Showing 162001 words to 165000 words out of 306755 words
Chapter 55 - YAR DANDI CEH COMPLET BY SAADATU BINTU ABDULLAHI.txt
tari wata nurse Christan, cikin harshen turanci ta tambayeta ina ne office din DR MARYAM M.A. nurse din ta mata jagora zuwa har office din Amihh ita a Zatonta ko hilwah yar Amihh ce. Hilwah ta mata Godia bayan ta rakota har cikin office din Amihh, nurse din ta juya ta fice a office din. Hajiya maryam tayi gaggawan sallarmar patient din dake gabanta, tace a dakatar da wasu, kafin ta gama uzurinta. Amihh ta taso daga kn kujerarta ta karaso inda hilwah take fuskarta dauke da fara'arh da murmushi, ta zauna gefen hilwah, kasancewar kujerar 2ct ce, office din babban office ne irin na mnyan likitoci da akeji dasu a asibitin. Hilwah ta gaida Amihh ta amsa zucia fal kaunarta ta tambayeta ina AB'ILAL din, hilwah tace yana motar. Takaici ya kara rufe zuciar Amihh taso ace ya iso office din nata, da yau se yasha wulaknci a gunta. Kinci abinci?'' Amihh ta tambayi hilwah. Daga mata kai hilwah tayi alamar eh , Amihh tace 'Ok. .." Ta tashi ta dauko allurar dazatayi mata tana me duba time 10:44 ake nema, jan allurar Amihh tayi tana takaicin AB'ILAL. Ta karaso tace hilwah ta tashi ta juya ta mata allurar. Tashi tayi hadi dayin narai narai da ido kmr zatayi kuka, dmn da kyar amihh ke mata allurar sbda batason allura.lallabata Amihh ta shigayi, da kyar ta tsaya aka mata allurar harda hawaye a hk ma dan Amihh bata da zafin Allura ne kwata kwata. Amihh ta rungumeta a jikinta bayan ta mata allurar ta shiga bubbuga mata baya tana me bata hkri. "Sorry sweet hk zaki haihu kuwa anya? Ko de se CS za ayi ne? Uhm? To ki hkri knji sweetheart..." Amihh ta fadi hadi da rungumota jikinta sosai, se faman hawaye takeyi. Amihh ta rarrasheta sosai da kyar ta samu ta hkra ta goge mata hawayenta, ta dan zauna na 10mnt kama amih ta rakota har wajen cikin asibitin dai-dai kofar dazata fita daga asibitin amihh ta batta sbda wani dr dayazo ya jata zuwa duba wani a emergency. Hilwah ta fito farfajiyar asibitin a zatonta ko bazataga motar tashi ba sbda jimawar da tayi seta ganta ajiyar zucia ta sauke ta fara tafia a compound din zuwa inda motar take, wani babban mutum da tin shigarta ya ganta ya zauna yana jiranta tin dazu, ya biyota ta karaso bakin motar tana niyar shiga ya dakatar da ita cikin isar mata da aminci wato sallama ta dakata daga kai hannunta motar ta juyo ta amsa sallar tasa hadi da zuba masa sexy eyes dinta, babban mutum ne dagani nera ta zauna a kalla ze Kai 65yrs baki neshi kirin but yanada kyau, danyar shaddace a jikinsa royal blue se kyalli takeyi dagani me tsada ce. AB'ILAL dake cikin motar ya cika fam fam kmr ze fashe sbda yadda taje ta jima a cikin asibitin byn tasan yana nan yana jiran yana kallonta tin fitowarta daga cikin asibitin har zuwa ta karaso bakin motar, motumin ya biyota nan ransa ya kara bace, kmr ze hadiye zucia ya mutu sbda takaici ya zuba musu ido yanaji a ransa kmr ya fita ya shakure wuyan guy din sbda haushinsa da yaji yanaji a ransa, tsabar bacin rai ko ganinsuma ya denayi sosai, Wato a asibitinma se tayi karuwancin....'ya fadi a bayyane cikinn hasala. Daga wajen mutumin yaci gaba da mgna yana washe baki kmr yaga wawan zama tin dazu daya gnta yace shi ai yayi matar Aure. Hilwah de ta bishi da ido kawai. "Sannu beautiful! Ni sunana Alhaji Ibrahim sani, na ganki kuma knyi min,...ko zan iya samun lmbr wayarki sbda naga ynzu kina sauri ne...amma Allah yayi halit...." Alhaji Ibrahim ya gaza karasawa sbda ganin AB'ILAL ya bude motar dreva seat ya fito fuskarnan tashi baki kirin kmr baqin maciji mesa, ya zagayo inda hilwah da Alhaji ibrahim suke zucia kmr zata fashe... Tin fitowarsa a motar Hilwah ta dawo da kwayar idonta knsa, gabanta ya yanke ya fadi ganin irin bakikirin din da fuskarsa tayi, se uban huci yakeyi kmr ze tarwatse, nan take jikinta ya hau kakkarwa.... Hnklin Alhaji ibrahim ya kara tashi gabansa yayi mummunar faduwa ganin yadda fuskar AB'ILAL din keta kara baki kirin kuma Gashi yana tinkarosa.
