Showing 114001 words to 115099 words out of 115099 words
Chapter 39 - Bamu kadai ba ne book Complete by Zainab Makawa .txt
muka gane sunan da dan ta yaci watau Abdoullah.
Murmushi yayi yace malama mun fa gode Adisatu kin san rigima gareta a lokacin naso ta bari muzo tare amma ta matsa dole ita zata fara hanya.
Ya kara min godiya tare da yaba ma kokarin da akai masu yace zan iya cewa tun wanan lokacin komai a garemu Alhamdullahi.
Muma muka gode mai ga irin halarcin da yai muna na sakon daya aika min dashi daga baya yace haba haba wanan ba komai bane ai.
Muna kokarin mikewa mu bar falon ne nace sai dai akwai matsala dana hango wanan bakin dokin da aka shirya ma zaka hau kada ka haushi saida safe kasa a shirya ma farin adaidai lokacin da kake kokarin fitowa.
Kallona yayi cikin mamaki yace cikin yar murya kina nufin dokin da zan hau gurin kilisa gobe gurin suna nace shi din.
Ikon Allah ke nan da a kwai matsala ga bakin dokin nawa ke nan ?. Nace kwarai kuwa don yau sati daya ana asirce shi don jiran wanan ranan gare ka.
Cikin mamaki ya kara cewa ko zan san wanda yai wanan abin haka ?
Nace Allah zai baiyyana mai shi ta hanyan jarabtan shi da irin ciwon da mai shi yaso kayi ne don kaikayi zai koma ga mashekiya tun a gurin taron zai yanke jiki ya fadi a haka zaka gane maishi.
Muka barsu da matar shi cikin matukar mamakin abinda na fasa masu zai faru.
Bayan fitan mu yake cewa anya Adisatu wanan zancen gaskiya ne kuwa dokin da ko yaushe nake hawan shi tafiyan nan da nayi ne kawai ban haushi ba
Tace kadai yi hakkuri kayi yadda tace ma mu gani don gujewa wahalan rayuwa.
Buki ne sosai akeyi anci ansha anyi karyan arziki ko wace mace a gurin takai ta isa anan naga wanan masifaffan kakar tasu da ta sa Adisatu a gaba kan auren ta da mijin ta don basu so shi ya aureta ba sai daga cikin tsatson ta .
Tsohuwar na gani na ta kasa dauke idon ta a kaina ina ganin ta kira wata hadimarta tana tambayan ta ko ni wacece
Wacce ake tambayan take cewa daga Nigeria muka zo wai yan uwan Adisatu ne dake can.
Ta dago kai ta kalle ni na sake mata wani lalausar murmushi mai sake ma,ana ga maishi don karyan su ya kare ke nan.
Can maza suka fito saman dawa kan su sun saka mijin adisatu a tsakiya daga shi har dokin shi sun sha kwalliya sosai.
Sun na rafe suna dagawa mutane hannu har lokacin da suka karaso daidai wani rufa sun dan bada baya gurin wani mutum maji karfi daga mutanen dake zaune saman kujerun alfarma ya yanka wani irin ihu.
Take hankalin kowa ya koma furin shi nan ya zube a kasa wani farin kumfa yana fitowa daga bakin shi.
Aka kwashe shi zuwa ciki nan taro ya hargitse yan uwa da abokan arziki sai cewa suke subbahanallahi hamma alkasim ne .
Daga saman dokin da yake yakai idon shi a rufan da muke muna zaune saitin bayan matan shi idanuwan shi a kaina kai kawai na daga mai alaman hakane.
Haka aka karasa wanan bukin cikin sabon tashin hankali kakan su mai fada aji duk ta rikice ta rude sai cewa take a taimake ta bata son ta rasa alkasim din ta.
Komai yadda nai masu baya ni ya kasance masu Allah ya taimake su ba hamma Haroon ne ya hau dokin ba da sai buzun shi.
Don su bakin cikin su ya fara samun magaji ba zasu kai fa samun cin dukiyan shi ba da suks so shiyasa aka yanke shawaran a nakasa shi kowa ya huta.
Mun dawo gida da tarin saifa fam a tare da mu inda ban iso gida ba sai da matar gwauna tasa aka canza min kudin yakoma har miliyan uku da rabi namu na nan kasan.
****** ********* ******
Yanzu al, amari na zance Alhamdullahi ga karatu na koma inayi ina son hada digree dina don na rike kwalin a hannu na.
Ga harkan kasuwanci na abin ba, a cewa komai ba kasafai nake samun tsayawa yin aikin jinnu ba sai idan mutum ya tsurani ya zama dole nakeyin sa.
Nayi kudi fiye da tsanmanin mutum a wanan fannin na alamarin jinnu din dake kaina har yakai nakai yan uwana saudiya don sauke farali.
A shekaran da ya kewayo kuma maigidana ya samu cigaba don controler ya dauke shi ya mayar dashi Abuja suna aiki tare.
Shekaran da ya wuce ne na kara haihuwa lokacin na gama karatuna ranan suna mutane suna ganin bakin fuska dasu mukayi shagalin buki sai dai basu san iyalin baba malam ne dana mai shagona da su mukkadarasiya suka zo min wunin buki.
Yanzu idan kin ganni na koma wata hamshakiya dani ba kasafai nake son ina al, amarin jinnu ba duk da har wanan lokacin da nake baku labarina suna tare dani babu abinda ya canza a gareni na al, amarina dasu ban dai da lokacin yin wanan harkan ne don irin ci gaban rayuwan dana samu a yanzu din.
Da fatan yan uwa zasu dinga kiyayyewa a gidajensu da tsaron lafiyan mu dana yaran mu don kaucewa shiga hakkin wasu da bamu ganin su.
Amma su suna ganin muna ganin su da gangan muke shiga hakkinsu.
Na tabbatar da zamu kiyaye rayukan mu daga abubuwan da sunna ya koyar damu mukai watsi dasu insha Allahu babu abinda zai samu rayuwan mu.
Don wanan matsalar a yanzu babu family din da basu shafi wani ba amma mu bamu sanin hakan don ba ganin su mukeyi ba.
Nima zainab ina ce maku anan zan talaita maku labarin maman Abba don samun ci gaba da sabon novel dina dana farawa mosaya na da fatan Allah ya tsare ya kare muna rayuwan mu dana yayan mu da yan uwan mu musulmi.
Nagode kwarai da so da kaunan da kuke nuna min a kullun da dan lokacin da kuka bamu gurin bin karshen wanan labarin.
Allah ya kare mu ya tsare mu sai kuma wani lokaci idan Allah yakai rayuwan mu lafiya nagode nagode kwarai gareku yan uwa musulmai ga fahintar sakon mu a gare ku ma,assalam.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU