Showing 99001 words to 102000 words out of 168541 words
Chapter 34 - Bazan Barshi Ba! Complete Hausa Novels By Billy Giro .txt
ta kan qirjinsa ya kwantar,sae ga Aamil ya fad'o d'akin ya tsaya da mugun mamaki yana kallon man da ya d'ago fuskar Rynt zai had'e bakinsa da nata yaga bata hana shi ba sae ma lumshe idonta da tayi har man yakai ga saka harshen sa a cikin bakinta.
Aamil cikin rud'u da kuma mamakin da yake d'auke dashi ya shiga ja baya har ya fita d'akin ya nufi d'akin inna dmn jin shin wace ce Rynt❓
Dan Allah Kuyi haquri da fmn jirana da kukayi tayi jiya kuma sae gashi baku samu ba .
Then
Ku qara min afuwa dmn gobe bazan samu yi ba sbd tafiyar da zanyi.
Luv u all❤
Billy Giro 😊
[10:00PM, 5/2/2017] Billy giro😊: ```🔮BAZAN BARSHI BA!🔮```
🔮🔮🔮🔮
*```Page 63```*
Aamil na fita d'akin Rynt ta zare bakinta cike da jin kunya ta kwantar da kanta a hnkli kan qirjinsa tana shaqar qamshin turaren sa.
Shi kuma mohd sae wani qara kwantar da ita yayi a qirjin nasa yana mae shafa bayanta a hnkli cikin natsuwa.
Aamil kuwa yana shiga d'akin inna ya sami Abba da zuwansa knn ko zama bai yi ba sae Amir da ya samu ya zame kan kujera yana gaida shi bai kula su ba sae gun inna yaje a rud'e wacce taje zuwa bud'e fridge knn yace"inna zan so naji wace ce Rynt kuma ya take da mohd da na gansu a d'aki tare"
Abba dake kallonsa yace"mohd fa kace a gidan nn!
Aamil bai iya cewa komai ba sae kansa da ya gyad'awa Abba cikin rashin fhmtr yanayin da yaga Abba ya shiga ciki wanda yaga ya tafi fuuuu! a fusace yana fad'in lallai kuwa yau zan nuna masa haifo sa akayi ba haifar kansa yayi ba!
A nn Man da Rynt suka tsinkayo muryar Abba tafe hkn yasa suka miqe tsaye zumbur sae ga su Abba,inna, Aamil da kuma Amir duk sun shigo d'akin,inda kai tsaye Abba ya nufi mohd ya watsa masa mari biyu masu kyau ya kuma nuna kansa da yatsa yace"dan uwarka ni zaka mayar d'an iska ko kuwa shima nn gidan ban hanaka shigowa bane iye!
A natse mohd ya kalli Abba cikin damuwa sosai yace"dan Allah Abba....kaga yi gaggawar fita a nn kuma duk ka kuskura na koma ganin qafar ka a nn gidan ko a gidana to kuwa zan furta abinda baka ta6a tsammanin zan furta a gare ka ba!
mohd ya kalli Abba d'auke da idanuwansa da suka kad'a sukayi jajur yace"dan Allah Abba kayi haquri ka saurare ni wlh nazo ne dmn na bawa Rynt haquri na maida ta..... Kul!har abada Rayyanat baza ta ta6a komawa gare ka ba don ba shashashan mutum bane ni da zan aura ma ita ka sakota ka kuma yi tunanin zan barka ka maida ta,
Mohd yace"Abba itama fa tana son komawa"
Nan Abba yayi saurin kallon Rayyanat wacce ke kallon mohd shaye da toka yace"Rynt abinda yace hakane?
Ta kauda fuskarta da kallon da take yiwa mohd had'e da girgiza kanta snn tace"Aa Abba gsky ni bana son komawa"
Abba ya kalli Man dake kallon Rynt yace"maqaryacin banza shashasha fita a nn in daina ganin ka!