*littafinnan na kudi ne.... 08136349646*
08/01/2022 à 18:24 - SAADATU BINTU ABDULLAHI: 37***
Tinkarosu yakeyi gadan gadan zucia na kuna, hadi da tafarfasa, se faman hada hanya yakeyi sbda kunar zucia, idanuwansa ma nuna masa sukeyi kmr murmushi hilwah keyima mutumin. A matukar harzuke ya karaso inda suke daf daf da Alhaji ibrhm ya tsaya kwayar idonsa na kn hilwah wadda itama shi din take kallo hnklinta a tashe yayinda kaf jikinta keta faman rawa. "Keeee!! Shiga mota!!'' Itace kalmar data fito daga bakinsa cikin tsawa, firgita hilwah tayi a matukar rude ta bude murfin motar ta shiga gidan baya, jiki na rawa, ji takeyi kmr zuciarta zata fashe. AB'ILAL ya dawo da dubansa kan alhaji ibrahin wanda ya zuba masa ido jin yace hilwah ta shiga mota ya bashi tabbacin ko yayanta ne. "Ina wuni yayanmu..." Alhaji Ibrahim ya rissina ya gaida AB'ILAL cikin girmamawa , AB'ILAL ya zuba masa ido kallon kiyayya yake jifansa dashi a ranshi yanaji kmr ya shakuresa dande kawai ya kai zuciarsa nesa ne, zucia ta kara zuwarma AB'ILAL wuya jin mutumin ya kirasa da yaya, shi ganinsa rainin hnkli ne. "Look ni ba dan iska bane ka gane Kou? Uban meye hadinka da ita dazaka mata mgna! Wannan Ai isknci ne, da rashin sanin daraja!!'' AB'ILAL ya fadi cikin kunar zucia besanma ya fada ba, yayin da kwayar idonsa ke kn alhaji ibrahm. Alhaji ibrahim firgita yayi jin yadda AB'ILAL ke masa mgna cikin tsawa, kmr ze zaburo ya watsa masa mari, kalaman AB'ILAL sunyima Alhajin zafi amma ya daure, sbda son yarinyar yakeyi da gaske. alhaji ibrhm ya kara tsorata ganin kallon da ab'ilal ke jifansa dashi, duk yabi ya tsorace sbda yasan in aka barshi dashi se buzunsa, kirar karfafa garesa irin mazannan yan dambe.. "Bada kai nake mgna ba! Nace menene tsakaninku da ita! Ko an gaya maka nan gidan karuwai ne dazaka tare ta a titi!!'' AB'ILAL ya kara dakawa alhaji ibrahim tsawa murya cikin karad'i da bala'i. alhaji ibrahim jiki na rawa ya fara mgna sbda ganin kmr AB'ILAL na shirin yin ball ne dashi ''Ammm..am sorry ni bada wata manufa na mata mgna ba na ganta ne inaso kuma ni Aure...." Tin kafin ya karasa AB'ILAL ya dakatar dashi yana me jin kmr ya shakuro wuyansa sbda tsabar tsananin jin zafin kalaman nasa wato ma ze Aurenta zeyi...''se aka gaya maka neman miji takeyi! Ko an gaya maka budurwa,ce ita!! Manemin matan mutane!!wannan Ai isknci ne da wulaknci da rashin sanin darajar matar mutane!!'' AB'ILAL ya karashe mgnr murya da kwayar idonsa cike da tsantsar kishi da kiyayyar Alhaji, mgnganun nasa ma besan ta ina suke fito wa ba. Alhaji ibrahim ya kuresa da ido yana me hango kishi a kwayar idonsa, se yanzu ya kula d hkn. "To ko matarsa ce, ko budurwarsa, ya tambayi knsa d knsa. Nan take zuciarsa ta basa sede matarsa. dan hk jikinsa yy sanyi, ya fara mgna da laushin murya. "Am very sorry bnsan cewa matarka bace, wlhy