Showing 12001 words to 15000 words out of 142497 words
Chapter 5 - NI DA YAYA SADAM Complete Document by Binta Umar Abbale.txt
data bukata a lokacin tana raye a duniya yake mata......Sulaiman shima yaji mutuwar sosai tare suka dinga jajantawa junansu.
Sulaiman na ganin Sayyada yaji wani tausayi da sonta a zuciyarsa duk girmanta haka yake daukar ta su fita yayi mata siyayyar cizi biskit alawa iri-iri Sayyada ta zauna tana shan abunta bata da wata damuwa saboda da kuruciya a tare da ita a lokacin.
Sadam! kam ido ne nasa sam baya tanka musu watarana dai idan yaga abin yayi yawa sai ya daka mata tsawa idan tana wani shirman ita kuma sai ta fashe da kuka da ruga gurin Sulaiman tana fad'a masa shi kuma a lokacin ne zaka ga 'bacin ransa....Sadam! haushi da takaici ya sanya ya bar gurin sam a ganinsa abunda Sulaiman din yake wa yarinyar bai dace ba zata sangarce ta lalace duk girmanta sai ya dorata a cinya ko ya sa'bata a kafad'a ya fita da ita yana mata kiss a kumatu takaici kamar ya kashe shi.....Sai da sukayi fad'a kaca-kaca da Sulaiman din amma bai daina ba da karshe kawai sai ya daina kulashi gabad'aya to da yake Sulaiman din yafi shi saukin kai shine yake masa magana wani sa'in.
Bayan sadakar bakwai suka shirya tafiya.....Sayyada ta dinga gursheken kuka kamar ranta zai fita Alhaji Auwal yace." A had'a kayanta xai tafi da ita Baba Ladidi tayi tsalle ta dire tace"Bata yarda ba....Sulaiman ya dinga lallabata har da yi mata alkawari zai kaita umara tace"In dai sai ta basu Sayyada zai kaita Umara to bata so.
Sadam!!! 'bacin rai bai barshi yace komai ba shi dai ya zuba musu ido kawai sai da yaga iskancin Sayyadar yayi yawa sannan ya zare blet ya nufe ta yana zare ido......Ta ruga bayan Sulaiman tana kuka shi kuwa Sulaiman hararasa kawai yake yana fad'in"Wallahi ka dake ta da wannan blet din sai na rama mata mutum sai 'bakar zuciya kawai kai koma naka babu imani ka tausaya mata mana."!
Tsaki! Yaja ya maida blet dinsa ya daura a gu'kunsa ya koma ya tsaya shaye da toka sai wani cin magani yake duk suna kallo Sulaiman din ya sa'bata a kafad'a ya fita da ita sunfi 'karfin rabin awa basu dawo ba Sadam!!! sai tsaki yake yana kallon agogo an kira wayarshi ya kai sau biyar ana jiransu a bracck dinsu akwai sabbin sojojin da zasu horar dasu.
Mahaukaciyar siyayya Sulaiman yayi mata ta kayan zako iri iri Ya jibge baba ladidi ta cika da mamaki shi kuma yace."Ko idan sun kare ayi masa waya a sanar masa zai turo kudi." Baba Marka tace"Wannan ai ka siyo mata kayan ciwo haba ai abun yayi yawa za'ki ai ba abun sha bane."
Yace."Baba komai Sayyada take so zanyi mata tausayi take bani." Tace."To dai banda irin wannan siyayyar ta cutarwa kasan halinta yanzu sai ta'ki cin abinci ta dimanci shan alawa da madara.
Alhaji Auwal yace."Sai a kwashe kayan a dinga bata da kad'an-kad'an! Sadam!! yace."Nima dai abinda na gani kenan idan kun tara mata kayan za'ki taci ta sha to ku shirya da sanin cewar zata dame ku da kukan ciwon ciki."!
*To wannan shine tushen labari*
Page na gaba zamu dawo ainihin labari
NI DA YAYA SADAM
NA
BINTA UMAR ABBALE
9
*Cigaban Labari*
To haka Sayyada ta cigaba da rayuwa a hannun Baba Ladidi tare da kulawar 'bangarori daban daban mahaifinta ma yana iya bakin kokarinsa akanta sai da da yayi aure ne matar da ya aura ta janye masa hankali daga kan Sayyada ya daina kulawa da ita sosai Sayyada sam! bata sha'ku da bangaran mahaifinta ba tafi shakuwa da bangaran mahaifiyar ta shiyasa ba sosai take zuwa can gidan maigarin ba sai Baba Ladidi ta takura mata sannan take zuwa Juma'a Juma'a, shima idan taje bata wani zaman arziki take dawowa gida a cewarta baza ta zauna Hansatu tana yi mata kallon banza ba domin sun sha fad'a sosai da ita da matar baban nata mai suna Hansatu.
Sayyada yanzu haka tana aji shida a karamar makaranta suna dab da jarrabawa makarantar isilamiyya kuwa sun hada izifi ashirin to babu laifi tana gane karatu amma Amina ta fita kokari, kun san dai kowa da irin baiwar da Allah yayi masa.
*****
Karfe uku shaura na rana tana zaune da kwanon abinci a gabanta hijab ne a jikinta kalar ruwan toka gefanta jakar makarantar isilamiyya ce Amina ce tayi sallama ta shigo
Ta gaishe da baba Ladi dake bakin rijiya tana wanke kwanoni kai tsaye ciki ta shige itama ta shirya tsaf da shirin tafiya makaranta.
"Sayyada baki gama cin abincin ba kenan? duba lokaci ya kure da yawa kin san dai yau malam Bashir ne zai shigo ajinmu ko."?
" Yi tafiyar ki malama kar ki dame ni! sai me idan malam Bashir ne zai shigo sai a ka fad'a miki tsoronsa nake."!
Amina jikinta yayi sanyi tace"Kin san dai ko zai barki ki kishiga aji sai ya doke ki da wannan bulalar mai zafi shine abinda nake guje mana."
"To me ya dame ki? kinga nifa bance dole sai na tafi dake ba tafiyar ki daban tawa daban mtwss!
Baba Marka ta daga labule ta fito tana fad'in" Surutun me nake ji Amina."!?
Amina data sha'ka da yawa tace"Baba Wai daga nace mata tazo mu tafi makaranta kar mu makara shine take fad'a min magana."
Baba Marka tace"To bakya ganin abinci take ci ne."
Amina tace"Ai dama cewa nayi tayi sauri baba."
Marka tace"Ke Sayyada maxa ki gama ku tafi karku makara." Sayyada tayi musu shiru tana cin abincinta haushin Amina takeji sosai kuma tayi al'kawarin sai ta kunyata a gaban 'kawayensu na makaranta.
Tana gama cin abincin ta mike ta wanke hannunta jakarta ta dauka ba tare tace Amina komai ba ta kama hanyar fita....Amina tabi bayanta tana fadin"Sai mu dawo." Baba Ladidi tace"To Allah ya bada sa'a."
Ko a hanya ma Sayyada 'kin kula Amina tayi har suka isa makaranta Sayyada ta tsallake can gurin 'kawayenta itama Amina ta zauna gurin 'kawayenta dama gurin zaman Amina a gaba yake ita kuma Sayyada can baya take zama tare da manyan 'yan matan da suka girme ta nesa ba kusa ba suyi ta zancan aure sam basa gane karatu sai maganar aure da hirar samari Sai lokacin jarrabawa yayi idonsu ya raina fata Sayyada ce kawai mai 'kokarin cikinsu ita ke basu amsa ko kuma idan ta rubuta ta basu su kwafa shiyasa suke tsoronta komai tace dai-dai ne."
Sai bayan malam bashir ya fita ne kafin wani malamin ya shigo Sayyada ta kallesu tace "Kun san menene."!? Suka ce sai ki fad'a." Tace"Wallahi na tsani Amina muguwar munafuka ce." Sadiya tace"Ke Sayyada ke da 'yar uwarki kuma me tayi miki."?
Tace"Humm! wai saurayina ko kuma nace mijin da zan aura shi take so har da wani shishshige masa shi kuma har da sa mata zobe bayan fa tasan da al'kawari a tsakaninmu dashi."
Ummi tace"Lallai Amina bata da kunya wallahi to ke wane mataki kika dauka."!?
Sayyada tace"Ku taso muje inda take." babu musu suka mike suka isa inda Amina ke zaune da kawayenta suna bitar karatu.
Aminta taji magana a kanta "Ke Amina ciro wannan zoben dake hannunki."! Sayyada ce me wannan maganar tasha kunu.
Amina ta dago kai tana kallonsu tace" Kamar Yaya na ciro zobe me ya shafeki dashi."
Ummi tace"Lallai Amina baki da kunya au! tambayar ta ma kike meye ruwanta bayan kinsan zoben hannun Saurayinta ne ai tana da iko dashi."
Amina ta mayar da kai kasa tana karatu Sadiya tace"Wallahi tun muna shaida juna dake ki ciro mata zobenta ai itace tafi dacewa dashi tunda ita zai aura amma saboda tsabar shishshigi kin wani shigewa saurayinta wai don ya aure ki mun gane abinda kike nufi."
Daya daga cikin kawayen Amina tace"A gaskiya wannan abinda kukeyi bai dace ba ina ruwanku da Amina ni dai tunda na shigo banga ta shiga sabgarku ba."
"Dallah malama rufe mana baki banza 'kazama wacce bata waye ba ke idan ke akaiwa haka zakiji dadi? Mijina fa taje tana cusa kanta a gurinsa har sai da ya sa mata zoben da yayi niyar saka min wallahi sai ta cire zoben nan ko kuma ta raina kanta."!Sayyada ce ke wannan maganar tana girgixa jiki....Ai kafin kice komai 'yan ajin sun lullu'be su suna son jin 'karin bayani ita kuwa Ummi 'kawar Sayyada sai fad'a musu take Amina munafukace me 'kwacen saurayi don haka kowa yayi taka tsantsar da saurayinsa.......Aikuwa sai aka fara surutai kowa na fad'in albarkacin bakinsa.
Amina 'bakin ciki ya sanya ta fashe da kuka idanu jage-jage da hawaye take kallon Sayyada tace" Yanzu ni kika tozarta a bainar jama'a Sayyada nifa 'yar uwarki ce."!
"Oho! wannan ke ya shafa ni dai nace a ciro min zobe ko kuma yanzu jiki yayi tsami wallahi."!
Amina tace" Wallahi bazan cire zoben nan ba tunda ai bake kika saka min ba sai ki bari idan wanda ya saka min zoben yazo sai ki saka shi ya cire min da kansa."
Sayyada tayi wani juyi had'e da buga tsalle! sai ta cafki wuyan Amina ta sha'ke cikin hijab tana fad'in"Wallahi sai kin cire min zobe banza shashasha me 'kawacen saurayi."
Amina da Sayyada kokawa suke sosai da sosai Sayyada duk ta ya kushe mata fuska sai 'kwa'kule mata hannu take tana murd'ewa wai dole sai ta cire zoben ita kuma Amina ta dunkule hannunta.
'Yan aji kuwa sai Ihu! suke suna dariya da fad'in"Wallahi babu wanda zai rabaku ku casu ai 'yan gida d'aya ne."
Mariya 'kawar Amina ita ce ta nufi ofis d'in malamai domin ta fad'a musu halin da ake ciki sai suka ci karo da Malam Bashir ya fito daga ofis yana kokarin shiga wani aji tace"Malam Bashir ana fad'a a ajinmu.'' Yace."Waye da waye."!? Tace"Amina ne da Sayyada. Kai tsaye a jin ya nufa da zabgegiyar bulalar sa.
Har yanzu kokawar suke Sayyada ta kusa ciro zoben Taji saukar bulala a bayanta ko a jikinta sai da ta ciro zoben sannan hankalinta ya kwanta ta saki wuyan Amina tana nishi! Amina ta mike zaune sai kuka take ga Sayyada duk ta ji mata ciwo da yakushi.....Malam Bashir yace."Ku same ni a ofis."
Yana fita Sayyada ta mi'kawa Ummi zoben tace"Ri'ke min wallahi komai za'ayi ba zan bayar ba."
Ta kama hanyar fita Amina ta mike da jiki a sanyaye tabi bayanta duk 'yan ajin suka bita da kallo Amina ta tsargi kanta sai rufe fuska takeyi kamar wacce tayi abun kunya.
Suna isa ofis din suka tarar da Malam Bashiri na zaune kan kujera da wayarsa a hannunsa yace."Ku tsuguna ko wacce ta d'aga hannu sama."
Babu musu sukayi abinda ya saka su sai da sukayi minti goma shabiyar a haka sannan yace."Ku sauke hannunku." Suka sauke Sayyada ya kalla yace."Daka gani kece mara gaskiya bari na fara jin ta bakin ki me ya had'aku fad'a."!?
Sayyada ta soma inda inda" Malam nifa d dama ita k.....A gida bama shiri da juna kuma munafuka ce ita."
