Showing 126001 words to 129000 words out of 155717 words

Chapter 43 - FURUCINA NE HAUSA NOVELS BY AISHA GALADIMA.txt

29 Oct 2025

636

dalilin yi mata rapping a tunanin na Agrif zai hakura da ita yabar ta ne sai kuma cikin yaran nan ya shiga Allah yagani ban soba amma na dauka na yarda nayi babban kuskure ki yanke min ko wane irin hukunci amma Mommy dan Allah ki janye kalmanki na bakya son sake ganina kar na sake dosan inda kike nasha wahala Mommy nasha ruwan da cikina ya kasa karɓan sa naci abincin da ban zaji zan cishi ba na kwanta a inda ban zaci ɗan adam yana ƙwanciya ba Mommy ki yafemin nayi kuskure ki hukunta ni zan zama bai biyayya da umarnin ki.

zama itama tayi damar a wajen ta ɗago haɓar sa murmushi tayi tace "to na baka umarnin ka kalleni....
da sauri ya ɗaga ya suba mata idanuwan sa da suka rune kalan ja tana masa murmushi shima murmushi yayi ga hawaye yana sauko masa saida yasha kalon ta yakamo hannun ta biyu
yace "Mommy dan Allah karki sake cewa na barki nasha wahala na azabtu kullum addua ta Allah ya kawo min wannan rana da zaki janye kalman na baƙya son gani na Mommy bani da komai bani da kowa sai ke Mommy dan Allah ki cigaba da daukana a Nasir din ki na da wanda kike so da kauna Mommy ba kwanciyar hankali da farin ciki a cikin rayuwata idan ba sanya idon ki da Albarkan ki Mommy a bin barin ciki da yasameni banyi farin ciki ba sabida banida uwar da zan runguma muyi farin cikin tare tasa kamin albarka Mommy ban san uwar da akace ita ta haifeni ba amma Mommy nasan Abbana nafi son ki akan Abbana Mommy daukar ki a matsayin uwa danayi ne yajamin nauyin bakin da narasa Nasrim ina son daukan ta tamkar wanda muka fito ciki daya amma so baya shawara baya kuma duba can canta ~SO~ hatsarine Mommy So mugune so baya adalci Mommy nayi nayi na daure masa saida ya a zabtar dani yarayu acikin jini na Mommy bansan tunani ba sai na NaNa ta bansan mafarki ba sai da ita mommy nayi kukuren rashin furtashi har na rasata a karo na farko Mommy ki bani NaNa na gyara kuskurena kar na rasa ta akaro na biyu bazan iya daukan da amatsayin ƙanwa kamar yanda nake yaudaran kaina ba a matsayin matar aure na nake son ta".

"ai ko karasa ta dan saura sati biyu auren Nasrim da Izza da Humaira".

arazane ya meƙe yace "Mommy tunda har nariga na furta bazan rasata akaro na biyu ba saide ayi duk rikicin da za ayi mommy wllh bazan yarda wani ya auri NASRIM ba Mommy ki tausaya min ni namiji ne ma buƙaci inason kasan cewa da macce sosai amma zuciyata Nana kaɗai take ƙayatamin sai Sadiyan Malam Ladan da nake ganin zan iya maneji da ita saboda ita ma tana da duk abinda nake so ajikin macce amma idan ban samu Nasrim ba itama bazan iya auren taba saboda nasan banida nusuwar da zan mata adalci nafison na fara auren Nasrim kafin Sadiya Mommy mata biyu nake sonyi mace daya bazata iya dauka na ba ".

taɓe baki Mommy tayi tace "Nasir ba kunya ba rufi to itama sadiyar ta Abbaty ce saide ka nemi wasu kai....
katse ta yayi da cewa
"ummm Mommy za ayi rigima kenan ki sa a ran ki Nasrim da Sadiya matane ne tunda ina dake bani da damuwa mommy na ta saba bani duk abinda nake so".

