Showing 9001 words to 12000 words out of 142497 words
Chapter 4 - NI DA YAYA SADAM Complete Document by Binta Umar Abbale.txt
a tsakar gida da yake lokacin zafi ne nan suke kwanciya sai asubah suke komawa d'akunansu, kai tsaye daki ta shiga domin dauko bargon da take kwanciya taji masifar dadi da Sadam! ya ga Talle suna zance yasan itama ba samari ta rasa.
Tana fitowa daga dakin suka ci karo dashi ya shigo sai tayi saurin komawa da baya gabanta na faduwa ta dauka ai yayi tafiyarsa.
Cikin uwar dakin ta shiga ya bita sai ta soma ta'be fuska zatayi kuka ya daka mata wata iriyar tsawa! shiru tayi tana kallonsa.
"Wallahi duk sanda na kara ganinki a tsaye da wannan 'kazamin sai ranki ya 'baci ke ki rasa wanda zaki tsaya dashi sai wannan shashashan mai warin d'auda."!
" To ina ruwanka dashi ni shi naga ni kuma shi nake so."!
Mari ya kai mata ta kauce! da sauri ta tsorata da ganin yanayinsa.
Yace."Saboda baki da kunya ina miki magana kina mayar min kin raina ni ko."!?
Da karfi ya fadi maganar.
Shiru tayi yace."To ki kuskura na gani ko naji labarin kin sake tsayawa dashi wallahi sai na dauki mataki mai tsauri a kanki zan sanya matakan tsaro sosai a kanki."
Tana kuka tace"Wai kai ina ruwanka ne? kaine fa kace ba zaka aure ni ba sai kuma ka hanani kula Samarina ai ba zai yiwu b......Ya kaiwa bakinta duka da sauri ta rufe da hannunta ya daki hannun ta sake fashewa da kuka mai karfi wanda yayi sanadiyar tashin Baba Ladi daga bacci....."Ke! Sayyada menene kina ina ne."!? baba ladidi ke wannan maganar tana haska karamar toch inda sayyada ke kwanciya sai taga gurin wayam! tana kokarin mikewa Sayyadar ta fito daga d'akin a guje bayanta ta 'buya tana kuka Ya fito daga dakin yana wani irin huci! na bacin rai!
Baba Ladidi ta haske shi da fitila tace"Wai menene? Bafa nasan neman fitina me tayi maka."?
Yace."Baba kina kwance da kina bacci yarinyar nan ta fita da daddare tana zance da wani d'an iskan yaro kazami! duba time goma na dare har ta wuce."
Baba ta kalli Sayyada dake tsaye tace"Wato da kikaga nayi bacci shine kika fita zance ko wai ke Sayyada me yasa bakya jin magana ne."!?
Tana kuka tace"To Baba ai ba laifi nayi ba shima yana zance da wata kuma ai har yanzu bai tabbatar muku da cewar zai aure ni ba to kawai sai a hanani inyi zance."
Baba Marka dake kwance ta mike zaune tana fad'in" Yanzu ke Sayyada me zaki ci da wannan yaron Talle bai aje ba bai bawa kowa ajiya ba haba kiyiwa kanki fad'a mana, koda Sadam! bai aure ki ba Talle ba sa'an auranki bane saboda duk gari kowa yasan ba yaron arziki bane ko ya aure ki ba zaki samu kyakkyawar kulawar da muke so ba."
"To ni dai shi nake so A kyaleni kawai." Tafada tana goge fuska....Sadam! yace."Shikkenan Baba ku rabu da ita tunda shi take so sai a daura mata aure dashi ni idan Allah ya kaimu gobe kafin in wuce zan samu iyayensa sai a tsayar da magana."
Sayyada gabanta ya yanke ya fad'i!!!! da jin abinda yace cikin zuciyarta tace "Allah yasa ba da gaske yake ba lokaci kankani jikinta yayi sanyi.
Baba Ladidi tace" Shikkenan ni na cire bakina daga wannan sabgar tunda dai kin nuna mana cewar kin fi son ki auri Tallen shikkenan, kai Sadam! idan Allah ya kaimu gobe da wurwuri sai kuje da Kawunka ku fara maganar auran Allah ya za'ba abinda yafi alkairi."
Ya kama hanya futa Baba Marka tace"Yau ba anan zaka kwana bane."!? Yace."Eh can sashen Kawu Tanko zan kwana." Tace"To Allah ya tashemu lafiya." Ba tare da ya amsa ba ya fita.
Sayyada tayi tsuru a zaune Baba Ladidi da Baba Marka suka gyara kwanciyarsu ko wacce ta cigaba da baccin ta suka bar Sayyada da tunanin ya zatayi ta fitar da kanta.
Juyi kawai takeyi ta kasa bacci ga gari yayi duhu sosai kowa yayi bacci da alama ma sha biyu ta wuce sai dai karfe daya kuma, mi'kewa tayi a hankali ta lalla'ba ta fice kai tsaye 'kofar Kawu Tanko ta nufa......Shiru kowa yayi bacci ta lalla'ba ta nufi dakin da take tunanin yana ciki aikuwa takalmanshi ta gani kofar a bud'e amma ya sayo ta ta tura ta shiga babu fargabar komai a tattare da ita.
Yana kwance kan katifa da wayar a hannunsa yana dubawa da alama wani abu mai muhimmanci yake dubawa yana sanye da vest fara sai gajeran wando kirjinsa da abinda yayi cinyoyinsa zuwa 'kasa wani irin gashi ne akwance da alama mutum ne shi mai gargasa a jiki ko ga yanayin sumar dake kansa zaka gane.
Da sauri ya mi'ke zaune ganinta a tsaye a kansa ya kunna hasken wayarsa yana haske fuskarta.
"Ke! Lafiya."!? yafada cikin mamaki.!
Wasa ta farayi da hannunta ta jawo jelar dankwalinta tana taunawa, haushi ya isheshi saboda yanayi na dare yasa ya taushi zuciyarsa yace." Wai ba dake nake magana ba me ya kawo ki nan."!?
Zubewa tayu gwiwa bibbiyu ta fashe da kuka!
A razane! ya mike isa inda take, tura kofar dakin yayi sannan ya dawo inda take ya mikar da ita tsaye tare da toshe mata baki da hannunsa guda, hannunta yaja suka isa bakin katifar ya zaunar da ita kusa dashi har yanzu hannunsa na rufe da bakinta ya kura mata ido yana kallo itama shi take kallo da ido yake mata magana ta gane abinda yake nufi sai tayi kokarin had'iye kukanta sai da ya tabbatar tayi shiru sannan ya bude mata baki.
A miskilance yace."Menene."!? Shiru tayi tana turo baki yace."Ke yanzu kawai sai ki shigo min daki kina kuka kawai saboda ki jawo min magana ko sharri kike so kiyi min."!?
Girgiza kai tayi, Yace."To kan wane dalilin kike kuka kuma me kike so nayi miki cikin dare kika shigo min daki."
Cikin kuka tace"Nifa ba cewa nayi kaje gidansu Talle ba na fasa auransa."
Shaf ya manta da maganar mana Yace."Wannan dalilin ne yasa kike kuka."? daga kanta tayi yace."Me yasa to ba kyajin maganar magabatanki."? Shiru tayu tare da sunkuyar da kanta
Yace."Tunda dai aure kike so to za'ayi miki insha Allahu."! Ta kalleshi da sauri! Sai ya d'aga mata girarsa guda ta mai da kanta kasa yace."Ko ina da wata magana."!?
A hankali tace."To kai ba zaka aure ni ba."! Yace."Dama ai bance zan aure ki ba su Baba ne suke maganarsu bana sha'awar auran zumunci."
Sai hawaye ya fara zubo mata ta mike tsaye shima ya mike fuskarsa a daure yace."Idan zaki daina kuka da damuwa ki daina Aure kamar anyi miki da Saurayinki anyi an gama."
Tace."To sai me? ai shima mutum ne."! kofar dakin ta bude ta fita tana kuka ranta in yayi dubu ya 'baci.!
Murmurshi yayi ya koma ya kwanta ya cigaba da abinda yake.
Washe gari ya tashi da wuri ya tashi ya shirya tsaf ya nufi sashen su Baba domin su gaisa.....Lokacin da ya isa sashen suna karya kummalo Baba Marka ta shimfida masa tabarma ta kawo masa kayan karin kummalo ya karya Baba Ladidi ta fito da mafici a hannunta ta zauna kan kujera 'yar tsuguno tana fad'in"Ashe ka shigo." Yace."Eh Baba." Gaisawa sukayi yace."Kina fiffita da safe sai kace wata mara lafiya." Tace"Aini jin zafi ne dani bana rabo da mafici Tace."Ina fatan dai kunje gidan Su Talle kunyi maganar." Yace."Sai na k'ara dawowa za muje." Tace."Ai shikkenan to Allah ya kara dawo da kai lafiya." Yace." ameen. Suna nan zaune ta fito daga dakin cikin hijan na makaranta isilamiyya ta jakar buhu a rataye a kafadarta ko kallonsa ba tayi ba tace"Baba ni na tafi."