nasha budurwa ce...." AB'ILAL yaja kwafa kawai se faman tiriri yakeyi yana hajijiyar matsifa yaso ace alhajin ya masa wata mgnr bnza wlhy da sede a kwasheshi a sume. Kwafa yaja a karo na biyu ya kalli alhaji ibrhim a wulaknce kana ya juya ya koma motarshi alhaji ya juya shima ya koma motarsa jiki a sanyaye a gaskia ya kamu da sonta a gani na farko, yasan da wuya ya hkra da ita a nan kusa sbda y kamu da tsamanin sonta. AB'ILAL na shiga motar ya figeta da tsiya, aka bude masa get ya fice a guje kmr ze bige masu gadin ya daura motar a kn titi ya hau sharara gudu kai daganin yadda yake tukin zakasan cewa a hasale yake ko kallon inda take beyi ba sbda haushi take basa, be taba sanin iskncinta yakai hk ba se yau, driving yakeyi amma kuma takaici na cinsa inside ..... Kasa da knta tayi har lokacin jikinta na rawa, ganin yadda yake gudu da ita a motar ma seya kara mata tsoro gani takeyi kmr niyar kashesu ma yakeyi, ta kulle murfin idanuwanta tsoro da firgice na cin zuciarta. Har suka isa gidan be juyo ya kalleta ba itama bata kallesa ba sbda duk a tsorace take. Suna isa gidan ko gama packing beyi ba ta bude murfin motar ta fita, ta nufa falon Amihh a guje kai kace biyota akayi, sukayi kicibus da Salwah a tsakiyar falon Amihh, suka zube a kn 3ct salwah data firgita da ganin hilwah a firgice ta shiga tambayarta meya faru hilwah tace mata bakomi kawai, tanata faman haki , salwah ta kara tambayarta meya faru, tace mata ba komi, salwah taki yadda da hkn, ta nace mata da tambaya dole hilwah ta sanar da ita kawai sun kusa yin accident ne a hnyar daaowa, salwah ta mata Allah ya kyauta ita a fari ma tasha ab'ilal ne ya mata wani abu.... Fitowa yayi bayan ya gama packing motar zucia fal takaici har ynzu tiriri zuciarsa keyi, hannunsa riqe da car key dinsa ya nufa side dinsa, a falonsa ya yada zango a kn 3ct yana mejin kmr ze mutu se ynzu yake nadama dayabar mutuminnan dabe kai masa hannu ba ta yadda 44 ma bazasu amsheshi ba, ya zagi mutumin yafi sau dari biyu a zuciarsa. "Meyasa kakejin hkn a kn karuwa?'' Wani bangare na zuciarsa ta masa wannan tambayar, dogon tsuki yaja hadi da rintse kwayar idonsa, ya juya ya kwanta kwanciar gefe akasin da dayake kwance yana me kallon sama. Yasan kirayyar yarinyar ce tasashi jin wannan mugun yanayin a ransa, a lokacin ji yayi kmr ya rufeta da duka dan yafi ganin lefinta a kn mutumin, bacin rai ya hanashi mata mgna, da gudun raini,,juyi yashigayi a kn kujerar kmr zuciarsa zata fito waje ta fashe dan takaici ga yunwa na cin cikinsa amma beji takaicin da yarinyar ta kunsa masa ya hana yaji yunwar dake cikin nasa....ranar hk ya kasamce beci abinci ba seda daddare. Dayazo bacci da bacin ran hilwah ya kwana dadin dadawa kuma ga sha'awar nono, musammanma yau daya kara ganinta se hnklinsa ya kara tashi, bura kuwa bata rankwafa ba har washe gari....