Mommy tace " duk abinda kake so wanda nake da iko akai ba amma wanda bani da iko saide hakuri kacire son auren Nasrim aran ka Nasir a bune da bazai taba yuwuwa ba Nasrim bata son ka bazata taba zaman aure da kai ba takawo wanda take so HABIB ɗan gidan shugaban ƙasa ".

wani irin dariya Nasir ya kece dashi yace "Mommy idan za ki iya temakona ki temakeni idan bazaki iya ba ki samin albarka wllh a wannan karan bazan bari ba na farko ma na barine saboda Agrif dan uwana ne amma yanzu zan bawa kowa mamaki ita kuma Nasrim kwana ukku kawai zaki bani bayan an daura aure sai ki tambayeta idan tace bata sona na miki alkawarin sakin ta ".


"Nasir ni kuma ban baka daman neman auren Nasrim ba saboda wasu dalilai amma ada tana budurwa nafi kowa son hakan yanzu ka makara Nasir idan kaje three brother kayi FURUCIN kana son Nasrim bazan yafi maka ba".

a wani irin tsorace yake binta da kallo a hankali ya meƙe tsaye yana dafa setin zuciyar sa "Mommy da gaske kike serious baki yafemin na auri Nasrim ba ".

gyada masa kai tayi
cikin wani irin amon rauni wanda bata dama tsammannin nasir a izzar sa yana dashima yace "Mommy koda hakan zai zama sanadinyar da ƙushewar rayuwata ne zaki rasani Mommy NASRIM ce farin ciki na".

"Nasir ka koyi samu da rashi kayi hankali ba komai mutum yake so zanyi ko yake samu ba idan ka rasa Nasrim bazaka rasa wata ba kabarwa Allah kaji".

karasa me ƙewar yayi yace "MOMMY na bari ne saboda umarnin ki ita ma Sadiya na barwa Abbaty ita zanjira naka abin da ALLAH zanyi dani".
ya ƙarashe maganan yana sake danƙe setin zuciyar sa kamar zai fisgoshi






*masoya mu hadu a pg 31 danjin yanda zata kaya shi burin Nasir na ya maida Nasrrim garkuwar tada sha'awar sa zai cika ita Nasrim zata yarda da auren sa*



*Batul Jattko*
[4/8, 1:49 PM] Batul Adam Jattako: *FURUCINA NE*
( _rikicin babban gida_ )





*NA*





*BATUL ADAM JATTKO*





*31*

Mommy ma meƙewar tayi ta reƙe hannun sa tace" ina zuwa".?

"Mommy gidana".
yayi maganan cikin shagwaɓan sa irin wanda ya sabayi mata
juyo dashi tayi suna fuskan tan juna tace Nasir bakayi missing dina ba in da dane sai mun kusa kwana muna fira duk da bamu taba jimawa bamu hadu ba kamar na wannan karan shekara guda bamuga juna ba ba waya".

"Mommy kafin ki tafi zan dawo inason na dan hutane".
girgiza masa kai tayi
tace"Nasir yanzu zamu tafi gida yanzu haka Aliyu ya gama duk wani shirin tafiyar mu a yau zamu tafi idan akwai abinda zaka dauka agidan naka ƙafata ƙafar ka muje ka dauka mu wuce airport".
"Mommy zan iya binku zuwa next week dan Allah ina da uzuri"?.
girgiza kai tayi
tace " Nasir tare dakai zan tafi inason ganin Mama Emaka kuma Baba ya kafe wai sai da kai zamu tafi inason neman gafaran Mama."

Mommy tana shiga falon gidan
Nasir tacikaro da hotunan su wani tabkeke na ita dashi ta zubawa ido ya dafa kafaɗan ta duk suna murmushi baza ta man taba ran birthday din Zeenat ne saina shida su Fayya ya rungumo Fayyat da Khaldum a gefe da gefen sa sai Khaflan da ya lanƙayo wuyan sa ta baya duk kansu dariya suke kamar ka ƙirasu su amsa ƙarasawa tayi wajen ta shafa fuskan Khaldum da Fayyat afilin tace "Allah yajikan ku".
tana ɗaga kanta taci karo da tafkeken pic din Mama Emaka da shiganta na Igbo tana tsaye a haraban coci farinta yananan sai de ta tsufa sosai
agefen nata na Hajjane ta hakince a tsaƙiyar Parlour ta cikin tum'tum sai wani hoton family har su abu da su Muwadda Izza da Humaira da Nasrim ne kawai babu a ciki sai Aiban da tana tunanin alokacin yarasu dan ga Aiban Ƙarami a ciyar Agrif
da sauri ta juya zata tambayeshi ina yasamu pic din Emaka taga ya haura sama zama tayi acikin kujera tana bin hotunan da kallo harda wanda sukayi da Baba Nasuru sunyi kyau dagani a india ne inda yake kai shi ganin doctor
ta shagala da kallon hofunan ya futo tana son tambayar sa in da ya samu hoton Mama Emaka da kuma yanda akayi ya musu hoto ba da sanin suba dan su adaukan su Nasir baya hoto amma taga yawani sha kunu ba wasa taɓe baki tayi ta meƙe
tace "muje Aliyu na jiran mu".

