Showing 96001 words to 99000 words out of 168541 words
Chapter 33 - Bazan Barshi Ba! Complete Hausa Novels By Billy Giro .txt
fa kace?
Eh mana Amir to so kake tayi ta fmn wahala ne baka tsaya ka duba ta ba ka wani zo kana gaya min .
Calm down laulayi ne fa ka sani baya da magani,
Don baya da magani sae a bar yarinya tana wahala gsky ni shiga zanyi koma me zai faru sae dae ya faru! yana gama fad'ar hkn ya tafi fuuu! zai shiga gidan.....
Amir ya riqe sa yace"kaga dakata ai ba wae haka kawae za'a barta ba inna tace idan tasha agwalima abun zai mata sauqi so agwalimar ce aka rasa bcs babu ita a gidn kuma ta kirà nasir ta snr dashi bata same sa ba.
Ni kuma ba sanin inda ake saeda agwalimar nayi ba shiyasa na fito dmn na snr da kai.
Man yace" kaga yi sauri da Allah shiga mota muje koma a ina ne ai ma samota.
Nan suka shiga mota mohd yaja suka tafi sae bin gari suke guraren da ake sae da fruits amma basu samu ba sae can kan hanya suka had'u da mai agwalima man ya tsaida mota suka fito sae gun mai agwalima,
Man yace"malam nawa gabad'aya agwalimar taka take ne "
Da sauri Amir ya kalli man yace"kai kana haukane muda baza mu wuce siyen ta d'ari biyu ko uku ba kake zancen gabad'aya ai sae ta lalace bata kai ga shanye ta ba ma"
Mohd yace"taya zata lalace bayan a fridge za'a zuba kaga malam juye min agwalimar ka kaf a leda ka fad'i kud'in ka na baka"
Dariya Amir yayi yace"haba man aikin hnkli dae"
Snn yace da mai agwalima"malam yi hqr sa mana ta d'ari biyar kawae ta isa"
Nan mai Agwalima ya shiga qirga agwalima yana sakawa a leda yayinda man ya kalli Amir cike da niyar magana Amir ya riga sa da cewa"kar fa ka manta tana can tana fmn yunqurin amai idan muka qara 6ata lokacin mu a nn zata wahala da yawa ne"
Nan man ya fasa maganar da yayi niyya ya maida duban sa gun mai agwalima da ya gama saka ta d'ari biyar a leda ya bawa man ya kar6a yayinda Amir ya ciro dubu d'aya a aljihu ya bawa mae agwalima yace ya riqe canjin kawae,
nn mai agwalima ya washe baki yana musu godiya su kuma suka shiga mota suka bar gurin sae gidan inna.
Wanda da isar su Amir ya fito da sauri riqe da ledar agwalimar ya shiga gidan.
Kusan minti goma da shigar sa ne ya fito ya sami man sae kai komo yake a qofar gidan yana ganin Amir yace"ya ake ciki ne ta daina yunqurin aman? Eh har ma ta shiga bathroom zata d'an watsa ruwa"
A nn man ya fitar da ajiyar zuciya yace"olryt amma dae zamu dawo anjima don na samu naga yanda jikin nata yayi ko"
Amir yace"shikenan Allah kaimu".
Daga haka suka shiga mota suka bar layin.
Ana fitowa masallaci sallr isha'i sae gasu sun dawo gidan ,Amir ne ya shiga wanda bayan en mintina kad'an da shigar sa gidan ne man yaga flash d'insa a nn ya shiga gidan ya nufi d'akin Ryynt kai tsaye ya sameta kwance kan darduma ta idar da sallah idanunta a rufe kmr mae bacci.
Nn yaje ya durqusa gab da ita tare da d'aura hannun sa a kan gefen fuskarta,ta bud'e idonta a tsorace tare da saurin tashi zaune tana kallon shi ya sake mata d'an guntun murmushi ita kuwa lokaci d'aya tasha masa toka dan ta fhmci mohd ne sbd qamshin turaren sa da taji.
Fuskar ta a murtuqe ta miqe zata bar d'akin mohd ya jawota zuwa jikin sa bata yi yunqurin qwatar kanta ba sae goshin ta da tayi saurin kai hannu ta dafe sbd kanta da taji yayi mugun sara mata.
Cikin damuwa mohd ke kallonta dan ya fhmci irin ciwon kan da take d'auke dashi nn ya tafi da ita kan bed suka zauna ya kwantar da kanta a qirjin sa had'e da kai hannu yana murza mata goshin nata a hnkli, Rynt kuwa se hancinta ta shiga cusawa a hnkli cikin rigar sa sbd wani irin qamshin dad'i da taji turaren sa na mata.
Man bae hana ta ba sae kallonta da yake har ta shigar da hancinta gabad'aya cikin suit jacket d'in shi.
Billy giro😊
[10:00PM, 5/2/2017] Billy giro😊: ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```
_wuhuu!Really! Really!!Really!!! appreciate! my dearest family, Aunty zygiro,Nanà giro, Shamsiya giro,Hafsat giro,Apeeya giro n Rayyanat giro wnn page in naku ne and these hearts goes to u ❤❤❤❤❤❤_
🔮🔮🔮🔮
*```Page 62```*
Sun jima a haka d'akin tsit kmr ba kowa mohd ya katse shirun yayin da ya shafo bayanta yace"ina son zanyi magana dake kinji"
Nn yaji shiru ba amsa yakae hannu ya d'ago fuskarta yaga ashe tayi bacci abinta.
ya lumshe idonsa a hnkli yana kallon yanda ta koma maida fuskarta a qirjinsa ta lafe sosai kmr wacce zata sha mamma.
Nan kawae ya d'aura hannun sa kan cikinta yana ta kallonta lokaci mai tsawo se can ya tashi ya kwantar da ita kan bed ya kama hanya zai bar d'akin sae kawae yaji qarar waya nn ya tsaya da d'an mamaki yana kallon wayar Rynt dake fmn ruri kan bedside drawer a hnkli ya qarasa gun bedside drawer d'in ya d'auki wayar yana mae kallon Rynt snn ya kalli mae kiran wato Sarah bayan kiran ya tsinke ne ya danna wasu lambobi ya kira nn wayar sa dake cikin aljihu ta shiga ruri ya katse kiran ta jikin wayar Rynt snn ya maida wayar ya ajiye kafin yake ciro tasa wayar a cikin aljihu yayi saving number d'in Rynt ya fito falo zai bar gidan yana mai jiyo sautin firar inna da Amir .
Bayan ya fita ne Amir dake ta fmn ci gaba da jan inna da fira yaji shigowar text a wayar sa koda ya duba mohd ne ,
sae da ya d'an qara lokaci snn yayiwa inna sallama ya fito ya sami mohd jingine a jikin mota yace"Hope ta amince"
Mohd yace"no ko mgnr ma ban samu nayi da ita ba tayi bacci but i got her number zan kirata sae muyi magana a waya"
Amir yace"to shikenn ai haka ma yafi"
Daga haka suka shiga mota suka bar gurin.
Mohd na komawa gida ya rage kayan jikin sa ya fad'a bathroom wanda sae da ya kwashe kusan awa d'aya kafin yake fitowa sanye da white bathrobe ya nufi fridge ya bud'e ya ciro fresh milk ya tsiyaya a cup yaje ya zauna kan sofa ya jingina bayan sa tare da d'aura qafafunsa kan footstool ya fara shan fresh milk cike da tunanin idan Rynt bata amince da zancen sa ba wace hanyar kuma zai bi.
Yana cikin hakane malika ta fad'o d'akin ya kalle ta kawae ya kauda kai taje gab dashi ta zauna had'e da riqo hannunsa tana kallon sa snn tace"my man umma ce bata jin dad'i shine nake son naje na dubo ta"
Hannunsa ya zare daga nata yana kallonta shaye da toka.
Ta wani maràiraice fuska tace"ba wani jimawa zanyi ba dan ko 10 bazan kai ba pls kaji?
"Ba inda zaki je"
Pls my.....bata iya qarasawa ba sbd wani irin mugun kallo da ya mata had'e da nuna mata qofar fita d'akin.
Rae 6ace ta tashi ta fita d'akin taje d'akinta.
Wacce da shigarta ta jawo wayarta ta kira ana d'aga wayar ne tace"wlh d'an banzan bai bar ni ba ka bari kawae gobe idan ya tafi aiki zan zo na same ka.......tana kaiwa nn ta katse wayar ba shiri tana kallon man dake tsaye a bakin qofar d'akin ,
ya qaraso gurinta yana mata kallon tuhuma snn yace"da uban wa kike waya!?
Malika dake kallon sa a tsorace ta samu da qyar tace"umma ce fa......bana son raini meyasa to da kika ganni kika katse wyr a tsorace iye!
Banga shigowar ka bane sae ganin ka da nayi shiyasa na tsorata.
Cikin kallon tuhumar da yake binta dashi ya kai hannu ya fizge wayar hannunta ya shiga call logs ,sweetheart2 shine last call nata ya kalle ta kawae ya cillar da wayar kan bed ya fita sbd sweetheart shine sunan da tayi saving number d'in mamarta dashi ,
sweetheart2 kuma numbar gayen da ta gama yawa da shine,shine man ya d'auka ko wata number mamar ta sake yi shiyasa ya fita kawae ya barta.
Malika kuwa man yana fita ta dafe qirji had'e da fitar da wani irin numfashi na ganin bae gano ta ba.
Rynt kuwa tana cikin baccinta mae dad'i taji inna tana qwala mata kira ta tashi firgigit tana kallon inna da ta shigo d'akin snn ta kalli inda take kwance tana d'an dube dube a d'akin inna tace"me kike nema ne?
Tace "ba komai"
Inna tace "to tashi muje d'aki ki kwanta ko"
Ba musu Rynt ta tashi had'e da d'aukar wayarta da kuma littafinta da suke da jarrbawar sa gobe don tana son da dare idan ta farka tayi karatu.
Nan suka rufo d'akin suka fito wacce da shigar su d'akin inna ko hijabin jikinta bata iya cirewa ba ta fad'a kan bed ta ci gaba da baccinta.
Ba ita ta farka ba sae
11:40pm ta tashi a hnkli had'e da bisimillah tana miqa taje bathroom bata jima ba ta fito ta koma kan gado ta zauna tare da jawo littafinta ta kunna fitilar wayar ta tana karatu.
Tana tsaka da karatun ne wayar ta ta shiga qara tayi saurin sakata a silent tana kallon numbar da ke yawo akai, d'auke da mamaki a fuskarta na ganin baquwar numbar da bata sani ba kuma da daren nn.
Kiran na gab da tsinkewa ne tayi saurin d'aga kiran dan a take ta shiga tunanin ko Sarah ce.
Sae dai duk da hkn bai sa da ta d'aga wayar tayi magana ba se shiru tayi tana sauraren muryar da zata ji.
A natse taji ance "kin tashi?
Bata ce komai ba sae shan toka da tayi dan lokaci d'aya ta gane muryar mohd ce yayinda ta shiga tunanin a ina ya sami numbar ta,
ya katse ta da cewa"kina jina mijinki ne mohd ina son zanyi magana ta fhmta dake ne kinji"
Kmr yana ganin ta ta qara murtuqe fuska,murya can ciki tace"nifa ynx karatu nakeyi bani da wnn lokacin"
Yace"kun fara exam ne?
A qufule tace"eh"
Yace"olryt gobe zan kira ki idan kin dawo daga school"
Komai bata ce dashi ba ta katse kiran taci gaba da karatun ta.
Washe gari da yamma Rynt na zaune a falo ita da Aamil yana mata tambayoyi akan littafin da zasu yi exam next day.
Wayar Rynt dake ajiye gefe ta shiga qara Rynt ta kalli wayar kawae ta kauda fuskarta don ta fhmci numbar mohd ce Aamil dake kallonta yace"ya baki d'aga kiran ba?
Tace"ba komai kawae bana son in katse karatun da muke yine"
Bae ce komai ba suka ci gaba da aikin su har kiran ya tsinke aka koma kira Rynt ta kalli wayar had'e da kai hannu zata d'auki wayar se kawae wayar ta nuna battery low ta mutu hkn ya mata dad'i dan dama niyyarta tana d'aukar wayar katse kiran zatayi ta kuma kashe wayar gabad'aya.
Aamil da har ya soma jin haushin mae kiran dan hk kawae ransa ya basa cewa namiji.
Ya kalli Rynt kmr wanda zae ce wani abu sae kuma ya fasa suka ci gaba da yin karatun su kawae.
Bayan sun gama karatun ne ta saka wayarta a chaji da dare tana shirin bacci wayar ta ta shiga ruri tana ganin mohd ne mae kiran ta buga tsaki ta d'aga wayar had'e da fad'in"wae me?
Mohd yace"kan me d'azun na kiraki baki d'aga ba da qarshe ma dan kin rainani kika kashe wayar ko"
Komai bata ce ba sae tsaki da tayi ta kuma cillar da wayar kan bed taje taci gaba da shirin baccinta shi kuma se magana yake tayi ba amsa har sae da ya gaji ya tsinke wayar.
Sae da ta gama shirinta tsaf snn ta d'auki wayarta ta fito ta rufe d'akin ta tafi d'akin inna.
Washe gari da safe ta fito daga wanka knn mohd ya kirata kallon wayar kawae tayi ta kauda kai taje ta jawo Vaseline tana shafawa , tana ji har yayi kusan 3 missed calls bata d'aga ba wacce tana gama shirinta ta kashe wayar ta jawo drawer ta saka wayar a ciki snn ta d'auki school bag d'inta ta bar d'akin taje d'akin inna tasha fura a gaggauce ta fita.
Mohd kuwa rashin d'aukar wayar Rynt ba qaramin 6ata masa rae yayi ba shiyasa tun daga rnr bae sake d'aukar wayarsa da sunan kiranta ba har kuwa aka kwashe kusan sati d'aya sae harakar gabansa yake haka ma Rynt wacce yanxu wata irin shaquwa ce ta ban mamaki ta shiga tsakanin ta da Aamil wanda yanzu shi ke kaita school ya kuma je ya d'auko ta wani lokacin ma har d'aukar ta ya ta6a yi suka je shopping da dare ya kwaso mata kaya niqi niqi tamkar bai ta6a sanin meye zafin kud'i ba inna dae sae kallon su take dan duk a tunaninta Aamil tausayawa Rynt ne kawae yake.
Rnr litinin da yamma Man ne tafe cikin mota shida Amir yayinda Amir ke cewa"gsky man ka fiye gajen haquri dan kawae ka kirata taqi ta d'aga sae kawae ka fita harakarta "
Man yace"hm Amir knn ta yaya kake tunanin zan iya fita harakarta bayan ina sonta ina kuma son abinda ke cikinta,just na bata lokaci ne har ta gama nata ikon kafin nake fara nawa ikon.
Amir yace"ta yaya yarinyar da ko saurararka taqi tayi?
Shiru mohd yayi dan baya son kowa yasan abinda ke ransa na d'auke Rynt da zai yi ya tafi da ita waje.
Amir kuwa bae sake ce masa komai ba har suka iso gidan shi ya bud'e gambun motar zai fita Man yace"ka shirya anjima byn sllr isha'i zan zo na d'auke ka ka rakani muje gidan inna"
Gurin Rynt zaka je ne?
