Showing 66001 words to 69000 words out of 130248 words

Chapter 23 - Sirrin mu Complete by Nimcyluv.txt

25 Nov 2024

5972

a very nice name" kasa magana tayi sai kuma tace "to idan kuma ban iya soyayyar ba fa? Shkknan ni baza ka soni ba?" Mmkin shirmanta yake ta kasa fahimtar komai yace "Am not sure seriously, amma ki zama mace mai ƙarfin gwiwa, mai jajircewa akan da take so ki samawa kanki jarumta hqr salama,babban abu kuma ki gayawa Allah damuwarki idan abun ya kasance alkairi a gareki sai kiga komai ya sauya babu abinda lokaci baya sauyashi" kai ta jinjina masa yace "tashi kije" kwaɓe fuska tayi tace "Nifa tsoro ake ban wlh" idanunsa akan wani wajan yace "Uhm" lura tayi ya fara gajiya da mgnar akwai abinda ke damunsa sbd yadda yake ta riƙe ƙirjinsa tace "Eh wlh tsoro na keji kawai na kwana a nan" bai kulata ba ya kama kanta sosai ya shiga karanta mata addu'a kana ya ɗura laɓɓansa a goshinta nan ma ya karanta mata addu'a tare da sauke mata wata lafiyayyiyar sumbata a wajan yace "Jeki nothing happen in sha ALLAH" miƙewa tayi tana jin kamar idan ta tafi wani abu zai samesa a dolenta ta miƙe tsaye ta nufi wajan ƙofa harta buɗe zata fita taji yace "Zahraaah" da sauri ta juya taga ya ware mata hannayensa da sassarfa ta nufi wajansa suka rungome juna, Sheikh riƙeta yay sosai lokacin tuni jikinsa ya gama ɗaukan zafi cikin Muryar mara lfy yace.
_لا شك أن حبك في قلبي كمثل نفس الذي يخرج من أنفي،_
_الذي كان إدفاعة كان أن يكون كالموت_
_إذا كان كذالك كيف تري أخرجه في قلبي،_
_إلي أحبك ياصاحبة الحسن والنسب.💘💘_
Kallonsa tayi tace "me kace?" Girgiza kai yay yace "basai kinji ba Allah yay maki albarka jeki kwanta" juyawa tayi bisa uamarninsa tana tafe tana waigensa harta fice daga cikin bedroom ɗin, tana fita sauke ajjiyar zuciya "nayi amfani da harshen da bakya ji nace _Haƙiƙa sonki acikin zuciyata tamakar numfashin da yake fita daga hancina wanda tsayar da shi dai-dai yake da mutuwa_" baya yaja ya kwanta amma tarin da yazo masa yace sam bai isa ya kwanta ba cikin fitar hayyaci ya fara tari wanda daman tun ɗazo yake riƙesa, yana tsaka da tarin yaji wani wani ƙaton jini yay tsaruwa daga cikin bakinsa, fitar jinin yasa ya samu relief, sanyin ɗaya keji yasa yaja duvet ya rufe jikinsa. Can cikin dare yaji ana turo ƙofarsa ko mutsi bai ba bai kuma san mai shigowar ba, yaji dai ana buɗe inda yake ajjiye muhimman abubuwa, can kuma yaji ƙarar papers not too long akai waje da ɗan sassarfa, numfashi kawai ya sauke abinda ya keji bazai taɓa barinsa ya buɗe ido ba,idan yaga ko waye ta ina zai iya kamasa shi ba ƙafa garesa ba. Washe gari Sheikh da azumi ya tashi sbd Alhamis ce, gefen Fannah ma da nata azumin ta tashi, Barrister na zaune a cikin bedroom ɗinsa yana duba ayyukansa yaji an buɗe ƙofar an shigo, Mami ce sanye da wata Holand ɗin atamfa mai kyau tayi fess da ita sai zabga ƙamshi take, fuskarta ɗauke da Murmushi tace "Mrng dear" with much surprise ya kalleta kafin yace "Mrng" zama tayi tace "Yau ba zaka fita bane?" Kai ya ɗaga mata yana faɗin "Am not sure dai,amma jikin Son na bani tsoro yaƙi yarda a kaisa asibiti,ga kurar da yaywa Arjun da kuka Arjun yabar gidan nan,so ina jiran Uncle ɗinsa yazo" jinjina kai tayi tace "Daman fita biki ya kamani shi ne nace i can't anywhere without your permission" miƙewa yay tsaye yace "Oh really?" Tana