Mohd da ya duqar da kansa qasa yace"pls Abba dan Allah ko don abinda ke cikinta ka bar ta ta koma"
Kafin Abba yace "komai Inna ta riga sa da cewa" bafa zata koma ba shashasha marar mutunci idan har dan abinda ke cikin ta ne da ta haife shi zata baka abunka kaje can ka qarata dashi dan baza ta raina maka shi ba karatun ta zata ci gaba dayi.
Abba yace"Ba ma wnn kad'ai ba inna Aamil yaje min da wani zance na yana son zai auri Rynt na kuma yi na'am da zancen nasa dmn Aamil mutum ne da nsn zae riqe ta amana ko da kuwa ace baya sonta aka aura mae bare shi da kanshi yace yana so da haka na yanke shawarar idan Rynt ta haifu zan had'a aurensu sae taci gaba da karatun ta a can d'akinta.
Tun lokacin da Abba ya fara zancen sa mohd ya shiga wani irin tashin hankali yana kallon Aamil cikin mugun mamaki haka ma a gurin Amir ,Rynt kuwa banbarakwae taji zancen ta bud'e ido tana kallon Aamil yayinda Aamil duk ya sukuikuice yana kallon Abba cike da son cewa wani abu.
Sae dae kafin suce komai sae kukan kura suka ji mohd yayi zai afkawa Aamil Abba ya dakatar da dashi ta hanyar ture shi had'e da kife sa da mari yace "dan uwarka borin kunyar ne zaka saukar akanshi dan zae min abinda kai ka kasa min,to bari kaji Aamil yafi min kai sau dubu dmn yau ya yaye min duk wani baqin ciki da na shiga a knka,kuma aure shida Rynt ba fashi!
A nn Idanuwan mohd suka qara yin jajur har ana hango jijiyoyin goshinsa duk sun tashi yace"Abba wane irin zance ne wnn ace Aamil zai auri Rynt....gaya min inda yake haramun dan Aamil ya auri matar da ka saka!
Kmr zae yi kuka yace"haba Abba wnn ai abin kunya ne aji cewa wae Aamil zae auri matar da na saka kuma ai Abba ni wlh na mai......cikin daka tsawa Abba yace"kaga maza fita bana son sake jin zancen ka a nn idan ba haka ba wlh kasan sauran shashasha kawae!
Mohd bai iya fita ba sae wani irin mugun kallo da yake yi wa Aamil kmr zae je ya bugoshi dan jikin sa har ya soma rawa ma sae Amir ne yayi saurin jan hannunsa suka fita yayinda shi kuma Aamil yaja hannun inna suka tafi d'aki,Abba kuwa gun Rynt ya tsaya dmn jin ra'ayin ta wacce ya kalla a natse yace"Rynt gaya min gsky kina son komawa gidan mohd koh?
Tace"wlh Abba bana so"
Yace"to kina ganin zaki iya auren Aamil bayan kin haifu?
Shiru tayi sbd shirin da take yi da Aamil muqaddari ne da ta samu kanta dashi haka kuma bata da tabbacin wanda ya kashe mata baffanta a cikin su ukun ,
kawae dai tafi zargin cewa mohd ne.
Abba dake kallonta jin shirun yasa ya bud'e baki zuwa magana sae kawai wayar sa tayi qara ya ciro wyr a aljihu ya d'aga yayinda ni kuma na garzaya gun su inna dmn jin abinda Aamil zai ce da inna.
Cikin yanayin damuwa sosai na samu Aamil yana cewa da inna"inna wlh kwata kwata ban gane cewa Rynt matar man bace shiyasa naje wa Abba da zancen cewa ina son zan aureta, ba wae dan nasan cewa sun rabu ba"
Inna ta sauke numfashi tace"to Aamil ynx dan kaji cewa mtr da muhammadu ya saka ce meye matsala ko kuma sonta ne kaji ba kayi da kaji cewa ta ta6a aure har tana d'auke da juna biyu"
Ko d'aya inna ba ciki ba ko 'ya'ya goma ne da Rynt ni mae iya aurenta ne amma kasancewar ta mtr da man ya saka ce yasa bazan iya auren ta ba inna"
Aamil inace ba haramun bane dan muhammadu ya saki Rynt ka aura ,
Aamil yace"duk da haka dae inna ana barin halak dan kunya dmn man jini na ne da bazan iya masa haka ba"
Inna tace"Dan muhamadu yana jinin ka shi kuwa ubanka kabiru da yake ikirarin ka wanke mai baqincin da yake d'auke dashi fa ko kowa kaima so kake ka watsa mae qasa a ido ne iye!
ko d'aya inna bana son haka amma na fi son Abba ya haqura ya bar man ya maida matar sa tunda har ya nuna yana son maida ta"
Inna tace" Rynt fa bazata koma gidan muhammadu ba dan kaji in gaya ma idan kai d'in bazaka aureta ba ai bazata rasa wani masoyin ba"
Aamil ya fitar da numfashi yace"dan Allah inna me yasa ba kwa son ta koma ne?
Ajiyar zuciya inna ta sauke kafin take bashi kaf labarin abinda ya faru tsakanin man da Rynt.
Nan Aamil ya jima shiru yana tuna lokacinda inna ta mari man har abin ya d'aure masa kai wanda sosai yaso yaji dalilin faruwar hakan amma kuma sae bai san ya akayi bae tambayi dalilin ba,haka kuma ya tuna lokacinda ya shiga d'akin Rynt ta mai ihu a tunanin ta man ne kuma duk ta ganshi sae taji waye tukun kafin take sakewa dashi,ko hkn kad'ai abune da ya kamata ace ya fhmci wani abu amma kuma sae bai fhmta ba ,sae yanxu da inna ta bashi lbr.
Aamil ya ajiye tunanin sa da kallon inna yace"a gsky inna mohd bai kyauta ba amma tunda yayi nadama ayi haquri abar shi ya maida ta"
Inna tace"yo wa ya gaya ma nadama ce yayi kawae yana son abinda ke cikin Rynh ne dmn na tabbatar idan muka barta ta koma to kuwa ina gaya ma da ta haife mae abinda ke cikinta zaici gaba da wulaqanta ta ne,amma kai nsn zaka riqe Rynt amana tun da har ka iya riqe khadija tsawon lokaci ba'a ta6a jin kanku ba duk da kuwa cewa auren had'i ne a tsakanin ku da ita ba wae dan kuna son juna ba.
Aamil kam baya ko jinta dan yayi shiru yana tunanin shidae a ganin sa mohd ba don cikin sa kad'ai ne yake son Ryynt ta koma ba,dmn ya fhmci sosai mohd ya shiga damuwa a lokacinda Abba yace idan Rynt ta haifu zai had'a auren sa da Rynt.
Kuma ko abinda ya samu yana mata a d'aki abune dake nuna soyayya a tsakanin su, sae dai kuma Rynt d'in ce da ban mamaki da tace bata son komawa gidan mohd ko meyasa?
Baya da amsa kan dole ya sauke numfashi ya kalli inna yace"shike nn inna zan yi shawara"
Inna ta washe baki tace"to ko kaifa d'an albarka"
Shidae Aamil komai bai ce ba sae fita da yayi ya had'u da Abba ya fito d'akin Rynt ya sadda kansa kawae ya wuce zuwa d'akin Rynt Abba kuwa ya shiga d'akin inna,wanda sae da ya nemi guri ya zauna snn ya kalli inna dake zaune kan gefen gado wacce ke kallon sa tana fad'in"da kmr magana ka tsaya yi da Rynh ko?
