Showing 6001 words to 9000 words out of 168541 words
Chapter 3 - Bazan Barshi Ba! Complete Hausa Novels By Billy Giro .txt
ko munje gida ba shiga zanyi ba wlh ,kuma sae naci uban wnn er iskar yarinyar da ka kaiwa inna wacce a dalilinta aka hana ni jan mota sae naga ta yanda ma zata zauna gidan inna d'in dole ta barshi tunda ba gidan kakarta bane ko wani nata.
Nasir yayi shiru yana kallon pretty shidai ko kad'an baya son masifar nn tata gashi aikin kenan idan aka ta6o ta.
Hannun ta ya riqo tare da kai mata sumba snn yace"da kika yi shiru sae kika min kyau kamar ace ko yaushe haka kike ba ruwanki da fad'a"
Hm ba wani dad'in baki da zaka min nifa sae ka kaini gidan inna ,kallon ta yayi yana tunanin wayon da zai mata dmn yasan duk taje gidan inna ba qaramar rigima za'ayi ba,yace"gidan inna kwantar da hankalinki zan kaiki amma sae kin raka ni gida nayi wanka tukun,ta6e baki tayi tana kallonshi snn tace"wankan me zakayi da baza ka kaini gidan inna ba har sae na raka ka,banyi wanka ba da safen nn ina gama sallar asuba naje gida dmn nazo dake, kuma yunwa nake ji sosai kinsan kin tafi kin bar ni ba abinci kuma yau da safe ma haka,shine nake son ki had'a min breakfast kafin na fito wanka kinji,
ya fad'i haka ne cikin marairaicewa had'e da tsare ta da ido dmn yasan da ya mata haka bata iya masa gardama,
ta kauda fuskarta gefe kamar baza ta amince ba sae kuma tace "naji"
Karfe takwas da minti goma na dare Rayyanat na kitchen tana yi ma inna goge goge bayan ta gama wanke kwanukan da suka ci abincin ta ji an bude katon gate din gidan alamar mota xae shigo knn, duk lkcn da taji karan bude gate din sae gabanta ya fadi don ba sabawa tayi ba, bayan kusan minti bakwae inna ta shigo kitchen din ta gwalo ido tace "lahh bar maki aikin Hurera tayi" Rayyanat tace "A'a ni na karba inna" inna ta washe baki tace "ayyo!sannu da aiki jikata, ynxu duk ke kika gyara kitchen din nn hka" Rayyanat tayi murmushi ta sunkuyar da kanta bata dae ce komae ba, inna tace "to miko min wancan kulan abincin in kai ma mai gidana ya xo" Rayyanat ta dauko ta mika mata da ladabi inna ta fita tana cewa "yau ko dan kankanan da lemo bae siyo min ba ya kwaso kafafuwa ya xo xae cinye min abinci uwa shi ke siyo min" bayan minti goma da fitan inna Rayyanat ta gama abinda take a kitchen din baka taba cewa daga kauye take komae nata tsaf tsaf take yi, da kyar ta iya fitowa daga kitchen din a sanyaye tuno babanta da ta yi, hkn yasa kwalla ya cika idonta, tayi saurin sharewa bata tarda kowa falon ba sae hurera yar dattijuwar matar da ke goge tiles din falon ta kalleta tana murmushi tace "sannu Rayyanah, ki tafi can daya falon inna na can, amma ga furar ta nn da na dama mata ki dauka ki tafi mata da shi, Rayyanat ta gyada mata kai kawae ta dauki furan da ke rufe kan centre table ta nufi falon da Baaba Hurera ke nuna mata, inna na xaune kan tabarma ta tankwashe kafa ta kapa ma tv ido tana kallo uwa tasan abinda ake yi, shi kam yana xaune kan three seater rike da remote waya na kare kunnansa alamar waya yake, kallonsa kawae Rayyanat take a sace kuma a tsorace sae dae har lkcn bae juyo ba, inna ta juya da sauri ganinta a tsaye tace " A'a karaso mana Rayyanah" Sae a snn ya juya yana kallon da warce kakar tasa ke mgna, Rayyanat ta sake kwanon furar hannunta ba tare da ta shirya ba, inna ta mike da sauri tana salati, ya katse kiran da yake shi ma ya mike yana yatsine fuska yace "ina kika samo mai aikin nn kuma Inna, idan xa ku dauki masu aiki ku dinga bincike da kyau don Allah ku dena dauko yara irin hka masu kananan kwakwalwa, bnda hka meye xata shigo falon mutane ta sake masu kwanon fura a kasa kmr wata me tabin hnkli" juyawa Rayyanat tayi da gudu ta fice daga falon a rude.
Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[2:38PM, 5/2/2017] Billy giro😊: 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮
```Na Billy giro😊```
16/12/2016
🔮```7```🔮
Oh Allah yoni hajara!kai muhammadu ai wnn yarinyar iyakar hnkli da natsuwa tsautsayi ne kawai da in yazo ba mai tare shi.
Inna ina hnkli a nn da shigowarta ta 6arar da fura kmr wacce bata saba ganin mutane ba,kudai 'ya'yan kabiru haka kuke abu kad'an ya isheku masifa,
inna yau maigidan naki kike gaya ma haka, yo ai ko waye kai tunda ka ta6a er albarkar nn dole na maka magana yarinya tsakanin jiya iyau lafiya muke zaune sae gashi kazo zama d'aya ka rikita ta har ta tafi da kuka,nidai inna da wnn mitar kira hurera tazo ta goge gurin nn ,kuma dan Allah kidaina kwaso iren iren yaran nn sam ba abin yarda bane da har kike saurin bama yarda zama d'aya,wai er had'uwar jiya zuwa yau ce kike kora min bayani kamar kun shekara, masifa inna ta shiga yi dashi,Man ya bita da kallo yana murmushi har ta fita.
Taje ta samu Rayyanat a d'aki sae kuka take rusawa,
tayi zaune tana rarrashinta har ta samu tayi shiru.
Rayyanat ta tashi tana share hawaye tace"inna bari naje na kwashe furar"a'a ai nasa hurera ta kwashe, kika sata inna nifa na 6arar,kar ki damu indai hurera ce bata da wnn,bari na tashi naje nabar maigidana shi kad'ai ,tace"to inna"inna na fita Rayyanat ta kifa kai taci gaba da kukanta.
Da dare Nasir yazo ya samu sun kammala cin abinci sunyi zaune suna kallo ya gaida inna snn ya samu guri ya zauna ,Rayyanat ta sadda kanta qasa tana miqa gaisuwa ya amsa gaisuwar snn yace"ya jiki ?tace"Alhmdlh yace"kina dai shan maganin ki akan lokaci ko? Gyd'a masa kai kawai tayi tana wasa da en yatsunta.
Ya maida dubansa gun inna da ta miqe qafafu tana kallon Indian film kamar wacce kejin wani abu dmn duk ta tattara natsuwarta a can.
Sae da abin ya bashi dariya sae dai bai yarda yayi ba dmn yasan masifa zata aje mai in tasan dalili dryr dmn kallo d'an gidan ta ne ba mai shiga tsakanin su.
Yace"inna hln mai gidan naki ya koya miki indiyan ci ne naga kin maida hankali sae sauraren su kike?yo ina fa na iya Rayyanah na saka ma shine nayi zaune nima ina kallon abin tausayi naga sae wulaqanci yarinyar kesha a gun mijinta,dariya yayi yace"to ke inna ya akayi kika san mijinta ne? Yo kai Nasir banda idanu ne ko ko banda fahimta,gashi har gado d'aya naga suna kwanciya ai wnn sae miji da mata,dariya kawai yayi ya ajiye zancen dmn ya kalli film d'in ba miji da mata bane budurwa ce da saurayi ya mata ciki shine yake wulaqanta ta.
Hannu yakai ya shafi sumar kanshi yace"inna zan tafi "ah ah kaiko da wuri haka ,inna aski zanje sae dai gobe idan na sake shigowa ,to Allah kiyaye ,
sae da yace"Amin snn ya fita.
Ko minti ashirin bai yi da fita ba sae ga Man ya shigo gidan sae dai shi ba kallo ya samu suna yi ba tausa ya samu Rayyanat tana yima inna.
Rayyanat na ganin shi sae duk ta nemi natsuwar ta ta rasa, haka ta dake ta gaida shi ta kuma yi saurin tashi tabar gurin.
Bai ma amsa gaisuwar ba sae inna ya gaida ya ajiye ledar da ya shigo da ita kusa da inna snn ya zauna,inna ta tashi zaune tana washe haqora tace"me kuma kazo min dashi yau? Sae da ya jingina bayansa kan 2 seater d'inda yake zaune snn yace"gasasshiyar hantar rago ce na siyo miki kan hanya"
Kai Allah dai shi yi maka albarka kamar kasan nayi kewarta wlh,ai inna har fruit naso siya miki se na manta,,ayyo ai d'azun da rana Nasir ya shigo min dasu munsha har mun gode Allah har ga saura a fridge ko na d'auko ma zaka sha?Aa inna, to abinci kam zaka ci dai ko? shima haka dmn a qoshe nake, yau tawaye kamin kenan ,Aa naci abinci ne a gidan wani abokin mu da yayi sabon aure muka je, oh ni kakata talatu kai yanzu ka gwammace kayi ta zuwa gidan abokanai ba a zuwa naka ,
wai nikam yaushe zaka fara ra'ayin aure ne muhamnadu,hm inna ai aure lokaci
ne dashi kin sani in lokaci yayi zanyi har ma a wayi gari watarana kina zaune zagaye da en jikokin ki, nn inna ta washe baki tace"Allah nuna mana lokaci muna masu rai da lafiya"Amin inna.
Washe gari Rayyanat ta gama taya hurera duk ayukkan da take tazo tayi kwance qasan tiles tana jiran fitowar inna daga gurin wanka nn bacci yayi awon gaba da ita.
Pretty ce ta shigo gidan tayi tsaye tana kallon Rayyanat dake bacci tace"yau zaki ci ubanki yarinya"
Nan taje ta bud'e fridge har ta d'auko gorar ruwan sanyi sae kuma ta girgiza kai ta mayar ta nufi kici tana murmushin mugunta ta d'auko flask d'in ruwan zafi tazo kai tsaye ta bud'e tana kwara ma Rayyanat su a jiki ,
ihu Rayyanat ta saki ta tashi a firgice tana lalubar bayanta inda taji saukar ruwan zafi.
Mari pretty takai mata tace"er iska ai yau sae kin bar gidan nn wlh tunda bana ubanki bane!
Taja Rayyanat kamar wata kayan banza ta ingizata waje da qarfi sae kawai Rayyanat taji ta fad'a jikin mutum hkn yasa taji saukar wani irin gigitaccen marinda ya soma fitar da ita hayyacinta.
Billy giro😊
🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮🔮
[2:38PM, 5/2/2017] Billy giro😊: 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮
```Na Billy giro😊```
17/12/2016
🔮```8```🔮
La'ilaha ilallahu Muhammadu rasulillahi sallallahu Alaihi wa sallam!
Cewar inna wacce ta fito daga gurin wanka tace"Muhammad me rayyanah ta muku ne da zaku mata taron dangi tun ina bayi naji ihunta Fatima na faman sirfa mata masifa yanzu gashi na samu ka tafka mata uban mari haka!inna ta qarasa magana cikin muryar kuka irin na tsafi d'in nan.
Nan take man damuwar sa ta bayyana ya shiga bawa inna haquri bata kula shi ba sae kuka take taja Rayyanat suka koma cikin d'aki.
Pretty ta kalli man dake qoqarin bin su inna tace"to wai meye abun damuwa kabar su mana tunda kasan halin inna dama saurin kuka ne da ita in ba don shi ba meye abin kuka wa wannan er qauyen,harara ya dalla mata yace ai duk ta dalilin kine banga uban me ya kawo ki gidan nn ba....kamar ya yaya...zan mare ki wlh idan baki 6ace min da gani ba!
Turo baki tayi tana faman gunguni har ta fita gidan.
Man kuwa shiga d'akin yayi amma a iya falo ya tsaya inna ta fito tana shar6ar hawaye zata d'auki wayarta dake kan TV stand yace"inna yi haquri Allah sam na d'auka rashin hnklinta ne yasa ta fad'o min a jiki ban san cewa pretty ce ta ingixo ta ba,amma Muhammadu ai ka saurara mata ko! yanzu gashi bayan fasa mata baki da kayi duk bayanta ya kwaye... Kamar ya inna nifa marinta kawai nayi... Yo kai ba kasan ruwan zafi pretty ta watsa mata a baya ba,shiga ka duba ta kaga ai nasan dole sae an yanke wnn ftr ,ta qarasa maganar cikin kuka snn tace"ka shiga mana ka duba min yarinyar mutane kazo kayi tsaye se kallona kake!
Ba musu ya shiga ya sami Rayyanat ruf da ciki se kuka take abin tausayi zip d'in rigar ta a bud'e fatar bayanta har yyi ja, kauda fuskar sa yayi tare da sauke ajiyar zuciya snn ya kalli inna dake tsaye kusa dashi tana matsar kwalla yace "inna ina ganin ta sosa bayanta ne a lokacin da aka watsa mata ruwan, kuma wnn da gani ma ba wani ruwa me xafi bne, Rayyanat da bata ji shigowarsa dakin ba sae maganar sa taji tayi saurin tashi xata rufe zip d'in rgrta, inna ta karaso da sauri
tace "A'a Rayyanah kar ki rufe ai shi likita ne zai duba miki bayanki in kuma baxae iya ba sae ya kira mana ubansa ya xo ya kai mu asibiti," Rayyanat ta girgiza kai ba tare da ta kallesu ba alamar bata so, inna tace "A'a ki yi haquri ya duba ki kinji jikata"
Man da takaici ya ishe shi yace "inna bari kawai zan turo a duba ta" yana kai wa nn ya fice daga dakin kmr xae tashi sama.
Sae da ya kira wani abokinsa likita snn ya bar gidan ya nufi gidan kanwarsa pretty.
Yana isa gidan Nasir ya samu kan dining sama sama suka gaisa yace masa "ina pretty" kafin ya basa amsa sae ga prettyn ta sauko, bata damu da ganin fuskar yayanta ba annuri ba ta daure fuska ssae tace "gani yaya lafiya dai ko"
Yyi mata wani mugun kallo yace "me wnn yarinyar ta miki da zaki xuba mata ruwan xafi a jiki," shiru pretty tayi tana kallon shi kamar bata san me ya faru ba har lkcn fuskarta a tamke, ya daka mata tsawa yace "ya kika min shiru kina kallona ina maki mgna?" Ta tabe baki tace
"To nifa yaya ban gane zancen da kake ba bare na iya ce maka wani abu," nn ya fahimci ta fita ne bada ixinin nasir ba shine take wani nuna kamar bata san da zancen ba.
mari ya kai mata don bata da nisa daga inda yake yace "yanzu kin fahimci zancen nawa!ko kuma sae na qara miki wani," da sauri taja baya tana kuka don ganin da gaske yake, tace "to shine zaka wani mareni wlh sae na gaya ma umma!
daga haka ta tafi da gudu tana kuka ta haura sama.
Duk da Man ya fahimci Nasir yana buqatar jin bayani bai tsaya yi masa ba ya tafiyar sa hakan yasa nasir ya tafi ya haura sama gun matarsa da shima ya fahimci gidan inna taje bai sani ba.
Da shigarsa ta taso ta rungume shi tana kuka tace "ka gani dai ko honey ban masa komai ba yazo ya mareni," mugun kallo yyi mata yace "bana son qarya pretty nasan halin Man ba zai zo haka kawai ya mareki ba ,ba makawa gidan inna kika je gun Rayyanat kika aiwatar da nufinki ko?" shiru tayi alamar can taje d'in, nn ya shiga yi mata fad'a sosai daga qarshe yace duk ta qara fita bada izinin sa ba sae ya sanar da Abbanta, fushi ta shiga yi dashi bai kula ta ba ya tafiyarsa yaci abinci ya fice daga gidan.
Gidan inna ya nufa yaje yaga aikin da pretty tayiwa Rayyanat lokacin ma har likita ya xo ya dubata, bata wani kone ba sae dae fatar jikinta da yyi ja ssae.
Sosai ya bata haquri daga ita har inna da abun yabi ya dama har tana cewa a kira mata kabiru, Nasir dae ya dinga bata haquri yace shi zai yi maganin abun amma fafau inna tace ita fa sae taje shima zai kaita gidan da kanshi.
Haka ko akayi dmn tare suka fita shida inna suka bar Rayyanat ita da hurera.
Wani makeken gida suka nufa kyace gidan shugaban qasa ne kan tsari da kyawo irin nashi, kuma ba wani gida bane face gidan su Nasir d'in da kuma su pretty wato qanwar man sbd gabad'ayan su family's ne en wa da qani ne,
Baban su Man shine babba snn mahaifin Nasir bayan shi kuma akwai wani Alhj sa'eed wato qanin mahaifin Nasir inda shi kuma yana da qanwa mai aure a garin kd dukkan su 'yayan inna ne shine maxan suka had'e kansu suna zama gida d'aya sae dai kowa da nasa 6angare.
Suna shiga gidan
inna ta nufi 6angaren su pretty sae ga wata yarinya tazo da murna ta tarbe ta tana fad'in "he inna nida nake batun zuwa gurinki shine kika zo, inna ta washe baki tace "tukuna saukar yaushe Ameera? Yau yau d'in nan aka bamu hutu inna ,to ina er uwar taki saliha? "Tana 6angaren su tare ma ne zamu tafi gurin ki nasan yanzu haka ta shirya tana can tana jirana wlh, inna tace "ayyo to ai yanzu komawa zanyi sae mu tafi tare je kira min Abbanku kabiru yazo ina da magana dashi, tace "to inna zauna na kira miki shi"inna ta zauna ita kuma ta haura sama.
Nasir kuwa wani 6angaren ya nufa da alama shine na iyayensa dmn matar da ya samu zaune a falo sak suke kama dashi, cike da ladabi yaje ya durqusa ya gaisheta yana qoqarin tashi yaji an rungume shi ana fad'in "oyoyo yaya" cike da murmushi yake kallon wacce ta rungume shi yace "A'a saliha shin yau ne hutun ku ko to wa ya d'auko ku?
turo baki tayi snn tace "Abba ne yaje da kanshi tunda kai kaqi zuwa "oh no saliha yi haquri sam na manta da yau ne hutunku amma umma ya akayi ba a sanar dani ba sae Abba ne yaje da kanshi? Mamar tace "Abban ne yace akwai aikinda yasa ka shine ya tafi dakanshi ya d'auko su, Nasir yace "eh gaskiya ya bani aiki tun jiya ban samu na qarasa ba amma inshaAllah yanzu zanje office na kammala kafin ya tambaye ni, nn ya kalli saliha yace "ina zuwa haka naga kinci kwalliya? Tace "Gidan inna zamuje nida Ameera," eyyah ai tare muka zo nida inna tana ma 6angaren su Ameera, Saliha ta 6ata fuska tace "ita ko dai inna...ai ba jimawa zatayi ba dn inaga sae na maida ita gida ne ko zan tafi office ,yauwa bara naje na ganta, cewar saliha wacce ta tashi cikin murna ta fita.
Nasir ya kalli mahaifiyar sa da kulawa yace"umma ina yarinyar da na gaya miki cewa nakaita gidan inna? Hajiyar tace "eh na ji" "wlh pretty yau taje