Showing 102001 words to 105000 words out of 168541 words

Chapter 35 - Bazan Barshi Ba! Complete Hausa Novels By Billy Giro .txt

14 Jan 2025

9859

ya faru.




Bayan awa d'aya da faruwar haka ne,inna Abba,Nasir, Aamil da kuma Amir zaune suke zugum a d'akin da akayi admitting d'in Ryynt wacce har an fito da ita sae jiran farfad'owarta suke yayinda mohd ke gefenta zaune cikin damuwa yana kallon fuskarta d'auke da goshinta da akayi rolling da bandage.
Yana cikin kallonta ne ta shiga motsi a hnkli had'e da fara ware hannunta da ke jimqe riqe a hannun man dashi kansa bai lura hannun nata a jimqe yake ba sae da yaji tana yunqurin ware hannun nn ya saki hannun a hnkli yana kallon hannun nata da take ci gaba da warewa har ta ware sa gabad'aya nn yaga ashe abin hannun sa ne riqe a hannun nata, ya d'ago yana kallonta ita kuwa sae kallon abun hannun take wanda sak irin wanda ta tsinta ne a tare da kud'in da aka jefawa baffanta,
a hnkli
ta d'ago ido sukayi 4 eyes ita da man wacce take idanuwanta suka ciko tap da qwalla har ma suka soma gangarowa gefen fuskarta.
Cikin tausayi mohd ya kai hannu zai share mata hawayen ,tayi saurin tashi zaune had'e da fad'in"wlh kar ka ta6a ni!mugu dama kai nake zargi kuma sae gashi kuwa tabbas kai d'in ne wlh ina gaya ma bazan barka ba sae na d'auki fansar abinda kayiwa Baffana ko da kuwa zan rasa raina.
Tana kaiwa nn ta had'e kai da guiwa had'e da fashewa da wani irin kuka mohd ya shiga kallonta cikin rashin fhmtar abinda tace,
haka ma su inna dake zagaye dasu wani iri suka ji zancen nata.
Abba yace"mohd me take cewa ne da kayi tsaye kawai kana kallonta"
Abba ya qarashe maganar ne yayinda Rynt ta d'ago da sauri tana kallon su d'aya bayan d'aya dan kwata kwata bata lura cewa akwai mutane a d'akin ba ta d'auka ko su kad'ai ne ita da mohd.
Tana cikin kallon su ne ta tsinkayo muryar mohd yana cewa"Abba nima ban fhmci inda zancen nata ya nufa ba asali ma tsoro nake idan ba wata matsala ce ta samu a qwaqwalwarta ba dmn zancen nata yayi kama da hkn.
Nan kawai suka ji inna ta fashe da kuka tana fad'in innalillahi wa inna ilaihi raji'una na shiga uku yau Rynh wace irin qaddara ce ta same ki da safiyar nn haka.
Rynt dake kallon mohd rai 6ace kan mgnr da taji yayi,
tayi saurin kallon inna tace"Allah inna ba abinda ya sameni lafiyata qalau ya fad'a ne kawae dan wlh ya duk san abinda nake magana akai"
Mohd yace"Rynt ni kuma wlh ban san abinda kike magana akai ba yi min bayani ta yanda zan fi fhmta kinji"
Wani irin kallon takaici tamai yayinda shi kuma yake kallonta with innocent face d'inshi.
Abba dake kallon su yace"kaga mohd nsn hlnka sarai ka iya maida mutane shashasha tun d'azu da muka zo muke tambayar ku dalilin faruwar wnn accident d'in nata amma kunqi gaya mana sae ce mana da kukayi qaddara ce yanzu kuma tazo da wani zancen kace kai baka sani ba bayan ba makawa kasani don nsn hln Rynt bata da banzar tabi'ar yin qarya"
Mohd ya kalli Abba yace"wlh na rantse Abba ni ban san me take magana akai ba"
Cikin muryar kuka mai d'auke da takaici Rynt tace"wlh ka sa....bata qarasa fad'a ba sae ihu da ta fasa tare da saurin dafe cikin ta,
a rud'e mohd ya matsa gab da ita zai riqota,ta sauka kan gadon ba shiri har tana qoqarin fad'uwa sae inna ce tayi saurin tarbo ta zuwa jikinta inda cikin tsananin 6acin rai inna ta kalli mohd da ya nufo su tace"kar ka kuskura kace zaka matso nn shashasha marar mutunci.
Cikin nuna damuwa mohd ya kalli Abba yace"dan Allah Abba a barni na dubata idan ba wata matsala bace cikin ya samu"
Abba yace"ko matsalar ce ai kai ka jawo shashasha kawai.
Nan mohd yaje zuwa sake magana Abba ya watsa masa mugun kallo kafin yake maida dubansa gun inna wacce taja Ryynt suka zauna kan bed yaje gab dasu cikin kulawa yace da Ryynt "a kira likita tazo ta dubaki ?
Ryynt wacce dama motsin cikin ne kawae ya sata ihu,
ta girgiza kanta tace"a'a Abba ba wata matsala bace dama"
Inna tace" Aa fa Rynh kin tabbatar"
ta gyad'a mata kai had'e da kallon man shaye da toka nn kawae ta fashe da wani sabon kuka sbd jin tayi komai ya dawo mata sabo har tana mamakin rashin imani irin nasa ta yanda ya kashe mata mahaifi wanda ya rage mata qwaya d'aya tal a duniya.
Nan fa taci gaba da kuka sosai inna na bata hqr amma bata iya daina kukan ba sae ma qaruwa da yake.


Inna ta kalli mohd dake tsaye a sukuikuice yana ta kallon ryynt,
Cikin 6acin rae tace"ja'irin yaro wae me ka mata ne kasa er mutane sae kuka take tayi ne iye!
Yace"inna nifa na gaya muku ban san me na mata ba"
Abba yace"kaga wlh kar ka maida mutane shashashu kan me to zata zauna tana irin wnn kukan hk "
Mohd yaje zuwa magana Abba bai barshi ba sae fad'a da yaci gaba da yimae sosai.
A nn ran mohd ya soma 6aci yace"haba Abba wae ya za'a yarda da shirmen zancenta ne nikam kawai a barni na duba ta tukun idan ba wata matsala ce ta samu a qwaqwalwarta ba idan kuma har dgske take cewa lafiyar ta qalau ai sae tayi bayani ta yanda kowa zai fi fahimta ba wae ta wani cumuimuye magana azo anata ganin laifi na a kan abinda sam banida masaniya akanshi.
Rynt dake kuka ta miqe tsaya tana kallon sa da idanuwan ta dake d'auke da tsanar sa qarara wacce taso ace ta bar abin daga ita sae shi amma ya soma kaita qololuwa ta yanda bazata iya barin abun ba har sae ta fallasa sirrin,duk da cewa tasan idan ta snr dasu ba lallai bane su barta ta d'auki fansar abinda tayi niyya amma tunda tana da evidence ko ta hanyar hukuma ne sae ta nemi fansar ta.
Nan ta kauda fuskar ta ba tare da tace dashi komai ba sae duban ta da ta maida gun Abba da inna kafin ta iya ce musu komai sae hawaye taji suna silalowa a hnkli kan kumatun ta inda cikin sanyin murya mai d'auke da rawar kuka tace"Abba ,inna, ina roqon ku da kuyi haquri da jin abinda zai fito bakina da kuma jin ainihin dalilin da yasa na zauna ina rayuwa tare da ku,nn wasu hawaye suka sake gangarowa akan fuskarta snn taci gaba da cewa"inna a gsky ina rayuwa daku ne kawai dmn d'aukar fansar abinda mohd ya min wato na kashe min baffana na da yayi"
ta qarashe mgnr ne had'e da fashewa da kuka yayinda mutanen d'akin suka ji zancen nata kmr saukar guduma a kunnen su inda cikin gwalo ido mai d'auke da tsananin mamaki kowa ke kallon mohd yayinda shi kuma mohd ya dasqare guri d'aya ya saki baki yana kallon Ryynt cikin fiddo ido mai d'auke da mamaki,
wanda kowa a gurin ya kasa cewa komai sae Abba ne yayi qarfin hln cewa"innalillahi wa inna ilaihi raji'un mohd me zanji!
Cikin rud'un da Mohd yake d'auke dashi yayi saurin girgiza kansa yace"No Abba wlh kwata kwata zancen ta ba gsky aciki kawai nafi yarda cewa accident d'in nn ya bawa qwaqwal war ta matsala, abarni na dubata dan Allah Abba"
Abba ya kalli Rynt wanda kafin yace komai ta riga sa da cewa"Aa Abba abinda nake so shine dan Allah muje gida gabad'ya mu dmn na nuna muku shaida ta ta yanda zaku fi fhmtar cewa da hnkli na nake zancen nn"
Ta qarashe mgnr had'e da kai hannu ta share hawayen da ke kan fuskarta.
Abba kuwa bai musa mata ba suka d'unguma gabad'ayan su har su Aamil sae zuwa gidan inna.
Bayan sun isa ne Ryynt taje sae d'akinta ta d'auko kud'i da abin hannu irin na man tazo zata bawa Abba wanda kafin ya kar6a Aamil ya miqe xumbur cikin tsananin tashin hnkli yana kallon abun hannun da kuma kud'in.






Billy giro😊
[10:00PM, 5/2/2017] Billy giro😊: 🔮```BAZAN BARSHI BA!```🔮






























🔮🔮🔮🔮
*```Page 65```*
Bai iya ci gaba da tsayuwa ba sae jin yayi ya zube qasa kan guiwoyin sa yana ci gaba da kallon kud'in yayinda idanuwansa suka kad'a zama d'aya sukayi jajur snn bakinsa ya shiga rawa kmr zai ce wani abu amma ya kasa sae kansa da ya dafe had'e da rufe idanun sa yana mai tuna komai sak yanda ya faru.
Nan kowa yayo kansa yana tambayar Aamil lafiya me yake faruwa,
kuka ya fashe dashi sosai ,
ya bud'e ido yana kallon Abba dake gaban sa dafe dashi riqe da kud'in da abin hannun da Ryynt ta bashi a nn ya rumtse idon sa da sauri dan ko kad'an baya son ganin kayan.
Abba ya ajiye abubuwan da sauri yana tambayar lafiya Aamil wani abu ya sami idanun naka ne?
Bud'e idanuwan nasa yayi yana kallon Abba cikin kuka yace"Abba nine wlh ba mohd bane nine Abba.......kaine me Aamil?
Cikin rawar murya Aamil yace"Abba nine na kashewa Ryynt Baffanta!
Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!!!
shine abinda kowa ya shiga fad'i ba adadi akasin Ryynt da komai ta kasa cewa sae ja baya tayi da qarfi tana kallon Aamil d'auke da hawayen da suka zubo mata kai tsaye kmr yanda shima yake kallonta da nashi hawaye akan fuskar sa.
Nan kawai ta fashe da kuka ta tafi da gudu zuwa d'aki man ya tashi da sauri ya bita sae dai bai iya shiga d'akin ba sae jikin qofar ya tsaya sbd tasa makulli ta rufe d'akin amma ana jiyo tsaf sautin kukanta sbd a nn jikin qofar ta zame tana kuka.
Aamil ne yazo ya sami man tsaye a bakin qofar ya gurfana kan guiwoyin sa ya rungume qafafuwan man cikin kuka yace"i beg u yhu ka bata haquri wlh ba a kan hnkli na nayi kisan ba qaddara ce......
Abba ne yazo a fusace ya tada shi tsaye ya kifa masa wawan mari yace"wace irin qaddara ce wnn Aamil ko ka fara shaye shaye ne ban sani ba!
Aamil yayi shiru dmn tabbas ba zai ta6a mantawa ba yafi to daga gurin shaye shayen sa ya kad'e Baffan Ryynt.
Abba ya daka mai tsawa yace "dan uwarka gaya min garin ya ka kashe mata mahaifi kuma akan wane dalili!
Aamil yace"Abba qaddara ce wlh ba nayi kisan da niya bane asalima ban san cewa ya mutu ba"
Kaga bashi nake son ji ba ka gaya min ta yaya akayi har ka kashe mata mahaifi?
Ba musu Aamil ya gayawa Abba komai yanda abin ya faru ba tare da ya 6oye masa komai ba har magagin giyar da yake ciki kuwa duk sae da ya gaya mae.
Innalillahi wa inna ilaihi raji'un shine abinda Abba ke ta furtawa, yayinda ya cire hular kanshi yana fifita ta a jikin sa sbd wani irin zafin bala'i da gumi dake tsastsafo mai ta koina a jikin sa had'e da wani irin ciwo da yake ji ta 6angaren zuciyarsa,
ya dafe gurin da sauri yaje zuwa fad'uwa Nasir da man sukayi hanzarin tarbarsa inda a rud'e suka tafi dashi kan doguwar kujera suka kwantar ,