tashi tsaye zuwa wajansa tace "Sure! I'm sorry Barrister _for the past Weird experiences with are all regretful._" yana duba wayarsa yace "What the you want" kai tsaye tace "Your permission allow to go" yace "where?" Matsuwa wajansa ta sakewa zata riƙesa yace "Ohhh Hello, don't trying it" baya taja tana fidda wani kalar murmushi tace "Zani Sakoto ne" waje yay yace "ok" da ido ta bisa tana jan wani lalataccen tsaki "You're mad Barrister Hamdan Balarabe". Sheikh ko Company ban je ba sai yanzu daya fita zuwa Mosque sallar asar ya daɗe zaune yana yiwa Mutane karatun bulugur mara, sai wajan 5 yaja Wheelchair sa ya dawo, a Parlo ya samu Granny tana faɗin "To duk basai suci kansu ba,ina dalili fisabilillahi? To wlh babu abinda yaymin zafi ni ba gantalalliya bace yanzu zan haɗa kaya na, na tafi inda Allah ya kaini" Uncle Sham yace "ba takai ga haka ba,tunda yaƙi faɗin abinda yake damunsa sai a rabu dashi ai asirin ciki sai hanji" share ƙwalla ta fara tace "In dai da halarci baici Imamu yaymin haka ba, yaro abun tausayi rayuwarsa duk a gantale,ban sani wa yake dashi? To sai wannan yarinyar mai taimako na" Uncle Sham kallon fannah yay wacce take sanye da wata light blue ɗin laffaya wacce tai mata kyau sosai,tana tsaye wajan dinning area tana shirya dinner "Ah to babu ruwana idan hawan jini na ya tashi idan na mutu wana macewa wane yake da asara?" Shi dai Sheikh na zaune idanunsa rufe yana jin dukkan abinda Granny take faɗa "ɗauko min Mantina nasha ko zanji dai-dai" jiki a sanyaye Fannah ta nufi fridge ta ɗauko mata tana zuwa dai-dai inda yake zaune suka sauke ajjiyar zcy a tare slowly kuma ya buɗe idanunsa wanda ya samu sauka a cikin nasa, jikinta ne ya ɗauki rawa ƙafafuwanta suka ƙasa ɗaukan jikinta gaba ɗaya tayi kansa zata faɗi da sauri ya rufe idanunsa yana tura Wheelchair baya, Granny ta riƙeta tana faɗin "Ya! Ya! Ya! Haka kamar wata mai shafar aljanu, Auzubillahi sharrr walaƙuuwata!" Ta faɗa tana riƙeta girgiza kai kawai Uncle Sham yay yana tura Wheelchair Sheikh yace "Mohd jeka gobe kazo i want talk to you" miƙewa Arjun yay yace "In sha Allah Uncle" Granny tace "Ranjun kaga gida ya kusa zama na Maraya ko? Yooo idan na mace Imamu kaɗai yay asara amma dai in sha Allah mutuwa ba yanzu" murmushi kawai yay mata yace "We hope so.." Uncle Sham yace "Imam bazan takuraka aka ka faɗa min abinda ke damunka ba,Amma ka sani damuwa bata mganin komai, kasan komai tunda kana da ilimi amma ina gargaɗinka kasan me kake Fatima matar Ubanka ce" calmly yay yace "bana nufin wani abu amma ka iya takunka da ita za'a iya haɗa baki da ita a cutar dakai" sai lokacin ya ɗaga idonsa ya kalli Uncle Sham yace " i want freshen up" Uncle Sham yace "ok bari na turo maka Granny, ka tabbatar kaci abinci mai yawa tunda azumi kayi" bai ƙara kallon Uncle Sham ba sai ma idanunsa da yaja ya rufe yasan har abada Zahraaah ba zata taɓa cutar da rayuwarsa. Bayan Isshā Barrister na zaune a parlon sama yana waya da Alhj Kamal yace "Na kasa gane maganganun ka, nayi searching harna gani dan Allah ka fahimtar dani" Murmushi Alhj Kamal yay yace "Na daɗe da danin baka da ƙwaƙwalwa Hamdan let's go to the point a cikin yaranka guda Uku, ka kwana da sanin cewa guda biyu bakai ka haifesu ba, i mean bakai ne real father ɗinsu ba...








Allahamdulillah end of book 1🌚🌝.