Baba Marka tace"Kina kallon Sadam! kin wuce ba tare da gin gaishe shi ba." Banza tayi mata tayi tafiyarta."
Baba Ladi tace"Ki kyaleta kawai kina ganin ko karyawa ba tayi ba zata fita jiya ma ba tayi wani baccin arziki ba saboda an hanata soyayya da Talle."
Baba Marka tace"Ni dai banga abinda Sayyada zata ci da Wannan yaron ba."
"To ai tunda shi ta za'ba zata aura shikkenan Allah ya sanya alkairi." Sadam! na jinsu suna zancen su uffan bai ce musu ba har ya gama karyawa kana yayi musu sallama ya kama hanyar Kaduna.
29/5/2020
*BINTA UMAR ABBALE*
NI DA YAYA SADAM
NA
BINTA UMAR ABBALE
8
*Asalinsu*
Jauro mai shanu shine mahaifin Alhaji Inuwa da Kawu Tanko sai baba Indo wacce Allah yayi wa rasuwa shekaru goma da suka wuce lokacin Sayyada nada shekaru hudu a duniya yanzu in an hada duk tana da shekaru goma sha hudu a duniya.
Malam Jauro mai shanu yana da mata biyu Baba Ladidi da Baba Marka wanda rana d'aya aka d'aura masa auransu suka tare a rana daya....Shekara nayi Baba Ladidi ta haihu inda ta haifi da namiji aka sanya masa sunu Auwalu sai da Auwalu ya shekara bakwai sannan baba marka ta haihu itama namiji ta haifa Aka sanya masa suna Haruna dake sunan mahaifin Malam Jauro ne sai suke ce masa Tanko.....Bayan shekaru uku Baba Ladidi ta haifi mace Aka sanya mata Aisha suke kiranta da Indo Tsakanin Marka da Ladidi suna zaman lafiya sosai da sosai ta inda yaransu basa gane cewar wacece mahaifiyarsu a ciki zaman lafiya da kwanciyar hankali suke inda har jama'ar garin suke sha'awarsu suke kuma kwatance dasu.
Dai-dai gwargwado Auwalu da Tanko sun samu ilimin addini dana boko sai suka soma har kokin noma da kiwon shanu da sauransu dake Auwalu mutum ne mai kuzari da zafin nama sai ya yanke shawarar fita daga garin nasu neman shekarar da sukayi aikin shinkafa ya cika mota guda ta a kori kura ya nufu kasuwar kano kasuwar (dawanau) ya sauka jama'a suka rufe shi kafin kice kwabo shinkafar da ya sauka da ita ta kare kimanin buhu talatin 'yan sari duk sun siye a take ya had'o kan kudinsa ya nufo gida suka sake aikin wata shinkafar ya sake dauka ya nufi garin kaduna anan ma dai shinkafar ba tayi wani tasiri ba suka siye tas....Kafin kice kwabo likkafa ta cigaba harkoki suka budewa Auwalu ya dinga bin gari gari yana sauke musu shinkafa mai kyau suna siya.......Cikin garin kaduna ya hadu da matarsa wacce ta kasance itace uwar 'yayansa Fatsima sunanta, ko da ya sanar da iyayensa cewar ya samu matar amma ba 'yar dangi ba bace can garin Kaduna take sai suka nuna amincewarsu sukayi masa fatan alkairi ba'aja wani dogon lokaci ba aka daura aure tare da amincewar su.
Allah ya albarkaci auran kawarai da gaske Arziki da wadata suka sake suke 'karuwa shekara na zuwa duk ya biya musu kudi sukaje suka sauke farali Dashi da Mahaifinsa Jauro da kuma baba ladidi da baba marka da Indo sai da dan uwansa Tanko da matarsa, addua ta ko wane fanni Alhaji Auwal ya samu ya gina gida mai kyau da kayatuwa sannan ya dawo garinsa na gado *Dabi* ya gyara musu dai-dai gwargwado ya zube musu abubuwan more rayuwa.....Tanko shike kula da harkokinsu na noma na garin.....Shekara daya da zuwansu aikin hajji Hjy Fatsima ta haihu inda ta haifi d'a Namiji aka sanya masa suna Sulaiman.....Malam Jauro da iyalinsa suka zo suka ga jinjiri suka sanya masa albarka.
****
Auran Kawu Tanko da Baba Indo a rana daya aka daurashi Kawu Tanko auran zumunci yayi inda ya auri 'yar gidan Dantani wanda ya kasance 'kani na jini da Malam Jauro Baba Iya itace matar Kawu Tanko asalin sunanta Hamara'u
Baba Indo kuma ta auri d'an gidan Maigarin garin *Dabi* mai suna Qasimu, ta zauna a cikin gidan mai gari dake gidan mai girma ne sosai bangare guda aka ware mata a cikin gidan.
***
Sulaiman nada shekaru hudu Hjy Fatsima ta sake haihuwa inda ta sake haihuwar Da namiji lokacin ne aka rigima tsakanin turawa da salihin mutumin nan da ya baiwa addinin musulunci guduma wato *Sadam! Hussain* a ranar da aka haifeshi aranar aka kashe Sadam! don haka sati na zagayowa Alhaji Auwal ya sanya masa suna Sadam! Saboda duk wani musulimi a wancan lokacin yaji ciwon abinda kafirai suka aikata kan mutumin nan duk mai kishin musulunci dole sai ya jajanta al'amarin.
*******
Sadam! tunda ya taso yake da wani irin hali mutum ne mai gudun zuciya da tsantseni yana da tsafta sosai kuma miskili ne sam baya son wasa idan kagan shi tare da d'an uwansa sai ka dauka shine babba saboda Allah yayi masa kwarjini da haiba dukanin family dinsu babu ba'ki sai shi dukaninsu farare ne kyawawa daga mazan har matan hanci har baka ga uban gashi shi kadai ne 'baki a cikinsu amma kuma a zahirance yafi su kyau sai wanda ya zauna dashi zai fahimci hakan kyakykyawa ne mutuka yana da manya idanu wanda suka dan risina kadan kewayayyiyar fuskar ta kawatu da wani saje mai kyau da tsari kasan ha'bar sa da saman bakinsa yana yawan yin gyaran fuska saman goshinsa akwai wani abu da yayi duhu tabon sallah kenan Sadam! yana da ibadah da kula da addini tun yana dan shekara goma sha hudu ya sauke al'kur'ani mai girma kwataa-kwata ba tsarinsu d'aya da yayansa Sulaiman ba wanda shi ya kasance mutum mai a'kidun turawa kaf karatunsa akasar waje yayi yanzu haka yana aiki 'karkashin hukumar tsare birni da kewaye na jahar Kaduna Sulaiman yana ta'ba siyasa sa'i da lokaci don har takarar dan majalisa ya tsaya Allah bai bashi ba.
***
Sadam! kam tunda ya kawo 'karfi yaji yana sha"awar aikin soja don haka kawai sai ya sanja shawara ya shiga makarantar horar da sojoji dake Kaduna ba, General Abdul Salamu shine ya tsaya kai da fata kan Al'amarin Sadam! a cewar sa a wannan zamanin idan Najeria ta samu jajurtaccen mutum irin Sadam! zata samu cigaba irin wanda ake bukata.
To tun Alhaji Auwal da Hjy Fatsima basa son abun suka dawo suna so domin General Abdu salam da kansa yazo ya sake wayar musu da kai kan yanda al'amarin suke sai suma daga baya suka gane abinda yake nufi.
