Showing 153001 words to 156000 words out of 168541 words

Chapter 52 - Bazan Barshi Ba! Complete Hausa Novels By Billy Giro .txt

14 Jan 2025

9858

shi don ko da kuskure ta kalle sa sae ya watsa mata mugun kallo.
Washe gari ta tashi da wani irin zazza6i mae qarfi ta yini haka komai bata iyayi sae alawiyya ce ke d'an kula da ita wacce taso a snr da mohd Ryynt tace a'a dan ta fahimci alwiyya bata san abinda ake ciki ba.
Kwanan ta biyu tana fama da rashin lafiya a na ukun ne taji sauqi sosai dan komai tana iya yiwa kanta qarfin jikinta ne kawae bae gama dawo mata ba.
Da yamma bayan la'asar tana zaune kan darduma riqe da qur'ani tana karatu sae ga mami ta shigo d'akin aguje tace"Anti yaya Nasir na kira ku gaisa"
Ryynt ta tashi riqe da hannun mami suka fito Nasir na zaune shida mohd kan doguwar kujera yayinda mohd ke riqe da laptop yana wani aiki wanda yana ganin Ryynt ya tashi ya bar gurin byn yace da Nasir idan kaje ka gaida inna.
Nasir yace "za taji"
Yayinda Ryynt tayi qoqarin had'iye hawayen dake son fito mata ta shiga gaida nasir, nasir ya amsa gaisuwar yana kallon ta da kulawa dan ya fahimci da kmr akwai damuwa a tattare da ita har dae yanda yaga ta rame nn ya bawa mami makullin motar sa yace je d'auko ice cream a mota mami ta kar6i key ta tafi aguje sae murna take tana tsalle a natse nasir dake kallon Ryynt yace"me yake damunki ne Ryynt?
Ryynt tayi saurin girgiza kanta tace"ba komai"
Yace"amma kuma kika rame da yawa haka ko dae ba kya son gaya min abinda ke faruwa ne"
Ryynt tayi d'an guntun murmushi tace"ba haka bane nayi zazza6i ne kwana biyu"
Yace"Eyyah Allah sarki to ya jikin?
Tace" Alhmdlh ae naji sauqi sosai"
Ta qarashe mgnr ne yayinda mami ta dawo riqe da ledar ice cream,Nasir ya kar6i makullin motar sa yace"to ni na tafi Allah ya bida lafiya tace"Amin"
snn ya tafi ita kuma taja mami suka koma daga ciki suna shiga mami ta bata d'ayar robar ice cream dan guda biyu ne Ryynt tace"Aa kaiwa alawiyya dae idan zata sha .
Mami na fita Ryynt ta zauna tare da d'aura hannun ta akan cikin ta sae kallon cikin take tana shafa shi a hankali tana sauraren yanda cikin ke motsi yayinda hawaye ke silalowa a hnkli kan fuskarta dan tayi kewar kulawar mohd ba kad'an ba.
Bayan kwana biyu da faruwar haka guraren qarfe goma sha biyu na dare Ryynt na kwance tana bacci kan darduma riqe da littafin addu'o'i a hannunta,
a cikin baccin nata ne ta soma jin daddad'an qamshin turaren mohd yana shiga hancin ta nn ta soma bud'e idanun ta a hankali har ta sauke su akan mohd dake durqushe a gabanta d'auke da qwallah tap a idon sa sae kallon yanda ta rame yake.
A d'an tsorace ta tashi zaune tana kallon sa sae ganin tayi ya tafi da ita zuwa jikin sa ya rungume ta sosai a jikin sa sae kuka ya fashe dashi yana bata haquri kan abubuwan da ya mata dashi kansa baisan dalili ba Ryynt dae bata ce komai ba sae kuka ta fashe dashi itama yana ta rarrashinta har ya samu tayi shiru ya cire mata hijab tare da d'aura hannun sa akan tulun cikinta yana kallon yanda cikin nata ya qara girma bae ce komai ba sae kallon yanda ta rame yake cike da tausayi don har sae da idanun sa suka ciko da qwallah yace"my Ryynt dan Allah ki yafe min wlh bansan ya akayi ba haka kawae naji na tsane ki amma bayin kaina bane wlh i don't know why"
Ya qarashe mgnr ne yayinda hawaye suka gangaro kan fuskar sa.
Ryynt da bata kawo zargin kowa a ranta ba tasa hannu ta share masa hawaye snn ta kwantar da kansa a qirjin ta tace"ba komai Mk sharrin shaitan ne da baya son ganin ma'aurata cikin shiri kuma inshaa Allah ba zae sake yin galaba akan mu ba.
Nan mohd ya maida ta kan qirjin sa ya kwantar ya lumshe idanun sa sae shafa bayanta yake haka itama idanun ta a lumshe suke tana shafa sumar qijinsa a hankali sbd rigar da ke jikin sa a bud'e take.
Haka suka kwana abinsu har safe baccin da Ryynt taji kmr kar ta farka sbd ta jima batayi bacci mae dad'i irin sa ba.


Guraren qarfe tara na safiyar rnr Ryynt ce ta shigo d'akin mohd cikin doguwar rigar ta mae kyau ta atamfa ta sami mohd d'aure da towel ya fito daga wanka knn yayi tsaye sae kallonta yake tayi dan sosai tayi kyau duk da ramar da take d'auke da ita kuwa.
Bata iya qarasawa ba sae sadda kanta tayi qasa dan haka kawae taji tana jin kunyar sa sae mohd d'in ne ya qaraso da kanshi gurinta ya kai lips d'insa a hnkli kan goshinta ya d'aura mata kiss,a nn ta mishi ina kwana ya amsa tare da jan hannunta suka je kan bed suka zauna yakai hannu sae shafa cikinta yake yana kallonta yace"babyna yana lafiya?
Ta gyad'a masa kai tare da kwanciya kan qirjin sa takai hannu tana shafa sumar qirjinsa da ta kwanta luf abin sha'awa.
Mohd kuwa d'ankwalin kanta ya ture yana shafa gashin kanta da yasha gyara har ma yana fitar da wani daddad'an qamshin da kai tsaye mohd ya soma jin kansa a kasala ya lumshe ido sae shaqar qamshin yake yana ci gaba da shafa sumar a hankali, Ryynt na jinsa har ya soma wuce gun dan zip d'in rigarta ya zuge sae shafa jikinta yake ta koina yana kissin d'inta bata hana shi ba ta bada kai suka shiga romancing d'in juna kamar zasu kashe kansu har suka lula duniyar ma'aurata wacce suka ji dad'inta ba kad'an ba.


Tun daga rnr wata irin tsabar kulawa da soyayya mohd ke nunawa Ryynt wacce tafi ta farko ma dan duk rnr girkinta zaka gansu harabar gidan gurin shan iska manne da juna sae soye wa suke tayi abinsu kmr wasu Luv birds.
Malika kuwa tun da ta fahimci sun dawo da shirin su ba yanda batayi ba na ganin ta wargaza shirin ta hanyar sake zubawa man garin magani a abinci amma abu ya faskara sbd still Ryynt batayi sake da nafilfili da addu'o'in da takeyi ba dare da rana.
Kan dole malika ta gaji ta daina zuba masa maganin cike da nadamar ina ma tun farko bata soma ba dan gashi yanzu shirin da sukeyi ma yafi na daa yayinda ita kuma ta qara dawowa kwandon shara.