Abba yace"eh inna hkne na tambaye ta ra'ayin ta ne kan had'a aurenta da Aamil sae bata iya cewa komai ba tamin shiru, daga baya da nace ko bata ra'ayin auren ne, tace ita a gsky tafi so tayi karatu, nace indai karatu ne kar ta damu dmn Aamil mai barinta ne ta qarasa karatun ta cikin jin dad'i da kwanciyar hnkli amma idan tafi son sae ta kammala karatun to,
sae ta min shiru kuma bata ce komai ba shine na fito na barta dmn na fhmci shawara take a ranta kmr wacce na fhmci yanzu tsoron aure take ganin irin wahalar da tasha a gun mohd shine take ganin kmr duk inda taje hkne.
Inna tace"dole ne fa tayi wnn tunanin amma ni mai fhmtar da ita ne sannu sannu har ta fahimci cewa ba duka a aka taru aka zama d'aya ba.
Abba yace"to shikenn inna ni zan tafi Allah sa a dace"
Tace"Amin d'an albarka Allah kiyaye hanya a gaida gida yace"to"snn ya fita.
Aamil kuwa a lokacin da ya nufi d'akin Rynt sae da yayi sallama Rynt ta amsa mar snn ya shiga ya sameta zaune gefen gado kanta qasa yace"Rynt dan Allah kiyi haquri sam ban gane ki ba bare na fhmci cewa ke mtr man ce shiyasa kika ji wani irin zance a bakin Abba da yake farin ciki da shi amma ni tunda na fhmci wace ce ke banida farin cikin da ya wuce ki koma d'akin ki, kiyi haquri ki manta komai kije ku gina sabuwar rayuwa keda man dmn nafhmci dgske yake son maida ke sbd irin damuwar da naga ya shiga a yau ban ta6a ganin sa a cikin irin ta,kuma ko don qaruwar da ke tsakanin ku ya kamata ace kinyi haquri kin koma kinji"
Muryar can ciki tace"to"
Dan kawai ta samu ta huta dashi dmn ita sam bata son jin ana zancen qaruwar da suka samu tsakanin ta da man abinda ko yaushe ftr ta taga an cire cikin ta huta amma sae wani zancen sa ake mata.
Aamil dake kallonta yace"naje na gaya ma Abba kin amince zaki koma gidan mohd d'in?
Tayi saurin kallon sa had'e da girgiza kai snn tace"sae nayi shawara tukun"
Yace "shikenn idan kin gama yanke shawarar sae ki gaya min"
Ta gyad'a masa kai kawae shi kuma ya fita ya bar d'akin.
6angaren su mohd kuwa a lokacin da Amir yaja shi suka fita da qyar ya samu mohd ya shiga mota wae a cewar yau in shi in Aamil dole a kwashi gawar d'ayan su don ba zai ta6a yarda ya auri Rynt ba sae dai ko idan da gawar Aamil za'a d'aura auren to zae gani.
Shine Amir ya samu da qyar da lallami ya kaisa gida ya dawo kan hnya sae mamakin Aamil yake da kuma mamakin Abba da ya yarda zai ba Aamil Rynt ya aura.
Guraren goma Amil ya tafi gidan Amir wanda yazo masa shaye da toka yana kallon sa Aamil ya sadda kansa qasa kawai ya shiga mai bayanin komai kan cewa shi bai san cewa Rynt mtr man bace shiyasa yajewa Abba da zancen yana son zai aureta ba wae dan yasan sun rabu ba.
Tun lokacinda Aamil ya fara zancen sa Amir ke kallon sa da mamaki se can yace"shine matsalar kai kwata kwata ba ruwanka da kowa bare ka san wnn waye ya kuma yake damu abinda kasa ma gaba kawae ka damu dashi wace irin rayuwa ce wnn kuma inace damu akayi bikin su kuma har gidan sa munje byn auren wanda muna zaune ta biyo ta wuce har ta gaida mu,haka ma a gidan inna mun had'u da ita ka sani,
Aamil yace"Amir wlh sam ban gane ta ba kawae dai d'ayar matar sa na sani malika da dama nsnta kafin auren.