haka de Mommy ta sako Nasir agaba har nigeria nasir acikin girji ƙin kula Aliyu yayi nunawa ma yayi bai san dashi ba Mommy da Aliyu suna hada ido zasuyi murmushi suna mamakin fushin Nasir kamar bashi yayi lefiba daga ƙarshema fito da laptop din sa yayi yafara aiki Mommy ko jakar ta ta zuge ta dauko Qura'anin ta tafara karantawa

Motoci ne sukaje taryansu airport dare da bodyguard sai faman fuɗawa Nasir ake shiko cikin Izzar sa yake takawa idan kagan shi zakace baƙin cikin zuwan yake nan ko farin cikine fal aransa ayau zayyi arba da Nasrim Khafalan Abdul da su Ummda drive yanayin parking scurity sukayi kan motan da Nasir yake bude masa sukayi Nasir ajiyan zuciya ya sauke yana ƙarewa haraban gidan nasu kallo shekara guda rabon sa da gidan uban sa shikenan yanzu yadawo cikin ta gyara zaman black glass din sa yayi yana dan sakin fuskan sa hango Baba Yakubu dayayi yana ta zuba masa kirari ahankali yafito da ƙafarsa ya fito yana dan sakin murmushi Baba yakubu yace " garo da garo sai rabo duk wani babba sai Babba wanda yagaji bai saba ba ai ai'kin da wuyar sabawa sai ɗan gado arziƙi jini yake bi NASARA KO GANI KAFI MUTUM NASARA MAI WUYAR FADANCI GOSHIN JIRGI MAI WUYAR KARAU
SAI DAN GADO".

Nasir bin ma ai'katan yayi yana basu hannu suna nuƙewa amma yana sake matsawa cikin sakin fuska yake amsa gaisuwar su daga ƙarshe ya rungumo Baba Yakubu yana tsakar masa murmushi yade kasa magana har Mommy ta shige parlurn Hajja shima sakin Baba yakubu yayi ya dauru bayan Mommy
Hajja rungumo Nasir tayi ta saki kuka tace "oo ni Maryama Nasuru kaine farin cikin gidan nan me yasa ka gujemu". zamewa ajikin ta yayi yana lalashin ta
ya zube agaban Abu da Daddy yace "Daddy Abu.......
sai kuma muryar sa ta fara rawa yakasa ƙarasa maganan kawai ya kifa kansa a ciyoyin ABU yana sauƙe numfashi shafa kansa Abu yayi yace "please my son karkayi kuka kai jarumine jarumai basa saurin kuka musamman cikin yaran su"
yaƙarashe maganan cikin tsigar wasa".

"Abu kugafar tamin kaida Daddy wllh ban wulaƙan taku da son raina ba saide kawai dan banason kuce zaku tursasani zuwa gida ne wanda nasan hakan halakane a gareni dan zan sabawa umarnin Mommy na Daddy ku yafemin duk lefukana Daddy na san na ɓa ƙanta maka nayi Repping din ƴarka aranan auren ta Abu na ɓa tawa ɗan ka AGRIF dare mai mushimmanci nayi sanadiyar jefa ka cikin rashin lafiya Abu idan baku yafemin ba Allah bazai yafemin ba kunje ne mana na wulaƙanta ku na nuna ban san kuba nacuci ahali ........

da sauri Abu ya girgiza masa kai tare da sa hannun sa na dama yatoshe masa baki Daddy saukowa yayi akan kujeran ya ja Nasir jikin sa
yace" my Son mu mun yafe maka dama ba kaine mai lefin ba an hukunta masu lefin..........