A da Sadam! yana karantar aikin likita ne wato bangaran mata to sauyawar ra'ayi yasa ya aje karatun likitanci ya shiga aikin soja gadan! gadan! A yanzu Sadam! nada mu'kamin Captain a brecck din nasu kuma suna masifar ji dashi saboda babu wani abu da zai tun karo su na tashin hankali bai magance musu ba,
****
*Waiwaye adon tafiya*
Wannan magana da Baba Ladidi da Baba Marka suke ta samo asali ne daga gurin marigayiya Baba Indo wato mahaifiyar sayyada kenan Baba Indo in dai baku manta ba 'yace ga Baba Ladidi ta kasance 'kanwar Alhaji Auwal da Kuma Kawu Tanko....To a tun lokacin da aka kaita dakin mijinta ta had'u da lalura wani ciwo ya fito mata a kafarta guda inda ya dinga cin jikinta a lokacin har ta haifi Sayyada tayi wayo kusan shekararta hudu a duniya saboda yanayin jinyar da Indo take ne yasa Baba Ladi ta dauketa ta koma gurinta da zama. To duk a wannan lokacin Ciwon ajali ya kwantar da Malam Jauro inda baiyi wata doguwar jinya ba Allah ya amshi ransa......Wata uku a tsakani Baba Indo ta bishi a ranar da zata rasu a ranar Sadam! yazo garin hutu.....Lokacin Sayyada tayi bud'ud'u da jar 'kasa hancinta dagaje! dagaje! da majina gashi lokacin kunnenta babu yari ga aski baba ladidi tayi mata saboda kuraje da suka dame ta Sayyada dai kwandala ba zaka siye ta ba, aikuwa rankwashinta yayi ta yayi mata tsawa! ya korata gida tana ihu! ta shiga gidan bayan baba ladi ta boya tana nuna shi shi kuma sai hararata yake....Baba Ladidi tace"Daga zuwanka zaka dinga dukanta wannan ai cin zaline da mugunta.
Yana ya mutsa fuska yace."Baba wannan yarinyar sadaka aka bawa mutum ba zai kar'ba ba yarinya kamar ba mutum ba dubi jikinta ka'zama babu kyan gani."
Tace."Ai wasa take kuma yanzu dama nake cewa bari nazo nayi mata wanka."
Yace."Babu wani kawai don nayi magana ne amma da banzo ba haka zata kwana." Mikewa yayi yace."Zanje na duba Baba Indo kafin na dawo kiyi mata wanka." Cikin jin haushi Baba Tace"Ba zanyi ba d'in! kai kaji yaro da iyayi da kaine kake sani nayi mata wankan? sai dai idan ka dawo kayi mata ehee."!
Fita yayi bai ce mata komai ba....Halin da ya iske Baba Indo a lokacin da ya isa gidan ya bashi tsoro
Matan gidan sun kewaye ta suna mata fifita masu kuka nayi da salati baba indo kuwa bata san inda kanta yake ba sai nishi takeyi kamar ance ta bude ido sai ta ganshi a tsaye a kanta ta mika masa hannu matan gidan duk suka cika da mamaki hannunsa ta rike da kyau tana so tayi magana bakinta yayi mata nauyi da kyar tace"A kawo min Sayyada." Matar kanin mijinta ta fita daga dakin da sauri ta sanya yaro ya nufi can gidan ya fada musu halin da ake ciki......Minti ashirin ya kawo su Baba Marka ta fashe da kuka ganin halin da Indo ke ciki Ita kuwa Sayyada kin zuwa gurin mahaifiyar tata tayi ta 'buya a bayan Baba Ladi dake kukan zucci tana addua Allah ya saukakawa indo wannan larurar
Mahaifin Sayyada ne ya shigo dakin tare da wani likita Ba tare da wani tunani ba likitan nan ya hada ruwan allura ya zurkuda mata a cewarsa allurar zata sanya ta samu saukin ciwon.....Ai ko minti biyar ba'ayi ba jiki ya rikice Indo ta dinga wata iriyar girgiza kumfa na fitowa daga bakinta sai a sannan kuma Bakinta ya bude ta dinga salati ta bude idanunta da suka jirkice tana kallonsu tana kiran sunansu tace"Sadam! ko bayan raina ina so ka auri Sayyada wannan shine burina Baba ku xama shaida na bawa Sadam! Sayyada Mahafin sayyada yace."Allah zai cika miki burinki Indo zaki samu sauki mu cigaba da rayuwa." Sadam! yace."Insha Allah baba kina raye zaki ga aurena da Sayyada nayi miki alkawai." tace"Mutuwa zanyi ku yafe min." Sai ta fara sha'kuwa tana salati a wannan lokaci Rai yayi halinsa.
Wannan mutuwa tayi masifar girgiza zukatan mutane domin indo mutum ce mai shiga rai da barkwanci kowa sai da ya girgiza da jin mutuwar Indo Mussaman mutanan da suke rayuwa da ita a cikin gidan a wannan lokacin akayi mata suttura aka kaita gidanta na gaskiya, Sai bayan an dawo ne mutanan kaduna suka sauka a garin Alhaji Auwal yayi kuka sosai da mutuwar kanwarsa yana kaunar Indo shiyasa duk wani abun