Bayan kwana biyar hilwah ta kara samun jikinta sosai har yar kiba tayi tana nan side din Amihh tana bata kulawa sosai. Yau Amihh tace ta koma side dinta tinda ta samu sauki sosai, sam hilwah bataso hknba hk de ta koma can din zucia ba ddh, sam bata bari sun hadu da Ab'ilal ba, tinda ta kule a daki ko falo bata fitowa, hilwah bata mnta da warning din AB'ILAL. Har ynzu a kasan carpet take kwana shima a tsorace, salwah ke kawo mata abnci har tayi 2 days a side din basu hadu ba, rabonta dashi tin rnr daya kaita asibiti, hk shima rabonshi da ita tin rnr daya kaita asibitin a 2 days dinnan yayi busy sosai kullum seya fita ma'aikatarsa dake nan garin kadunar, gashi sun bude wani sabon company na saida motoci na alfarma dan hk se yy busy sosai. Da safe de kullum kafin ya fita se yaje ya gaida Amihh takan amsa ba yabo ba fallasa, sam batabi ta knsa ba kn bacin ran daya kunsa mata rnr daze kawo hilwah asibitin, tasan ze kuma wani iskncin seta hada taci ubansa a lokacin.. Tinda Hilwah ta dawo side din kullum se tayi aikace aikacen daya zamana nata na gidan, ko rana daya bata taba tsallakewa ba, tin bata saba ba harma ta dan fara sabawa, a bangaren gyara nasa dakin kuwa Se ta faki idonsa in benan kmr lokacin azahar da la'asar hk tasan yana zuwa masallaci, shine take shiga ta gyara masa shape shape ta fito, har wanki take masa, ta gyara masa komi tsaf. sede in gogan ya dawo yaga an gyara masa ko ina sannan ga kamshin jikinta da zuwa ynzu ya riga daya gama kama masa daki, ba krmin jin dadin kamshin nata yakeyiba, hkn ba karamin kara tada masa sha'awah yakeyi ba , daman ya lafiar kura, be bacci har ynzu kullum bura a mike, se da kyar yake bacci shima se zuwa bayan asubahi.
Amihh tayi ciku cikun sa hilwah a mkrntar su salwah, ta zaba mata irin cos din da salwah ke karanta ba tare da tayi shawara da ita ba, sosai hilwah taji dadin cos din da Amihh ta zabar mata na krtun likitanci. Rnr monday hilwah ta fara zuwa makarantarta ita da salwah komi na bukatuwwa Amihh ta mata, tase mata dogayen riguna kusan kaloli arba'in marasa nauyi wadanda zata rinka sakawa zuwa mkrntar, danta kula batason kaya masu nauyi sbda duk kayan da AB'ILAL ya mata bata sa ko daya ba a ciki sbda bata ma iya sasu ba. A sati daya data fara zuwa mkrntar mlmn suka yaba da kokarinta ai tini ta samu shiga a gun malamai da wasu dalibn mkrntar hadda wadanda ta fisu aji sosai, amma sam bata sakewa da maza sbda Amihh ta mata fada kn ta riqe mutumcinta tinda tabada Aure. Duk wainar nan da ake toyawa Sam AB'ILAL besan ma meke faruwa ba, kwanansa goma a garin kaduna, aiki ya taso masa zuwa garin kano ya nemi izinin Amihh tayi masa fatan dawowa lafia yaji dadin hkn , ya nufa garin kanon cikin jin Dadin zucia sbda adduarh mahaifiyyarsa garesa, har ya tafi bega fuskarta ba, yana cike da bukatuwar ganin fuskarta amma sede bacin ranta be bar zuciarsa ba, na rnr daya kaita asibitin.