"Daddy nima mai lefine na rasa me yasa nayiwa ƴan uwana da banida kamarsu NASRIM da AGRIF haka yasaki kukan da yake dannewa tun shigowar sa gidan Khaflan da Abdul ne sukazo suka faɗa jikin sa suna murnan ga papa wayyo ga papa


hannu biyu yasa ya rungumesu yana tambayar su ina su Muwadda sukaje
su kace uncle yaje daukosu a gidan gyaran gashi Izza da Humaira cikin ladabi suka zo suka gaida shi haka Fajji ƴar gidan Mala yayan Mommy na maiguguri wanda zatayi kusan sa a dasu Nasrim amma budurwa ce itama cikin ɗoki tace "my brother ga sister dinka da baka santa ba."

Nasir kallon ɗaya yamata yagane eh family su ce dan ga kamanan da Mommy har farin ta farace tas kamar Mommy amma dayake ita yar zamanice ta hada da mai tazama kamar zabiyan gyaɗa kansa Nasir yayi yana son yace ƴar wajen waye amma miskilancin sa ya hana
kawar da kansa yayi yafara magana da su Musanat da suka shigo yanzu da gudu suna rige riken faɗa fasa ya kamo hannun Musanat
yace "my daughter kin girma me kike cine murmushi yarinyar tayi tace "papa bakomai....

Ummda tace " wllh papa musanat cine da ita komai ci takeyi sunan tafa ci TARA Allah har yafi so 9 ma takeyi".
murmushi Nasir yayi yana kallon tsantsar kaman Ummda da Aiban hatta maganan su iri dayane jayo yarinyar yayi yana shafa kanta
yace " daughter ai kwara tayi ci taran bakiga tafi Muwadda ba".
ya ƙarashe maganan yana kai hannun sa wuyan Musanat
Musanat tace "Allah Papa ka hana su cemin ci tara".

yace " daughter barsu su fada ai ci lafiya ne wani a gadon asbiti yake sai de ayi ta saka masa ruwa kinga keko kina da cikekken lafiya yanzu koda Boss zaki iya karawa."
ya ƙarashe maganan yana sauƙe idon sa akan Khaflan wani kallon raini Khaflan ya watsawa Musanat amma bayyi magana ba
Hajja tace ina Aisha ina wannan wanda akayiwa rowan imani".

Nasir yace "har yanzu bai dena dukan suba Son kadena sune fa manya yayun ka ne Ummda ce kawai ƙanwarka".

Khaflan yace "ni ina ruwana dasu".
yayi maganan yana rungumo Mommy yace welcome my Mom nayi missing naki thank kinzomin da papa na,"
tureshi Mommy tayi tana meƙewa
tace "dallah ɗagani ni naje nawatsa ruwa sai yanzu ka ganni".

Hajja tace "dama ko ƴan maiduguri sunzo suna can part dinki".
cikin murna tace "har sun ƙaraso gobe sai lagos kenan".

ta ƙarashe maganan tana me ƙewa ta kwashi tarkacen ta tafice

Nasir sauƙe numfashi yayi yace "Daddy Mama Emaka fa ta mutu na kasa gayawa Mommy yanzu idan munje ya zamuyi'".

Hajja da su Abu sun jajanta mutuwar Emaka saboda Mommy ta kwallafa rai akan tanason ganin mahaifiyar ta
Hajja tace " tun yaushe tarasu ".?

Nasir yace "zatayi shekata goma da rasuwa ayanda ƴan uwanta suke gayamin".

Mommy taji daɗin ganin su Baba danginta dayawa suka zo Mala Sharif da sauran su

Humaira da gudu ta faɗa jikin Nasrim tana murmushi tace
" He loves me and I love him very much wllh bayan Khamal ban zaci zan fada soyayya haka ba Zarran yacika namiji wow wllh yafi ya Kamal iya soyayya kodan damafa Kamal haɗin gidane".

tureta Nasrim tayi tace"
Lallle Humaira ko kunyar idona baza kiji ba ki fito a hannun dan uwana ki zauna agabana kina ambaton kina son wani".