Dan Allah dan Annabi Anty ki daina karanta littafina ba tare da kinbiya ba kiji tsoran Allah,ki sani ina da haƙƙi a kanki bazan maki Allah ya isa ba,amma kisan haƙƙin wani akan wani Ubangiji baya taɓa yafesa.




SIRRIN MU isn't free book..if you read for free..🤷🏻‍♀️🤷🏻‍♀️.


It's 500 via 0116886423 sulaiman Naima s union bank. Show your evedance via WhatsApp 08119237616








NIMCYLUV
22/10/2021, 10:31 - 🤔🤔: 51-52
[9/22, 6:46 PM] Nimcyluv✍🏾: Da rashin fahimta Barrister yace "What the you mean by that Alhj Kamal?" Wani Murmushin gefen baki Alhj Kamal ya sauke wanda ta cikin wayar Barrister yaji sautin fitarsa yace "I mean my words Barrister, acikin yaranka guda Uku biyu ba kai ne real father ɗinsu, wlh bakai ne Ubansu na gsky ba" wata zufa Barrister ya share yana son ya tuna abu amma sam ƙwaƙwalwarsa ta gaza ɗaukan komai, cikin ƙarfin hali yace "Am on mah way Alhj Kamal" zaro ido Alhj Kamal yay yace "Aini ka ganni gaf da shiga jirgi bana jin zan dawo Nigeria sai nan da 3yra to above" ƙitt Barrister ya kashe wayar ba tsaya ya gama jin zan can ba. Zagaye ya shigayi a parlo'n zcyarsa cike da tunani kala² daban², yaransa har guda uku wanda yake alfahari dasu ace guda biyu bashi ne ya haifesa ba, kenan guda ɗaya ne nasa to idan haka ne tsakanin Sheikh,Fareeq, Bahaiyya wanne ɗan sa? Da ƙarfi yace "Impossible, wlh babu wanda zaiji Wannan zan can, koda Alhj Kamal ɗin ne yace zai faɗa Tabbas zai iya ganin bayansa akan wannan muhimmin abun ya fita cikin mutane, yasan Alhj Kamal sarai tunda ya faɗi wannan maganar da gske haka ne babu ko tantama, dan haka dole ya nemi wata mafitar, dole ya samu wata sabuwar zuri'ar daga wajan Fatimansa ya shirya komai, dan haka ba a haifi wanda zai ruguza masa plans ɗinsa wanda ya tasu dashi ba, a gobe ko suma Fannah zatai sai ya kasance da ita" Yana zaune sanye da nightwear Pajamas Kimono Smooth Comfy Soft Bathrobe, a dalilinsa na son ɗauke damuwar dake ransa yasa tun safe Arjun ya kawo masa system, hanunsa saman system ɗin yana operating ɗinta, skin ɗinsa tai fresh sai Shinny take fuskarsa mai cike da haiba da kwarjini ta faɗa kaɗan idanunsa ya ƙara shigewa ciki, sai ya ƙarayin kyau fiye da lokotan baya. Yanayin yadda gabansa ya faɗi da zcyarta data buga yasan cewa Zuciyoyinsu sun yi kusa da juna, a hankali kuma ƙamshin turarenta ya fara kawowa hancinsa ziyara, ko ɗan baiyi ƙoƙarin ɗago kansa ba sai ma ƙara himma da yayi wajan latsa system sai ka ɗauka tun asali ya iyata. A hankali take kata ƙafafuwanta da sukai mata wani nauyi at the same time kuma itama taji zcyarta ta buga har sai data runtse idanunta, tana sanye cikin wata nightgown Amazon ta ɗura hijab a jikinta, ta rame itama sbd rashin ishasshan abinci a cikinta, har inda yake ta ƙarasa cike da nutsuwa ta ajjiye masa tray ɗin dinner mai ɗauke da Ingredient Shrimp Stir Fry, chicken and vegetables stir- fry, sai coffee da kunun gyaɗa, shiru ne ya biyo baya kuma ta kasa tashi a wajan sai ma zamewa da tayi ta zauna ƙasan ƙafafuwansa, few seconds ya ɗaga jajayen idanunsa ya sauke a kanta kamar wanda bai son magana yace "Have you eaten?" Shiru tai masa idan har gsky zata faɗa to rabunta da abinci tun jiya,dan ko datai azumi batai wani shur ba, a hankali ya sauke numfashi tare da ajjiye system ɗin can gefe guda, zamuwa yay tare da zama a inda take zaune kallon yadda tai wani zururu yay fuska ya haɗe