Ranar dasu hilwah suka dawo daga scul Amihh ke sanar da hilwah mijinta ya koma kano, ba karamin jin dadin hkn hilwah tayi ba, ta dawo side din amihh da kwana zuwa kafin AB'ILAL din ya dawo a cewar Amihh. Sosai amihh ta matsa gun koyawa hilwah girki a kiching kullum tare suke shiga kiching abincin dare ko weekend haka to rnr daga safe har dare basa zama, musammanma a yan kwanakinnan dasuke yawanyin baki, daga gidan Alhaji babba harshi alhaji babban ma yazo yaga hilwah ya yaba da kyaunta, se sakin zance yakeyi a gabanta, hilwah ta Tashi ta bar falon a kunyace. Hajia maryam ta girgiza kai kawai tasan Halin nasu alhajin a jini yake. A yau hajiya juwairiyya tazo garin kaduna, amihh ta mata tarba ta alheri abinci kusan kaloli biyar suka shiryawa hajiya Juwairriyya taci tasha, hirar yaushe gamo ta tsinke tsakaninsu da Aminiarta Hajiya maryam. Hilwah da salwah sukazo suka gaidata sbda dataso basunan 12:am suka bar gidan zuwa mkrntarsu amma dasu aka shirya mata abinci. nan Hajiya Juwairriyya taga hilwah aiko ta yaba da kyanta, bayan sun gaidata har sun koma cikin dakin salwah hajiya Juwairriyya ta juyo ta kalli aminiarta hajiya maryan wadda keta faman sakar mata murmushi tace "kai Aminiata, wannan shimfidediyya haka, ah dole fa ki gigice ki hada Auren nan, wannan ai kyakyawan iri ce yarinya ga kyau ga ladabi da biyayya gata kyakyawa ALLAH sarki..." Hajiya maryam tayi Murmushi zucia fal jin dadin yadda hajiya juwairiyya ke yabon hilwah taji dadin hakan sosai. "Kede bari hajiya gata nan fa tubar kallah....''cewar Amihh. Hajiya juwairiyya ta amshe da ''gaskia kam masha Allah komi yaji tako ina fam fam...." Hajiya maryam ta dan jefe hajiya da kallon kunya tace "kai hajiya wai fam fam....'' Hajiya juwairiyya tace "E mna kiga yarinya tako ina ya cika,....ko cikine da ita?'' Hajiya Maryam tayi yar Dariya tana tunawa da haka hajiya karama ma tace datazo waiko ciki ne da ita. "Hajiya wai baku gane me ciki ne? Wannan ma yaushe dannaku ya kusanceta balle tayi cikin..." Fuska dauke da rashin fahimta Hajiya Juwairriyya tace "kmrya be kusanceta ba? Kina nufin basu tare tarayyar Aure ba?'' Hajiya maryam ta daga mata kai alamar tabbatarwa. Hajiya Juwairriyya tace "kai haba de! Hajiya ke ina zaki sani, tinda de abu ne na sirri ba ganewa zakiyi ba, kila sunyi abunsu baki sani ba, ALLAH na tuba Yaushe zega wannan abubuwan ya gyale se kace ba namiji ba.... " Hajiya maryam dake sauraren hajiya juwairiyya ta amshe da "to inajin de ba namijin bane, domin kuwwa xan iya rantsewa be kusanci yarinyarnan ba, abinda ma dakunansu daban daban suke kwana, mutumin da duk yabi ya tsangwameta ya takura mata, Hajiya ta ina za ayi tarayyar Aure, wai sekace kin mnta halin yaronnan na taurin kai..." Hajiya Juwairriyya tayi jim kana tace "Haka ne hajiya, Amma ni naga yarinyar ai bata da makusa ,,,gaskia made da lefinki anfa juma dayin auren nan, to ki maidata dakinsa mna tinda de Matarsa ce halalinsa ce hajiya ba amfanin kwanan da sukeyi a rarrabe...'' Hajiya maryam tayi shiru tana me nazarin maganganun hajiya juwairiyya, tabbas mgnrta tayi kuma ta dace. "To shikenan hajiya aiko kn kawo shawara hkn za ayi,,,," hajiya juwairiyya tace "ai hkn yafi hajiya, wata rana ko ba aso dole za a kusanci juna....'' Hajiya maryam tace "gaskia ne kam Hajiya, Allah de ya tabbatar mna da Alheri,.." Hajiya Juwairriyya ta amsa da "ameen de hajia,... Gaskia AB'ILAL wani irin mutum ne, Allah na tuba da irin yaran nan ne Alhasan inajin da tin ranar da kika kai masa yarinyar nan side dinsa ze daddanne yar mutane..." Hajiya maryam ta zaro ido tace "kai hajiya karkiwa dana sharri..." Hajiya Juwairriyya tace "wlhy knji