Sannu sannu lokaci keta tafiya dmn yanzu cikin Ryynt ya shigo cikin wata na tara yayinda cikinta yayi wani irin girman gaske da duk wanda ya ganta sae ya tausaya mata don ta ma daina fita koina ko downstairs ma sae da taimakon mohd take iya saukowa wanda yanzu kwata kwata mohd bashi da wani aiki sae na kula da ita hatta office ma ya daina zuwa ya barwa Amir da Aamil ragamar kula da asibitin dan shi yanzu ta Ryynt yake wacce duk safe da yamma sae ya fita da ita a cikin harabar gidan ya sata su zagoya gidan kaf duk fad'in sa kuwa.
Hakan duk yafi qona ran malika dan duk tulun cikin da ke gaban Ryynt bae hana man ya d'auki abar sa idan ta gaji da zagayawar ya tafi da ita gun resting chairs ya zaunar kan kujera ya kuma tsiyaya mata fresh milk mae sanyi a cup ya bata tana sha shi kuma ya shimfid'a handkerchief a qasa ya zauna ya kama qafafunta ya d'aura kan jikinsa yana matsa mata su cike da so da kulawa.


Ranar lahadi da dare guraren qarfe tara mohd ne jikin wardrobe yana ciro tufafi sae ga Ryynt ta shigo d'akin cikin shirin ta na bacci mohd yazo da saurin sa yaja hannunta yaje da ita kan bed ya zaunar da ita ya ciro farin handkerchief yana share mata zufar da ya gani a kan goshinta d'auke da damuwa a fuskar sa yace"Ryynt meyasa kika fito da kanki baki kirani a waya nazo ba"
Tace"na kira wayar ka ban samu ba kuma gashi ina son in fito"
Kallon ta mohd yayi cike da tausayi dan yasan da qyar ne ta iya saukowa don gashi sae numfashi ma take ta fitarwa sae duk yaji kamar ya cire cikin ya maida a jikin sa amma ba yanda zae yi tunda abune da bazae yiyu ba hkn ya tashi ya tsiyayo mata ruwa masu sanyi a glass cup ya zauna ya bata tasha snn yasa ruwan a handkerchief ya d'an jiqa shi yana share mata goshinta,fuskarta har zuwa qirjinta.
Ryynt dake kallon sa tace"ina zaka tafi da daren nn naga kana ciro kaya?
Yace"tafiya ce ta kamani Ryynt"
Kmr zata yi kuka tace"zuwa ina?
Yace"Abuja zan tafi"
Tace"zan bika"
Cikin muryar rarrashi yace"my Ryynt kinsan ba zae yiyu ba kiyi haquri ae kwana biyu kawae zanyi kinji"
Tace"to ka kaini gidan inna in ka dawo sae ka d'auko ni"
Yace"No my Ryynt ga alawiyya ae zata riqa taimaka maki da wasu abubuwan kinji yi haquri"
Kallon sa tayi qwallah tap a idonta yayi saurin girgiza kansa yace"yi haquri dan Allah kar kiyi kuka kinji ba jimawa zanyi ba 2dayz ne fa kawae"
Da qyar Ryynt ta iya had'iye hawayen ta snn ta gyad'a masa kae.
Mohd ya rungume ta a jikin sa yana qara rarrashinta.


Washe gari tun da safe mohd ya tafi ya bar Ryynt sae kuka take wanda ba irin rarrashin da bae mata ba amma taqi shiru hkn ya tafi ba a son ransa ba wanda ba don tafiyar ta zamar masa dole ba da ya fasa.
Malika kuwa ba kad'an ba taji dad'in tafiyar sa sbd wani tunanin da ya fad'o mata a rae da zata samu tacika burinta kafin ya dawo shiyasa yana barin gidan tasa qafa ta fita.
Bata wani jima sosai ba ta dawo bata zarce koina ba sae d'akin Ryynt bata shiga ba ta la6e tana jiyo sautin kukan Ryynt a hankali dan har lokacin bata daina kuka ba.
Le6ace da baki malika ta baro qofar tana mae fad'in"wae ke miji dad'i zaki ci ubanki an jima don wlh sae kinyi naqudar baki shirya ba"


Da dare ta sake dawowa ta samu Ryynt na bathroom tana wanka mami kuwa har tayi bacci.
Kai tsaye ta nufi fridge har zata bud'e ta hango ruwa da cup a ajiye kan bedside drawer nn taje da sauri ta bud'e gorar ruwan ta saka wani tablet qwara biyu a ciki ta shiga jijjiga gorar ruwan har maganin ya narke tsaf snn ta ajiye ta fita ta la6e a bakin qofar d'akin ta jira har sae da Ryynt ta fito daga wanka tana kallo Ryynt ta tafi kae tsaye gun bedside drawer ta tsiyaya ruwa a cup tasha snn ta nufi dressing mirror ta zauna tana shafa Vaseline.