Malm Bashir yace."Ni ba wannan na tambaye ki ba ina so ki fad'a min ma'kasudin fad'anku." Shiru tayi ya girgiza kai yace."Ko anan ma alamu sun nuna kece mara gaskiya Sayyada nagaji da halin ki yanzu yanzu zan kira Sadam! a waya in sanar masa da abinda kikeyi a makarantar nan."
Sayyada gabanta ya yanke ya fad'i jin abinda yace sai tace"Nifa malam wallahi ba laifina bane itace ta shiga gona ta."
Malam Bashir ya kalli Amina yace."Amina ke fada min abinda ya hadaku fada kafin na yanke hukunci."
Amina ta warwarewa Malam Bashir duk abinda ya faru tsakaninta da Sadam! da yanda akayi yasa sanya mata zoben hannunsa.
Malam Bashir yace."Sayyada kece mara gaskiya don haka a kanki zan dauki mataki ina ruwanki da zoben hannunta tunda dai ba ke kika saka mata ba ko kuma ance miki shi Sadam! din idan ya aure ki dake kad'ai zai zauna to ki shiga hankalin ki wallahi."Sayyada ta kama 'kunkuni hawaye na kokarin zubo mata....Malam Bashir ya fara neman numbar wayar Sadam sai da ya kira sau uku sannan ya dauka hands free ya bude duk suna jin muryarsa suka gaisa da malam bashir din wanda dama tun asali sun san juna abokan juna ne saboda duk lokacin da Sadam! din ya shigo garin a majalisarsu yake zama.
Mlm Bashir ya fad'a masa dukanin abinda ke faruwa tare da fad'a masa hukumcin da ya yanke a kan Sayyada zai korata gida ta zauna sai bayan sati biyu ta dawo."
Sadam! Yace."Yanzu ina Sayyadar take."? Malam bashir yace."Duk gasunan a kusa dani." Yace."okey bata wayar zanyi magana da ita." Sayyada najin haka sai gabanta ya fad'i! da sauri ta aro dauriya da jarumta ta kar'bi wayar da malam Bashir din ke mi'ka mata.
_Afuwa bani da change sosai kuyi manege_
31/5/2020
*BINTA UMAR ABBALE*
NI DA YAYA SADAM
BINTA UMAR ABBALE
10
Dakakkiyar muryarsa mai cike da amo taji yana fad'in"Ina Sayyada."!? Baki na rawa tace"Gani." Yace."Wai ke me yake damun kwakwalwar ki ne? don Ubanki! ni da kaina kinji nace zan aure ki da har kike tozarta 'yar uwarki a kaina! ni me zanci dake ai idan aure zanyi Aminar zan aura tunda tafi ki komai da komai.....Tayi saurin katse shi ta hanyar fad'in"Ni wallahi Amina bata fini komai da komai ba."! Yace."Ni nake magana kina katseni wato nima zakiyi min rashin kunyar ko."? Shiru tayi bacin rai da bakin ciki yayi mata yawa, yace."Tun muna shaida juna dake ki cire zobe nan ki bata ai ina sane dake ban baki ba saboda ba ki dace dashi ba sai ita kuma wallahi kinji na rantse kada wata magana ta sake biyo bayan wannan a tsakanin ki da Amina idan kika kuskura nazo garin akace ga wani abu da kika sakeyi makamancin wannan to dama kin san sauran sai jikin ki ya fad'a miki kinji ko baki ji ba."!? Ba tare da ta amsa ba masa ta kashe wayar....Cike da mamaki! ya bi wayarsa da kallo wato yarinyar shi ta kashewa waya ashe haukan banza yake ba sauraransa take ba lallai Sayyada wuyanta ya isa yanka.
Kiran wayar ya sake yi sai tayi saurin mi'kawa Malam Bashir wayar ya dauka tana jin sanda yake cewa malam Bashir din duk sanda ta sakeyin wani abu ya sanar dashi zai zo da kansa ya dauki mataki a kanta.
Sukayi sallama da juna malam bashir ya kashe wayar sannan ya Umarci Sayyada da ta mayar wa da Amina zobenta tana zum'bura baki tace"Zoben baya hannunta tunda ta cire a cikin aji ta neme shi ta rasa. Malam Bashir dai yasan karya take saboda kar yaja maganar tayi tsaho yasa yace su koma aji Sayyada ta duba ko ina mutukar bata ga zoben nan ba to sai ya zaneta.
To koda suka koma aji bata sauya zani ba don Sayyada habaici ta dinga yiwa Amina tana fad'in "Duk abunda xa'ayi sai dai ayi amma ba xata bada zobe ba.