Amir yace"to naji yanzu ya kake so ayi bayan duk kabi ka qara lallata komai"
Wàto Amir so nake ka raka ni muje gurin man na masa bayani na kuma basa haquri.
Amir ya girgiza kai snn yace"let tomorrow dan yanzu idan mukaje komai zai iya faruwa sbd ransa a 6ace yake sosai ba zai ta6a saurararka ba.
A sanyaye Aamil yace"shikenan Allah kaimu goben"
Amir yace"Amin"
Snn sukayi sallama kowa ya kama gabansa.
Washe gari da safe Rynt ce cikin shirin makarantar ta tsaf riqe da kofin tea a hannunta ta kasa sha don tun jiya har yau ta kasa sakewa sae tunani take tayi inna kuwa lalla6a ta shiga yi ta samu har tasha tean byn ta gama sae ga Aamil ya shigo gidan zai kaita school wanda ba don komai yake son ci gaba da kaita school ba sae don ya samu ya riqa bata magana har ta amince da komawar ta gidan man .
Inna na ganin Aamil ta washe baki suka gaisa cikin sakin fuska yayinda Rynt ta gaida shi ba yabo ba fallasa.
Snn suka fito suka kama hanyar makaranta.
Suna cikin tafiya ne sae kawai Aamil yaga motar man tasha gaban su kai tsaye har sae da yayi saurin cije birki ya tsaida motar ya fito yana kallon d'an uwan nasa da ya fito cikin mota a fusace,nn ya tafi zai qarasa gurinsa cike da niyar mai bayani man bai saurara masa ba sae kukan kura da yayi ya cakumi collar rigar sa had'e da kai sa ya manna sa jikin mota ya kuma shaqe mai wuya da hannunwansa duka biyu.
Aamil da bai ta6a tunanin abinda mohd zae masa ba knn sae qoqarin qwatar kansa ya shiga yi amma ya kasa nn Rynt ta fito mota a tsorace ta nufo su tayi tsaye a rud'e tana kallon yanda man ya shaqe Aamil da har idanuwan sa sun fara firfitowa,ai kuwa nn ta shiga ihu tana neman taimako.
Da qarshe ganin ba sarki sae Allah taje da kanta ta fizgo hannun mohd zata janye shi daga jikin Aamil bata iya janye shi ba sae abun hannu taji ta sa6ulo a hannun sa had'e da wani irin turi da mohd ya mata wanda bata an kara ba sae jin kanta tayi kamas! mota ta banke ta, nn ta saki wani irin ihun da yasa mohd ya jiyo cikin muguwar razana yayo kanta ya kwashe ta a rud'e ganin yanda jini ke fita a kanta yaje ya sakata a mota yaja motar aguje ya tafi ba tare da ya damu da sanin wanda ya kad'e ta ba da kuma Aamil da ya bari riqe da wuyan sa yana fmn tari.
Billy giro
[10:00PM, 5/2/2017] Billy giro😊: 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮
🔮🔮🔮🔮
*```Page 64```*
Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!
shine kake taji a bakin mutum biyu wato Nasir da Amir da sune suka fito cikin motar da aka kad'e Ryynt da ita wanda koda suka fito tuni man ya fice da Ryynt sai gun Aamil suka nufa da ke durqushe kan guiwoyinsa yana fmn ci gaba da tari.
A nn Nasir ya bud'e motar Aamil ya d'auko ruwan gora a mota ya ba Amir dake riqe da Aamil a cewar ya ba Aamil ruwan se su hanzarta zuwa asibiti dmn ganin halin da Ryynt ke ciki.
Bayan Aamil yasha ruwan ne suka d'aunguma gabad'ayan su se asibiti.
Wato Man specialist hospital inda kai tsaye A&E ward suka nufa suka samu an riga an shiga da ita zuwa dubata nn suka zauna zaman jiran a fito da ita, sae yi suke suna safa da marwa musamman Amir da shine ke tuqa motar koda abin