Nan Malika ta bar qofar d'akin cike da murna ta kira fa'iza tace"tayani murna fa'iza wnn abar dae tasha maganin"
Fa'iza tace"dagaske?
Malika tace"wlh kuwa a gaban idona ina kallo tasha nasan ko ta kira kafin dae azo a tafi da ita asibiti abinda ke ciki ya gama hallakewa ita kuma kin san sauran"
Nan fa'iza ta fashe da dariya tace"aikin ki na kyau malika kika ce dae gobe akwai labari mae dad'i"
Malika tace"hm bari kawae kedai zan kiraki goben"
Daga nan ta katse wayar.


Ryynt kuwa lafiya lau ta gama shirinta na bacci mohd ya kirata a waya suka jima suna waya bayan sun gama wayar ne snn ta kwanta bacci a cikin baccinta ne wani irin ciwon baya ya farkadda ita wacce tun tana jin abun sannu sannu har abun ya soma yawa sae juyi take ta kasa komawa bacci.
A gurin mohd ma haka ta kasance don yana cikin baccin sa haka kawae yaga ya farka ya kuma rasa me ke masa dad'i sae tuñanin Ryynt da yake.
Nan kawae ya jawo wayar sa ya kira ta ba tare da ya damu da ganin ko qarfe nawa na dare ba shidae yaji lafiyar ta.
Ryynt da har ta zame kan bed tana durqushe kan guiwoyinta cikin matsanancin hali taji wayarta ta soma ring ganin mohd ne mea kiran yasa ta iya d'aga kiran amma kuma ta kasa cewa komai sae mohd ne keta magana bata iya bashi amsa.












