta ko ta dawo dakina kuma why plx? Gaskia ni de knsan ba dan iska bane ta yaya zan kwana daki daya da mace....." Hajiya maryam ta saki baki tana kallon ikon Allah shi da anyi mgna se yace waishi ba dan iska bane. Hilwah knta seda ta dago ta kalleshi jin yace shi ba dan iska bane wato yana nufin ita ce yar iska, taji zafin wannan klmar da kalmar karuwa da kalmar yar iska suna mata zafi a zuciarsa, ta maida knta kasa tana mejin zuciarta na nukurkusar haushi da takaici. "Karka kara min mgnr isknci in ina mgna Kaji na gaya maka! inma kai ba dan iska bane da can ynzu zaka zama dan iskan dole, matarka ce ta sunna nace ku kwana daki daya ba kwanan dadiro nace kuyi ba..." Amihh ta fadi kwayar idonta na kansa, shima ya dago nashi idon ya sauke mata byn ta idar da mgnrta ya dasa da tasa "Gaskia Amihh dazaki temaka dakin hkra da mgnr a