Ba tare da ya kalle sa ba yace"eh"
Amir ya fita had'e da fad'in"sae ka zo"snn ya rufe gambun motar ,
man kuwa yaja motar tasa ya tafi.
6angaren su Aamil kuwa Rynt ce ya d'auko daga school ya kawota gidan inna ya ajiye ta wacce kafin ta fita motar sae da ta kalle sa d'auke da murmushi a fuskarta tana mae godiya shi kuma cikin sakiñ fuska ya lumshe ido had'e da ware su a kanta snn yace"ki gaida inna zan shigo anjima "
tace"to"snn ta tafi sae shillo take da ledar agwalimar da ke hannun ta wacce ya saya mata.
Aamil kuwa a maimakon yaja motar sa ya tafi sae kallonta yake tayi cike da tunanin yau zae kawo qarshen haqurin sa dan anjima idan ya dawo kai tsaye zai je ya gaya wa inna abinda ke ransa na game da Rynt koma kawae zae je ya sami Abba ya gaya masa dan inna tasan cewa lallai da gaske yake.
Da tunanin hkne yaja motar sa ya tafi.
Rynt kuwa tana shiga gida tayi wanka taci abinci tayi zaune a d'akinta ta tasa agwalimar ta gaba tana sha a nn ta miqa hannu ta bud'e drawer dan nn inda take zaune da drawer ba nisa ta ciro wayarta ta kunna sae kawae taji shigowar text murmushi tayi ganin Aamil ne ya turo saqon wacce ta san ba komai bane face kati don kullum sae ya turo mata katin dubu d'aya, hkn kuwa na mata dad'i sosai don sae ta kira en uwa da abokan arziki suyita waya wato Sarah da kuma umman saliha wacce bayan sun gama waya da ita sae ta bawa mami,suyi ta waya da Rynt cike da nishad'i suna dariya.
Da dare bayan isha'i Rynt ta idar da sallah ta miqe had'e da linke darduma ta saka a wardrobe ta kai hannu zata cire hijab bata cire hijab d'in ba sae tsaye tayi tana kallon cikin ta da har ya d'an fara turo hijab ,
a hnkli ta d'aura hannunta kan cikin sae kuma tayi saurin d'auke hannun ba shiri sbd motsa mata da taji yayi cikin takaici mai d'auke da alamar zata yi kuka takai hannu tana doka cikin.
Mohd dake tsaye a bakin qofa yana kallonta ya qarasa gurin ta da sauri har yana hard'e qafa ya riqe hannuwanta duka biyu ya kalle ta rae 6ace yace"kinyi haukane idan kika kashe abinda ke ciki fa"
Shaye da toka ta ture shi tace"dan ya mutu sae me ko ce maka akayi dama barin sa zanyi!
A fusace ya fizgota zuwa jikin sa yace"wlh idan har na koma jin kince zaki cire cikin nn zanyi mugun sa6a miki"
Tace"wlh sae na cire cikin nn kayi abinda zakayi"
Rufe bakinta keda wuya taji saukar duka a bakin nata wanda zama d'aya ya 6are da jini ,
sosai ta fashe da kuka tana kallon jinin da ta shafo a hannun ta.
Man kuwa sae farin handkerchief d'insa ya zaro zae share mata d'an jinin da ke gefen bakinta, ta buge masa hannu tana masa muguwar harara tare da fad'in mugu Allah ya isana wlh.
Ta qarashe maganar ne cikin muryar kuka sosai ,komai man bai ce mata ba sae janta yayi tana fmn fizge fizge har yaje da ita kan bed suka zauna taje zuwa tashi ya maida ta had'e da rungumeta yakai bakinsa saitin kunnen ta yana gaya mata magana cikin natsuwa, a nn ta d'ago ta kalle shi tace"da gaske kake yi"
Yace"eh"yayin da ya maida