Billy giro😊
[10:07PM, 5/2/2017] Billy giro😊: ```🔮BAZAN BARSHI BA🔮```




























🔮🔮🔮
*page 88*
Sae can Ryynt ta samu da qyar tace"Mk bana jin dad'i ka bari da safe mayi waya"
Daga haka bata jira me zae ce ba ta katse kiran ta ajiye waya ta soma kuka a hnkli sbd zafin ciyon abinda take ji ya soma kaita maqura.
Mohd kuwa duk ya rud'e sae kiranta yake tayi amma bata d'aga ba nn kawai ya kira Nasir da inna ya sanar dasu halin da ake ciki.
A cikin daren Nasir ya tashi ya shirya yaje ya d'auko inna suka zo gidan.
Kai tsaye suka nufi d'akin Ryynt Nasir ya tsaya a bakin qofa inna ta shiga daga ciki ta sami Ryynt kwance cikin jini duk ta galabaita sae kuka take a wahal ce tana juyi a qasan tiles d'in d'akin.
A rud'e Inna ta qwalawa Nasir kira ya shigo d'akin wanda bae tsaya wata wata ba ya kama Ryynt inna ta kama masa suka fito da ita suka saka ta a mota ,
inna ta zauna baya tare da ita Nasir yaja motor a gaggauce suka bar gidan.
Nan itama malika ta fito ta shiga motar ta ta bisu dan tun shigowar su gidan tana sane asali ma ita da kanta ta bud'e musu qofa a lokacinda taji suna knocking.
Man hospital suka nufa ta parker motar ta tayi zamanta a ciki tana kallo aka shiga da Ryynt ta saki shu'umin murmushi d'auke da chewing gum a bakinta tana taunawa ta d'auki wayarta ta kira fa'iza ring d'aya biyu sae ga fa'iza ta d'aga ,
malika tace"au bakiyi bacci ba knn"
Fa'iza tace" inafa hubby bae barni ba kinsan yau ya dawo daga tafiya da qyar ma na samu ya saurara min yanzu haka ma yana bathroom yana wanka sae dae kuma ke ya akayi bakiyi bacci ba har yanzu?
Hm lallai fa'iza har kya tambaya ae yau banga ta bacci ba sae komai ya gama faruwa a gaban idona tukun don yanzu har wnn abar ta kira wnn tsofuwar da ake kira inna sun zo ita da Nasir suka kawo ta asibiti shine na biyosu sae kallon su kawae nake dan na tabbatar ba abinda likitawan zasu iya mata don kafin ma su iya yin komai abinda ke ciki ya riga ya gama hallakewa haka itama zafin aikin maganin da wahalar naquda bazai bar ma ta rayu ba don kan aje koina ma har ta fara bleeding"
Fa'iza tace"Au haba?
Malika tace"Wlh kuwa ae overdose na had'a mata maganin ynx jira kawae nake in ga an fito da gawar er banza.
Fa'iza tace"kae kinyi dae dae wlh,
ashe koni banga ta bacci ba yau sae dae najira kiran wayarki dmn naji kyakkyawan labari"
Malika tace"lallai
dae kam ki saurari kirana ko yaushe don yau kan farin ciki ma har sadaka sae nayi abinda ban ta6a yi ba a rayuwata kuwa"
Fa'iza tayi er dariya tace"kinga bye sae kin kirani dan naji alamar hubby zae fito daga bathroom baccin qarya nake so zanyi dan nasan halinsa in yaga ban koma bacci ba ko yayi wanka wlh zai iya sake nemana a second round"
Malika tayi er dariya tace"ae kima yi baccinki dan koni idan naga zasu 6ata min time gida zan koma dole dae da safe zanji labari don mutuwa dae ba 6oyuwa take ba kawae dae ki saurari kirana"
Fa'iza ta fashe da dariya tace"kae malika bakida dama wlh"
Malika tace"uhm kedai sae anijma"
nn suka katse wayar.
Daga nn ma kawai malika taja motar ta ta koma gida.


Ryynt kuwa har washe gari ba kanta sae wahala da take ta faman yi ita bata haifu ba ga jinin yaqi tsayi duk da irin taimakon da nurses keta bata kuwa.
Guraren qarfe goma sae ga mohd ya diro asibitin da kallo d'aya zakayi masa kasan hankalin sa a tashe yake.
Ya sami inna da Nasir still su kad'ai ne a asibitin ba wani wanda yazo dan ba'a sanar da kowa ba tukun sae anga yanda abun ya kasance.
Yace dasu"ya ake ciki ne dan Allah ina Ryynt d'in take in ganta?
Kafin suce komai sae ga wata likita ta fito tana ganin mohd tace"yauwa Dr ur wife tana cikin wani yanayi gabad'aya ta galabaita sam bata iya pushing any more da kamar sae an mata aiki"
A rud'e Mohd yace"muje in ganta"
Nan suka tafi kai tsaye se d'akin da Ryynt take wacce ke kwance kan gadon haifuwa abin tausayi duk ta wahala mohd ya nufi gurinta kmr zae yi kuka yana kallon yanda take bleeding a fusace ya kalli nurses d'inda da ke kan Ryynt yace"wane irin abune haka kun bar min ita sae bleeding take kuma kun kasa fitar min da babies d'ina so kuke su mutu ne ko yaya!
Likitar da suka shigo tare da shi tace"Sory Dr wlh it's not our fault haka aka kawo mana ita kuma munyi iya qoqarin mu amma abu ya faskara kawae abinda na fahimta ba time d'in haifuwar ta bane da akwai maganin da tasha da ya mata qarfi har ya tashi naqudar shiyasa ta wahala har ma abinda ke ciki duk ya galaibata baya iya yunqurin fitowa"

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login