inna ta tafi cikin rud'u da firgici ta bud'e fridge ta ciro ruwa ta kawo musu suka yayyafa masa.
Amma bai farfad'o ba sae d'aukar sa sukayi zuwa asibiti yayinda man da Amir ne ke kansa har suka samu ya farfad'o suka mai allurai ciki har da ta bacci.
Koda suka fito suka sami inna sae kuka take tana fmn sirfawa Aamil zagi yayinda Nasir ke gefen ta yana ta fmn lallashi wacce tana ganin su Amir sun fito ta nufe su tana tambayar halin da Abba ke ciki nn suka nuna mata ba wata matsala bace dan har ma ya farfad'o sun mai allurar bacci,
a nn ta nemi ta ganshi basu hanata ba suka barta ta shiga tare da Nasir yayinda su ma suka juya zasu bi bayansu sae ga hjyr su da man ya kira tazo cikin rud'u tana tambayar sa abinda ya faru da Abban su,
Man yayi shiru kawae yana kallonta ya kasa ce mata komai sae Amir ne ya bud'e baki yace"umma muje dae kiga Abba tukun"
Bata musa musu ba tabi bayan su suka shiga dan dama ta matsu taje ta ganshi.
Ta sami Nasir ya jawo wa inna kujera ta zauna nn gefen gadon da Abba ke kwance akai.
Ta qarasa ciki tare da gaida inna yayinda ita kuma nasir ya gaida ta ta amsa tana mai kallon Abba dake kwance yana bacci ,
ta sauke numfashi tana ci gaba da kallon sa snn ta kalli su man tace"na tambaye ku tun a waje me yake damun sa baku gaya min ba sae cewa kukayi na shigo na ganshi"
Amir ne ya sadda kansa qasa cikin jimamin baqin cikin abinda zae snr da ita ya d'ago had'e da share er qwallar baqin cikin da ta fito masa ta gefen ido snn ya shiga snr da ita lbrn komai abinda ya faru cikin nuna baqin ciki da damuwa"
Yana gama bata labarin ne kafin tace komai sae Aamil ta hango tsaye a bakin qofar d'akin yazo gab da ita ya durqusa a gabanta d'auke da idanuwan sa da sukayi jajur kan kuka,ita kuwa sae kallon sa take cikin mugun 6acin rae yace"umma ki yafe min,a yau nayi babbar nadamar qin daina abinda kika hana ni wato shan giya da ke kad'ai kika sani sae kuma Amir,kuma kunyi iya bakin qoqarin ku na ganin na daina amma sae na kasa har takai ga na aikata babbar 6arna,wacce tun daga rnr wlh ban sake yarda nasha giya ba umma duk da cewa ban san nayi kisa ba amma ko kad'an banji dad'in abinda ya faru ba a lokacinda hnkli na ya dawo gare ni wanda tun daga rnr nake fmn istigifari a gurin ubangiji na ina neman yafiya a gurin shi,dmn dama tun farko bada niya na fara ba sharrin frnds ne da kuma sharrin shaid'an da har ta kai ga na aikata abinda har mutuwa ta ba zae ta6a kankaruwa ba.
Ya qarasa maganar ne cikin muryar kuka mai qunshe da baqin ciki,
umma kuwa sae kuka ta fashe dashi tace"lallai Aamil ka riga ka cuci rayuwar ka tun farko sae da na gaya maka wnn banzar tabi'ar sam bata dace dakai ba ka daina ta amma kaqi yanzu gashi ka aikata abinda har mu mutuwar mu baza mu manta ba ,ka 6ata mana suna ka wulaqanta mutuncin gidan ku da kaf dangi ma baki d'aya,
shashasha kawae fita a nn in daina ganin ka!