Humaira tayi murmushi tace "koke da kukayi soyayya da Agrif kamar zaku cinye juna naga yanzu kin bawa Habib dama.

"cikin sauyin yanayi Nasrim tace "ya zanyi Aisha a take taken su Abu tabbas idan ban fitar da miji ba wllh zasu min dolle da wanda ban sani ba amma wllh habib baya cikin jerin mazajen da nayiwa kaina buri kuma ma nifa soyayya da aure ahalin yanzu basune agabana ba du du du shikara daya da rabi da mutuwar mijina awani matsa sai na fitar da miji akan me".

Humaira tace "pls sis wllh ganin mu duk kan mu ukku a zaune a gidane ya janyo hakan yanzu ba ga Izza ba shekaran Aiban biyar da rasuwa ai basu matsa mata ba saida mu muka ƙaru yawan mune yakawo hakan kuma idon mutanen duniya akan mu yake saboda wannan abubuwan da ya faru especially make amma kinsan wani magana danaji ɗazu a falon Hajja wai an baida kudin auren ki dana Izza ke da izza an muku miji baza abawa Habib kema itama Izza baza a bawa Zayyat ba an fasa saboda wasu matsaloli da suka ɓullu wai abin yaban mamaki to suwaye mazajen naku kuma fa shirye shiryen biki ake daga anzo daga lagos za a daura aure".

Nasrim tace "ban gane ba anayiwa bazawara auren dole ne kuma yama za ayi a ce an bai da kudin auren mu mu ba muji ba".

Humaira tace "kude zuba ido tunda bamu san manufar hakan".

duk gidan kowa yace sai yaje lagos har Hajja da take kushe arna dayake safgar yawone tana wajen ga gaiyar yan maidukuri awani ɗan ƙaramin jiri nasu na family maicin mutum 34 suka shirya tafiyan gasu suda yaran su har ƴan maiduguri su arba'in da ɗaya ne dan haka yaran yawanci a cinyar mutane suka zauna

Nasrim itace kusan ta ƙarshen shigowa dan haka tana shigowa saura seat din mutum biyu kuma ajere dan haka adayan da zauna bayan ta Bukar ne ɗan gidan yayar mommy da matar sa sai daga gaban ta izza da Fajji

tana shirin gyara zaman ta kawai sai taga mutum yana shirin zama a gefen ta cikin ɓacin rai ta fara kalle kalle amma ina ba wani seat sai ƙwaya biyun zama tayi tana daure fuska shiko ko kallon ida take bayyi ba ya zauna cikin izzar sa
Nasrim zama tayi tacigaba da wayan da take ƙamshin turaren sa yana tariyo mata wani abu jitayi gabanta yafadi domin bazata taba banta wannan ƙamshin ba a take taji wani irin ɓacin rai ya ziyar ceta amma ta daure tacigaba da waya da Habib har jirgi yatashi Nasrim tajima tana waya tunkun taji networks ya ɗan dauke bata jinsa sauƙe wayan tayi tana murmushi Fajji da take gaban su tajuyo tace "kai sister irin wannan dogon wayan haka ba sararawa kewai baƙya gajiya dawaya ne baki da wani lokacin sai na wannan koɗaɗɗen meyasa ba kya gajiya .?'
murmushi Nasrim tayi tace "
because my souls and spirit boid with his blood".

zaro ido Fajji tayi tace "rushin ki da jinin jikin ki hade yake da nasa lalle kam ba gajiya cigaba yar uwa

Murmushi Nasir yayi ya kwantar da kansa sosai ajikin seat din yakai bakin sa setin kunnnen Nasrim idon sa alumshe ahankali yanda ba meji sai ita
yace" most of the time whats ours heart desired may not happened
So tari abinda zuciyo yin mu keso bashi yake tabbata ba

wani irin mugun kallon ta watsa masa amma ina ido sa alumshe kamar ma bashi yayi maganan ba

wayan tane yasake rin Habib dinne kuwa dauka tayi tare da gyara zaman earpieces din ta tacigaba da sauraron zaƙaƙan kalaman Habbib

a lagos Mommy tasha kuka jin Maman ta tarasu sai ƴan uwanta wanda yanzu Nasir ya gama wadata su dayawa daga cikin matasan yabasu aikin yi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login