sosai kafin ya sanya tattausan hannunsa a saman fuskarta ya tallafo haɓarta yace "What Is this?" Kwaɓe fuska tayi tare da sauke ƙwayar idanunta ƙasa tace "Me nayi to?" Ta faɗa a shagwaɓe, tsayawa kawai yay yana Kallonta yadda take abu kamar yarinyar goye, sakinta yay yaja baya kaɗan yace "Ci abinci" marai-raice masa tayi tace "To ai kaima ba kaci ba" ba tare daya kalleta ba yace "Uhm" banda tasan idan hawayenta ya zuba tamkar ta rusa al'ƙawarin da tai masa da babu abinda zai hana tai kuka kota samu yaci abinci, idanunsa a lumshe ya lulaa duniyar tunani yana jin sanda ta buɗe warmers ɗin ta shiga zuba masa abincin a plate, bai ji zuwanta ba sai jinta yay gaba ɗaya a kusan rabin jikinsa ta riƙe fuskarsa da kyau, da ɗan sauri ya buɗe ita kana ya buɗe baki da niyar faɗin "Move" sai kawai yaji ta tura masa laumar abinci ba kinsa, rufe idanunsa yay sosai sbd ɗacin da abincin yay masa a baki ya kasa kota taunasa, cikin ƙasa da mai ɗauke da lallashi tace "Babu ruwan ciki da damuwa, yanzu zai haifar maka da wata cutar ta daban, ita na rasaka ka sani rayuwan Zahraaanka na cikin wani hali, babu abinda nake buƙata a yanzu sama dakai Malamina, please kaci sabo da soyayyar da nake maka,ban shirya rasa Malamina farin cikin zcyta ba" ba tare daya kalleta ba ya fara tauna naman data saka masa a hankali cike da nutsuwa da ƙyar ta samu ya taune naman ya tafi, tana ganin haka ta ƙara ɗebuwa still idanunsa a rufe ta buɗe madaidaicin bakinsa ta saka masa, taunawar farko yay saurin dafe ƙirjinsa yana shirin fito da naman daga bakinsa ta saurin sanya nata baki naman ya faɗa ciki, da ɗan sauri ya janye bakinsa, Fannah kam kasa hqr tayi tasan da gaske duk su biyun suna buƙatar taimako amma a yanzu yafi buƙatar taimako fiye da ita, a sanyaye ta lallausan hannunta ta shiga murza masa ƙirjin haɗe da shafa bayansa, cak tarin ya tsaya sai numfashi da yake saukewa, cikin rawar murya yace "Leave Zahraaah" girgiza kai tayi tace "Why?, Kana buƙatar taimakona Malamina! A shirye nake da baka koda rayuwata ce" ta ƙare maganar tana ɗura masa mug ɗin kunun gyaɗar a baki, sha ya farayi a hankali² harya sha fiye da rabi while Hannunta na bayansa, Sheikh ji yake kamar tana zuba masa wuta a jikinsa haka ya keji dauriya kawai yake ya tsani kusancin da suke samun kansu a kullum,zcy sam ba tai masu halarci ba hanunsa yasa ya riƙe nata kana ya buɗe idanunsa tare da Kallonta, matsuwa jikinta ya fara a hankali ita kuma tana zaune kamar statue sbd buguh da ƙirjinta ke mata ya hanta ko ƙwaƙƙwaran mutsi ne, fuskarsa ya kifa a shoulder nata ya fara sakin ajjiyar zcy yana jan numfashi, a hankali kuma yasa hanunsa a bakinsa tare da tufar da yawo,mai makon yaga yawon kamar yadda yay expected sai yaga wani gudun jini a tsakiyar farin hannun nasa, wani murmushi takaice kawai yay ya ɗauki handkerchief ya goge jinin dake hanunsa kana fesar da iska daga cikin bakinsa kafin ya sauke numfashi yace "Don't leave me alone Zahraaah!" Bakinta na rawa tace " I won't, always be your side forever and ever you're the only one i pray for" hanunsa yasa ya rungome ta sosai a hankali yaji idanunsa na lumshewa wa cikin ƙaramin lokaci taji Numfashinsa na fita da zafi, Cikin rawar jiki tasa hannunta a kwantacciyar sumar kansa tace "Malamina... Sheikh na Are you okey!?" Gaba ɗaya nauyinsa ya sauke mata, da ƙyar ta zamesa a jikinta taga ashe bacci ya ɗauke