Ita dai Amina bata ce mata komai ba ta zauna cikin kawayen ta kunya duk ta isheta ganin irin kallon da wasu suke mata.
*****
To haka suka cigaba da rayuwa tsakanin Sayyada da Amina babu jituwa kullum fad'a kuma Sayyadar ce ke takalo fad'an har ta kai ta kawo suka daina kula junansu saboda Sadam! wanda shi da suke abun dominsa ma bai san sunayi ba.
" Oyoyo Yayana" Oyoyo sannu da zuwa." Sayyada ke wannan ihun tana tsalle tun sanda taji Sallamar Sulaiman a 'kofar su da gudu taje ta rike hannunsa shi kuma ya dan rungume kafad'anta fuskarsa dauke da murmushi wanda ya kara masa kyau da kwarjini yana mata wani irin kallo yace."Babyna kece kika girma haka.'"! Cikin kunya ta rufe fuskarta tana kokarin kar'bar jakar kayansa....Murmushi ya saki yana d'an shafa siririn sajen sa yace."Masha Allah babu shakka Baba Ladi ta iya raino akwai gwaggwa'bar kyautar da zanyi mata." Baba Marka ta d'aga labule ta fito daga d'aki tana fad'in"Murya wa nake ji ne kamar ta soja." Da Sulaiman tayi tozali tace."Au! ashe bature ne to sannu da zuwa lallai yau za'ayi ruwa da 'kankara *Dabi* tana da babban 'bako." Sulaiman yace."Kwarai kuwa baba yau naso nayi suprise d'in ku ne shiyasa kawai kuka gani ba tare da kunyi tsammani ba." Baba Marka na shimfid'a masa sabuwar tabarma tace"Aikuwa dai munyi mamaki kwarai da alama ma zaka kwana biyu a garin tunda na ganka har da guzirin kaya." Yace."Zanyi sati biyu insha Allahu kafin in koma, wai ina d'aya matar tawa ne."!? Yana nufin Baba Ladidi Sayyada tace"Yanzu yanzu ta tafi sabuwar kasuwa, amma dai nasan yanzu zata dawo."
Yace."Okey. Baba Marka tace"Bari in dama maka fura kafin a d'ora abinci." Yace."Nagode Baba sosai nayi kewar wannan furar taku mai dad'in gaske." tana dariya ta mike ta shiga daki....Sulaiman ya tsirawa Sayyada ido yana kallonta sosai yake masifar son yarinyar a cikin ranshi yana ganin idan da babu maganar aure a tsakaninta da 'kaninsa da babu abinda zai hanashi auranta sonta ya riga ya zama jinin jikinsa.
Rife fuskar ta tayi tana murmushi tace"Wayyo Yayana wai na sauya maka ne naga sai kallona kake tun da kazo." Ya saki murmushi mai kyatarwa yace."Sosai kika sauya min Sayyada kin girma kin zama cikakkiyar mace alhamdullahi ina rokon Ubangiji ya baki miji nagari wanda zai kula dake."
Murmushi kawai tayi tace "Yayana ina auntyna." Yace."Tana nan lafiya lau da da tare zamu zo to saboda yanayin jikinta ne ya sanya nace ta bari sai ta haihu sai na kawo ta ta kwana biyu tare daku."
"Wayyo Allah ashe auny Luba ta kusa haihuwa kai gaskiya naji dad'i wallahi Allah ya sauke ta lafiya." Yace."Ameeen ya rabbi Sayyada ya karatu ina fatan kina mai da hankali ko." ? Tace"Eh Munayi yayana A dai taya mu da addua."Yace."Idan kina so in tafi dake can kaduna mana sai ki cigaba da karatun ki a can ni sai nake gani kamar bakya mai da hankali anan." Jiki a sanyaye tace"Wallahi ina karatu Sosai Sai dai kasan makarantun cikin birni da irin namu ba d'aya bane amma nima ina ganewa sosai." Yace."Okey zanzu kuna jiran jarrabawa ta fito kenan." Tace"Eh kuma isilamiyya ma mun had'a izifi ar'bain." Yace."Alhamdullahi to kafin in koma za muyi karatu ni dake sai in gani shin da gaske kike kina fahinta ko kuwa." dariya tasa tace"Tom ai kuwa zan baka mamaki."! Mikewa tayi tace"To bari dai in dora maka abinci ko." murmushi yayi ya bita da kallo yana ayyana abubuwa da dama a kanta.
Baba Ladidi ta shigo da daurin buhu a hannunta wani a kanta tana