Hawaye ne suka sailalo a hknli kan kumatun sa snn ya kama hanya ya fita d'akin jiki sanyaye.
Nan man ya kama hanya zai fita d'akin, umma ta takadar dashi ta hnyr cewa "ba dai bin Aamil d'in zakayi ba"
man ya girgiza kansa yana kallon ta sbd shi ba inda zae je ba knn gun Ryynt yake son ya tafi.
Bata ce dashi komai ba sae Abba ta kalla da ya soma tari wanda ya bud'e idonsa a hnkli had'e da tashi zaune ,
umma ta qarasa gurin sa tana mai sannu haka ma inna da su Amir duk suka mae sannu yayinda Man yaje ya kawo masa ruwa had'e da masa sannu Abba ya kar6i ruwan yasha.
Bayan ya gama shan ruwan ne ya kalli man yace"Ryynt fa?
A hnkli man ya sadda kansa qasa yace"tana gida"
Nan Abba ya maida duban sa gun nasir yace"je ka zo min da ita"
Nasir yace"to"snn ya fita d'akin wanda ya d'an jima kafin yake dawowa suka shigo d'akin shida Ryynt wacce kallo d'aya zakayi mata kasan taci kuka har na fita rai don duk idanunta sun kumbura sunyi jajur tayi tsaye kawae a bakin qofa kanta qasa ta kasa kallon kowa.
Abba dake kallonta yace"qaraso daga ciki Ryynt"
Cikin tako mai natsuwa ta qarasa gurin Abba wanda ya kalleta da kulawa yace"Ryynt ko kad'an banji dad'in abinda kikayi niyya ba amma kuma banga laifin ki ba dmn babban mai laifi shine Aamil da duk shine yayi silar haddasa faruwar komai ,
ya haddasa miki baqin ciki da quncin rayuwar da kika shiga a matsayin ki na er qaramar yarinya da har yasa kika yi tunanin abinda bai dace dake ba,da hk nake son kiyi haquri ki ajiye wnn tunanin ki bar komai a hannu na dmn nida kaina zan sa a kama Aamil a kuma yanke masa hukunci dae dai dashi ta yanda duk wani mai banzar tabi'a irin tasa bazai ta6a sha'awar aikata abinda ya aikata ba.
Girgiza kanta tayi had'e da share qwallar da suka zubo mata tace"Abba ka barshi,
dama duk a tunani da gayya yayi kisan shiyasa na d'auki wnn alqawarin wanda na d'auki
alqawarin ne cikin baqin ciki da jin zafin yanda aka kad'e Baffana da kuma sanin cewa ko na kai qara a hukuma ba lallai bane abi min haqqina a wnn lokacin kasancewar mu talakawa en qauye da ba'a d'auke mu a bakin komai ba shiyasa amma ni ynx na yafe masa Abba"
Abba ya girgiza kansa yace"ai ba ubanda ya ake sa shan giyar dn hk sae na nuna masa kuskuren sa ta yanda zaiyi babbar nadamar fara shan giya a rayuwar sa"
Ryynt ta sake share qwallar da suka zubo mata tana tunanin hallaci irin nasu tace"Abba dsgke na yafe masa kawai ka barshi"


Abba yace" ko d'aya Ryynt ke yarinya ce mai kirki da mutunci da ya zama dole abi maki haqqin ki kan zaluntar da ya miki,dmn ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login