sa, wata ƙwallar tausayinsa ta kawo idanunta da sauri ta goge Idanunta ta raɓa kusa dashi a ƙasan carpet ɗin ta kwanta ta daɗe tana kallonsa kafin bacci ya ɗauke ta a kusa dashi numfashinsu na haɗewa. Misalin ƙarfe 1 na dare Mami zaune ita da ƙawart Kubra suna jira layi yazo kansu, wannan shi ne first time da Mami ta ziyarci wajan boka,domin ta aminta da shawarar ƙawarta suna ta zaune har wajan 1:30 sannan layi yazo kansu Kubra a gama Mami biye da ita a baya sbd tsoran daya shige ta, a zaune suka samu wani ƙaton baƙin Mutum mara fasali da kayan asiri birjik a gabansa, yana ganin su ya fasa dry yace "Sannunku da zuwa gantalallu wanda suka yarda da shirka fiye dasu roƙi Ubangijinsu" kallon juna sukai ita da Kubra kafin su nemi waje su zauna, Kubra ce ta buɗe baki zatai mgn yace "To muguwa mai mugun nufi, taki bata fissheki ba sai ta salammiyya ƙawarki,maza duba nan" ya faɗa yana dukan ƙwaryar dake gabansa, zare ido Mami tayi haɗe da dafe ƙirjinta sbd ganin Sheikh da tayi kwance a ƙasan carpet gefensa kuma fannah ce ta zagaye hannayenta a wuyansa suna bacci cike da nutsuwa, tashin hankali ƙarara ya bai yana saman fuskar Mami jikinta na rawa tace "Na shiga uku ni Saudat me nake Shirin gani, Imam da matar Ubansa,wlh sai naga ƙarshen ki munafukai" dry bokan ya ƙyalƙyal kana ya haɗe fuska yace "Gana almura mai baƙar aniyya abinda kike ƙwaɗayi itama take ƙwaɗayi" cikin Kuka Mami tace "Ka taimakamin ka raba tsakanin wannan mutanan, wlh zcyta ba zata sami sassauci Ba indai ban mallaki Sheikh ba" Dry ya kumayi wannan karan har wani hayaƙi ke fita daga cikin bakinsa yace "Rabuwar su na nufin faruwar wasu sabbin alamura,haka haɗuwar su na nufin sabon abu, ko wanne da muhimmanci sa" kai tsaye tace "A'a ban damu da dukkan abinda zai faru ba,kawai ka rabasu dukkan abinda kake so zan maka" yana zana abu yace "Kaga kinibau, a fuska Musa a baki fir'auna" shiru gaba ɗaya sukai kafin yana numfashi yace "Akwai hatsari a aikin duba da yadda suke matuƙar so da ƙaunar junansu, sannan duk abinda za'ai bana jin aikin zai tasiri jikin namiji,ko aljani bai isa ya cutar da shi bare mutum" Kubra tace "Kawai kayi Abinda Ya dace kayi ka rabasu" jinjina kai yay yace "Kun aminci da dukkan sharaɗin dana faɗa?" Da sauri Mami tace "Shegiya mai baƙar aniyya, ai dole ki aminci sbd mugun nufinki na gab da cika" Mami tace "I mean my words ko akan yarinyar ne kayi aikinka burina kawai su rabu na mallaki Sheikh Mallaka ta har abada" kai tsaye bokan yace "Duk abinda kike so za ki samu, amma bazan taɓa gaya maki sharaɗin ba sai bayan na gama aikin, sannan duk abinda nace kiyi ya zama dole tunda kin manta lahira kinzo neman duniya" ba tare da shakka ko tunanin komai ba tace "Na amince" "Uhm ta yaro kyau take bata ƙarko" tashi yay ya nufi wani ɗaki ya daɗe ciki kafin ya fito ɗauke da wasu garin maganin yace "Amshi wannan, ki zubawa ita yarinyar a abinci" wani ya ɗauka ya bata yace "Wannan kuma sanda zaki kwanta dashi tsarkakakken yaron saiki saka a cikin jikinki yana kwanciya dakai zaiji baya ƙaunar ko wacce mace saike duk abinda kikace jiki na rawa zai aikata" karɓa tayi tace "To ka gano rabon yara a tare dani dashi?" Dry yay yace "Yara dai? Tabbas akwai rabon yara masu matuƙar yawa da kuma kyau uwa uba addini, sai dai ban san a ina ya samu rabon ba domin yaran a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login